Sashe 40
A Zato Na Complete Hausa Novel · about 8 min read
Na rolling idanu sama tare da jefa mata baki, nace "a haka nake so ya ganni ya kuma so ni, ni fa ba rokon ya so ni nake yi ba. Sannan ke kina ganin nayi miki kama da wadanda maza zasu kalla suji basa so ne?".
Ta girgiza kai tana murmushi, "ba karya abokiyar, kinyi fa! Ai karya ne wani da namiji ya kalleki yace baki yi ba, ko matan ma tankawa suke yi balle kuma maza. Abinda kawai nake so ki sani shine, ku hausawa da kanku ne kuka ce idan kana kyau ka kara da wanka. Kinga duk da kina da kyanki tubarkallah son kowa kin wanda ya rasa, ina ga da kin dan kara koda mascara ne da eyeshadow yadda zaki kara fitowa sosai, ki kara rikita shi, kin gane ai".
Ni duk bayanan da take watsawa sauraronta kawai nake yi ba wai don ina fahimtarta ba, duk wucewar dakika daya, fargabar dake cikin zuciyata karuwa take yi. Nerves sun cika min ciki.
Nace mata "ni duk ban damu da irin wadannan abubuwan ba, fatana kawai ya karbeni a yadda nake. Zan fi son ya ganni a ainihin wacece ni, ba wai kyale-kyalin banza ba".
Tace "kinyi yar gaskiya kuma". Ni dai na kauda kaina gefe kawai don bana jin zan iya tsayawa yin doguwar hira a halin da nake ciki yanzu.
Karfe biyar da rabi daidai, sai ga kiran wayarshi. Hannuwana har rawa suke yi lokacin dana dauki wayar na karata a saitin kunnena. Nace "hello?", da kyar kamar wadda take koyon magana.
Yace "yanzu na karaso kofar hostel din, ina daga waje ina jiranki", cikin wani irin husky voice, deep and soothing a lokaci guda. Sai naji kamar yau na taba jin muryar. Naji wata irin rawar cikin jiki ta ziyarceni, kamar na fito waje cikin muku-mukun sanyinnan, na kakaro sautin "to", daga can kasan makoshi na kamar an shake ni. Na kashe wayar na ajiye a gefena ina maida numfashi da sauri da sauri kamar wadda tayi gudun ceton rai.
Sai dana tabbatar da natsuwata ta dawo cikin jikina, sannan na tashi tsaye, duk da haka sai da naji kamar zan kifa saboda yadda kafafuna suke rawa. Wani tray dana amsa wajen Esther, mai fadi ne ba laifi, da zanen manyan jajayen furanni a jiki. A cikin jug dinshi na zuba zobon da nayi, na yanka cucumber da kankana kanana a ciki bayan na cire 'ya'yan, su kuma kananun cups din jug din na kifa guda biyu akan tray din.
Na shirya meat pie din akan wani karamin plate, na kawo foil paper na rufe shi. Na dora lemun dana amso da ruwan akan tray din, aka yi sa'a ya kwashe duka.
Na kara duba fuskata a cikin madubi naga lafiya lau, na dauki gyale mai dan fadi nayi yafawar zamani, na kawo turaren fantasy na kara badawa a jikina. Duk wadannan abubuwa da nake yi, cikin takatsan-tsan da rawar jiki nake yinsu. Na dauki takalmi mai dan tudu baki na saka, sannan na dauki tray din wannan da wayata na fita.
Akwai wani karamin waje daga can gefen hostel din, yawanci dalibai kanyi karatu a ciki musamman irin group assignment da aka hada maza da mata a ciki, nan suke zuwa suyi karatun. Ko kuma idan wata daliba tayi baki nan take zuwa dasu idan maza ne. Nima can na fito da rana na samu wata yar kwana, inda babu yawan giccin mutane sosai na share na kuma goge kujerun da aka kera na sumunti a wajen da niyar nan zan jagoranci Muhammad din idan yazo.
