← Book details A Zato Na Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 21 OF 95

Sashe 21

A Zato Na Complete Hausa Novel · about 8 min read

Na kare mishi kallo, duk da kokarin dannewa da nake yi, da nuna kamar ban damu ba, amma nayi kewar shi. Kwana daya da yini daya kacal, amma nayi kewarshi.
Na kalli Jan data tsaya tana kallonmu, nace "ki wuce abinki kawai, zan shigo in same ki". Babu musu ta shige cikin gidan ta barmu a tsaye.
Na harde hannu a kirji ina kallonshi, "me? Yanzu kuma mai kake bukata ne? Kana so mu kebe wani waje ne ko kuma ka kama mana daki ne a hotel?".

Ya dafe kai, "Subhanallah, haba Na'ilah me ya kawo wannan maganar kuma? Kuskure ne nasan dana riga na tafka shi, amma ina neman afuwarki don Allah. Wallahi ban san abinda ya hau kaina ba, ok, na sani. Gajen hakuri ne irin nawa, amma wallahi na gane kuskurena, ba zan kara ba, don Allah ki bani dama Na'ilah, na miki alkawarin hakan ba zata sake faruwa ba".
Naji zuciyata ta fara yin sanyi da jin hakan, nace "how sure are you? Ta yaya zaka tabbatar da cewa nan gaba ba zaka sake tare ni a cikin mota, trying to touch me inappropriate ba?".

Ya hau girgiza kai da sauri, "I assure you hakan ba zata sake faruwa ba, na miki alkawarin ba zan kara taba ki ba tare da izinin ki ba har auren mu!".
Nace "idan kuma hakan ya sake faruwa fa?".
Yayi shiru yana kallona, nace "magana daya ce Umar, idan abu makamancin haka ya sake faruwa, we are over! Dama kasan hakan ta taba faruwa, yazo ya sake faruwa yanzu, to babu na uku. Idan kuma muka rabu, mun rabu kenan, ka yarda?".
Ya gyada kai, "it's not as if zan sake maimaitawa, but yeah, na yarda. Fushin ki ba abu bane da zan yi marmarin sake gani ba koda wasa. Yanzu dai kin yafe min?".
Nayi jim ina tunani, na yafe mishi? Ya riga yayi convincing dina, kuma yayi alkawarin hakan ba zata kara faruwa ba, saboda haka meye aibun yafe mishi a ciki? Don haka na gyada kaina, ya saki murmushi a tausashe wanda ya sanya ni sakin murmushin nima, "oh thank God! Wallahi baki ji yadda na damu ba, God, I miss you wallahi".
Nayi murmushi kawai, yayin da naji wani sanyi yana kwaranya a cikin raina. Ban sani ba, na yafe mishi din da nayi ne, ko kuma na dawowa gareni da yayi bane. Kafin in sake daga baki inyi magana, muka ji kiran sallah, ya kalleni yana murmushi, "bari in wuce masallaci to, zan kira ki zuwa anjima".
Na gyada mishi kai tare da shigewa gida.

Bayan mun ci abincin dare a dakin Janan, ta zauna a gefen katifa suna waya da Al-Mustapha saurayinta, ni kuma na shiga whatsapp chatting. Sakon mutumin nan na dazu shine abinda na fara gani, ni na ma manta dashi.
Amsar tambayar dazu dana mishi da safe ce ya turo min, "kamar yadda na fada miki, na san ki farin sani. Kuma ina matukar kula da lamuran wadanda suke very special a gareni, don haka ba wani abin mamaki bane".

Na maida mishi da amsar 'haba? Ta yaya aka yi na zama very special a gare ka?'.
Babu jimawa sai ga reply ya shigo, 'oh, you are very very special in fact! Idan nace zan miki bayani zamu jima a haka, to cut it short, ina jin ki a cikin raina fiye da yadda kike tsammani'.
Haka kawai na tsinci kaina da darawa. Wani abu game da mutumin is very fascinating, yet so familiar. A karo na kusan biyar tunda muka fara chatting dashi yanzu, da naji a jikina duk yadda za ayi mutumin nan ya sanni fiye da sani na, kuma nima ko yaya ne na san shi. Sai dai duk hakan bai dameni ba, yadda naji hira dashi ta dauke min hankali, shine abinda ya bani mamaki ya kuma daure min kai a lokaci guda. It's a first.

Mintunanmu talatin kacal muna hira ta hanyar musayar rubutattun kalmomi, sai gani kwance rigingine a tsakiyar daki, ina kallon fankar dakin dake juyawa, waya a hannu ina ta faman rubutu, yayin da lokaci zuwa lokaci sautin dariya zai fito daga baki na, walau na sani ko ban sani ba. Hakan ya kan sa Jan, da har lokacin tana kan waya, zata juyo ta kalleni cikin alamun tambaya, amma bata tambayeni ba.

Zuwa lokacin da yayi min sallama akan wani aiki da zai tafi yayi, ba ni kaina ba, hatta zuciyata da gangar jikina naji sun aminta da mutumin. Wanda hakan a karan kanshi ma abin tambaya ne, na farko ban san mutumin ba, babu abinda na sani dangane dashi sai sunanshi, yana aiki da wani kamfani da yake sarrafa takardu, shikenan. Dana tambayeshi yana da mata? Sai yace ba ga ki nan ba? Hakan yasa naji sautin bugun zuciyata kamar zai tsaga tsakiyar kirjina zuciyar ta fito.
Tsakanina da Allah ban so muka yi sallama dashi ba, na tabbata idan zamu kwana muna chatting dashi ba zan taba damuwa ba a cikin raina, kai a takaice ma zan so hakan ba kadan ba. Muka yi musayar sai da safe, ya tafi bayan ya turo min 'sleep tight!', ya Allah, ban taba jin dadin ganin kalmomin nan daga kowa ba a rayuwata sai a yau din nan.
Yana sauka naji gabadaya chatting din ya fita daga raina, don haka nima na sauka.
Na lalubo jakata na ciro littafai daga ciki na fara karatu da bibiyar practicals din da muka yi yau.