Lokacin dana fito waje ban ga kowa ba, da alamu a can wajen gate ya tsaya, don haka na fara kai kayan hannuna wajen da zamu zauna na ajiye su, sannan na taka a hankali zuwa wajen gate din. Idan wani ya kalleni a lokacin, nasan babu bata lokaci zai ce tafiyar yanga ce nake yi, sai dai a zahirin gaskiya, tsananin fargaba da tsoro ne suka sa nake tafiya kamar wadda take jan kafarta. Ban san dalilin wannan sudden tsoro da naji ya dirar min ba, amma nafi danganta hakan da cewa kila saboda kawai haduwarmu ta farko kenan yau.
Na fita daga gate din, idanuwana suka fara karade ilahirin wajen da kallo, ina duba gefena na dama, na hango shi. Jingine da motar rav4 baka kirin, sanye yake da wata jikakkiyyar danyar shaddar getzner ruwan kasa mai haske, ta sha dinkin surfani na zare shima ruwan kasa amma mai duhu sosai, takalmin kafarshi shima ruwan kasar ne irin flats dinnan na maza, ko ba'a fada maka ba kasan ba karamin kudi da daraja zasu yi ba. Daga inda nake, babu abinda zan iya karaswa game da features dinshi, kawai dai nasan dogo ne, ya danyi min nisa, ban hangi komi a fuskarshi ba, musamman da yake a daidai wannan lokacin ya nutsa wayar tashi cikin wayar hannunshi. Sai hular kanshi kawai.
Na samu kaina da takawa a hankali zuwa inda yake, kaina a kasa ban iya dagowa na kalleshi ba saboda wani irin nauyinshi da naji ya dirar min, amma duk da kan nawa a kasa yake, ina jin zafin kallonshi a cikin jikina. Sai dana fara ganin kyawawan jerin dogaye kuma zara-zaran yatsun kafarshi da suka yi matukar kyawu cikin kyakkyawan takalmin kafarshi, sannan na iya daga kaina a hankali.
'Assalamu Alaik...", sallamar da nayi niyar yi mishi, ta makale a makoshina lokacin da na dago kai a lokacin, muka hada idanu hur-hudu dashi.
Fuskarshi bata nuna mamaki, al'ajabi ko rikicewar tunani kamar yadda na tabbatar suna zane akan fuskata ba baro-baro. A tsaye take kyam, maimakon hakan ma, sai wani tattausan murmushi daya bayyana akan fatar bakinshi.
Yace "wa alaikumussalam wa rahmatullah... Har kin fito?".
Na tsinci kaina da karkata kaina gefe guda cikin tsananin mamaki, can kasan zuciyata kuma ina maimaita kalmar 'har kin fito?', ko me yake nufi da hakan?.
Na dan duka cike da girmamawa nace "Yaya Bilal ina yini?". Gabadayan idanunshi fuskata suke karewa kaina kallo kamar yau ya taba ganina, yace "lafiya lau Na'ilah! Ya kike?".
Na gyada kai kawai, zuciyata cike da tambayoyi, yayin da a gefe guda kuma naci gaba da dube-dube ko zan hango Muhammad. Ya nake ganin kamar mu kadai ne a gaban hostel din? Ko kuma bai zo ba yace min yazo?.
Na furta tambayar da take ta ci min rai tunda naci karo da Yaya ne, nace "ko kazo wajen wata ne anan ko wani?", a raina nace ko dai wani auren yake nema ne? Na danyi shivering lokacin da tunanin abinda hakan yake nufi ya darsu a cikin raina.
Ya cigaba da jefa min irin wannan kallo da tunda muka hadu dashi yake jefa min, yana kuma gyada kai a hankali, "wata".
Na dan zare ido cikin mamaki, kafin nayi kokarin maida mamakina na kulle, sai anjima Janan zata sha labari, nace "uhmm, to. Dama nima akwai wanda na fito gani ne dama, tunda bai zo ba kuma bari in koma, ka samu wadda kazo ganinta ne ko kuma kana bukatar in dubo maka ita ne?".
Idanuwanshi na fitar da wasu alamu, awe and mischief, yace "a'ah, no need. Nagode. Na ganta ai, gata nan a gabana!".