Sai wajen karfe goma Jan ta gama tata hirar da Almunta, (yadda take kiranshi). Ta juyo ta kalleni tana murmushin tsokana, "fadan masoya hutu, wato saboda kun shirya shine kike wannan glowing?".
Nayi murmushi kafin na jefa mata harara, "ni kada ki min sharri wallahi".
Tace "wani sharri? Ga abu nan a fuskarki, kin kuwa ga yadda kike ta zuba murmushi sanda kuke chatting dinnan? Har wani dariya kike yi, irin soyayya tayi dadi dinnan!".

Na danyi frowning ina kallonta, a hankali nace "ba da Umar nayi chatting ba dazu".
Ta hangame baki cikin mamaki, "wasa kike yi ko? I mean, idan ba Umar ba, waye to? Yanzu da kika fadi haka sai na tuna Umar baya dogon chatting, wanene muka samu??". Ta karasa fada tana daga min gira cikin alamun tsokana.
Na jefeta da littafin hannuna, ta cafe tana dariya, "fada min mana!".
Na mike ina tattara kayan dana baza a wajen na maida su cikin jaka. Bandaki na fada kai tsaye na barta tana ihun, "ko shekara zaki yi a ciki sai kin fito kin fada min wanene yarinya!". Dariya kawai na saki mai sauti. Nasan kafin in fito ta manta da zancen.

Har mun kashe wutar daki bayan mun kwanta, Janan ta kira sunana, na amsa a dan gajiye da kuma barci daya fara cin idanuwana, tace "wai me ya hada ki da Umar ne da?".
Nayi sighing a hankali, "abinda ya faru ya riga ya faru Jan, mun riga mun shirya dashi, that's all that matters. Tone-tonen abinda ya riga ya faru, babu abinda zai mana, don haka ki manta da maganar".
Tace "of course sugar, baki da matsala dani".
Kaunarta naji tana kara ratsa zuciyata, fahimtarta da goyon bayanta a kullum suna kara sa inji ta can cikin zuciya da ruhina. A hankali nace "nagode Jan".
Ina jin sautin murmushin data saki cikin duhun dakin, "sai da safe Na'ilah!".
Nima na maida mata martanin murmushin duk da nasan ba lallai ta gani ba, nace "sai da safe Jan!". Na juya barin damana, tare da rufe idanuna.

Daren ranar mafarkai nayi masu yawa, da yawa daga cikinsu sun kunshi wani mutum da yake ta nanata kalmar, "ke ce Matata!," kamar waka.

-Afuwan, in shaa Allah gobe zan turo mai yawa, wannan dinma aradun Allah da kyar hannuna da idanuna suka bada hadin kai nayi typing dinsa. Thank you all.

#F.W.A

.

.

*☆⋆10⋆☆*

A gabadayan tarihin rayuwata, ban taba, ko a cikin mafarki kuwa, tunanin akwai wata rana da zata zo da zan kwanta in kuma tashi da tunanin abu daya a cikin raina ba, musamman idan abinnan ya kasance d'a namiji. Amma yau sai gani na tashi cike da tunanin wannan bawan Allah da ko sunan shi ban sani ba. Har nayi wanka, na shirya, muka karya, muka dauki hanyar asibiti, tunaninshi ne a cikin raina. Daidai da sakan daya bai bar cikin raina ba.
Muna kan hanya, text message dinshi ya shigo cikin wayata. Na zaro wayar daga cikin jaka na daga, kawai cewa yayi,
*'salam, just wanted to say hi... Ban sani ba ko kinyi tunanina tunda kika tashi, ni dai nayi. Anyway, have a nice day!.'*
Ji na nayi kamar wadda aka wa kyautar kujerar makkah. Garin bai ma gama wayewa ba, amma wannnan text din kadai made my day already.
Na shiga cikin contacts dina nayi saving number da, 'Mysterious'. Wannnan a karan kanshi abin tambaya ne ga wadanda suka sanni farin sani, domin haka kawai bana saving lambar mutane a cikin wayata, musamman wanda na sani na rana daya kacal, abu ne mai matukar wahalar yarda a wajensu.

Yau ma da wuri muka dawo gida. Yau gidan babu kowa, muka dauki makullin gidan a wajen da suka saba ajiyewa muka bude muka shiga. Bayan sallar la'asar muka shiga kicin ni da Jan, muna cikin girki sai ga Haleemo ta fado kicin din, bamu ma ji lokacin data shigo gidan ba. Ta mana sannu muka amsa, tace "don Allah wayar wa take da sauran canji a cikinku ta taimaka min inyi kira?".
Jan tace ta baro wayarta a daki, ni kuma da wayata take saman cupboard muna sauraren kida da ita, na dauka na bata. Tayi godiya ta amsa ta fita.

Janan ta kalleni bayan fitarta, "da alama kuna shiri da Haleemon nan".
Nace "tafi sauran yan uwanta kirki da rashin rawar kai shi yasa".
"uhmmm, don dai kawai ba a gabanki take yin abubuwa bane, amma kada ki bari shiru-shirunta ya kwashe ki wallahi, duk ta fisu rashin mutunci".
Na kalli kofar da tabi ta fita cike da mamaki, "amma kuma yanayinta sam bai yi kama da irin nasu ba".
Chapter 21 · 0% Book details