Na dan juya bayana cikin tunanin in hadu da wadda take nufi din, sai naga wayam. Na girgiza kai kamar wadda take kokarin shaking din wani feeling, gabadaya abinda yake faruwa yanzu yana da matukar daure kai, na kasa banbance tsakanin karya da gaskiya. Ina bukatar in ganni a cikin dakina, in kwanta akan katifa inyi tunanin abinda yake faruwa.
Na gyada kai a hankali, a hankalin dai nace "to shikenan, zan koma ciki ni, a gaida gida". Kafin ma ya samu damar daga baki ya maido min amsa, maybe juya da sauri na daga kafata na fara tafiya.
Yace "Na'ilah, Muhammad ne fa!".
Naji na tsaya cak, kamar wadda aka kafe. A hankali na juya, zuciyata tana bugu da karfin masifa, cikin idanunshi nake kallo directly, ina laluben wani alamu da zai nuna wasa yake yi a cikin idanun nashi. Tunani nake, ta yaya aka yi yasan zance na da Muhammad? Ko dai yana daga cikin abokanshi ne? Haba, babu mamaki. Kila ma Muhammad din abokinshi ne, kila shi yasa zai biyo shi su zo tare ko. Na dauke idanuna daga kanshi zuwa cikin motarshi, so nake inga ko akwai alamun mutum a ciki, amma duhun gilasan motar ya hana in hango komi.
Kallon-kallo muka fara yi dashi, ganin bashi da niyar yi mun karin bayani akan wannan katoton al'amari, yasa ni na bude baki kamar wadda take tsoron magana, nace mishi "a ina kasan Muhammad? Ka san shi ne?".
Akwai wani nag feeling da yake damuna, daga can kasan zuciyata, wani bangarene yake jefo min tambayar, anya? Amma nake danne shi tun karfina, babu wata anya ko tantama, babu abinda yake faruwa. Yaya Bilal ba wani bane face aboki, ko kuma wani daya san zancena da Muhammad, and nothing more!.
Maimakon ya bani amsar tambayar daya min, sai ya daga kafa ya fara takowa a hankali har ya iso daf dani, ni kuma saboda tsabar rikici, na rasa ta yaya zan iya daga kafata inyi baya duk da cewa mun danyi kusanci dashi. A hakan ina iya shakar kamshin turaren daya fesa, kamar tufafin na nutsa a fuskata.
Ya daga yatsarshi manuniya yana nuna saitin kirjinshi, yace "ni nan, Na'ilah, nine dai Muhammad din da kike jira, Muhammad naki, wanda zai so ya ganki!".
Na kura mishi idanu kawai, idan banda bugun zuciyata babu abinda ya canza daga yanayin motsin jikina. Kila ma sandarewa nayi a tsaye ban sani ba. Ban san me yasa Yaya Bilal zai ji bukatar yayi min irin wannan wasan ba, halayenshi na kamewa da rashin son wasa yasa kwata-kwata na kasa yarda da cewa tsokana ce kawai kamar yadda nake nanatawa kaina domin karyata abinda zuciyata take fada min tunda na bayyana a gaban Yaya Bilal yanzu.
Allah kadai yasan iya lokacin dana dauka a haka, kawai ina kallonshi kamar wata bakuwar halitta. Na rasa gane a duniyar da nake, shin duniyar mafarki ce ko kuma ta gaske?.
Na samu kuzarin daga baki da kyar, bayan dogon lokacin nan, nace "wane Muhammad kake magana akai, Yaya?".
Ta girgiza kai tana murmushi, "ba karya abokiyar, kinyi fa! Ai karya ne wani da namiji ya kalleki yace baki yi ba, ko matan ma tankawa suke yi balle kuma maza. Abinda kawai nake so ki sani shine, ku hausawa da kanku ne kuka ce idan kana kyau ka kara da wanka. Kinga duk da kina da kyanki tubarkallah son kowa kin wanda ya rasa, ina ga da kin dan kara koda mascara ne da eyeshadow yadda zaki kara fitowa sosai, ki kara rikita shi, kin gane ai".
Ni duk bayanan da take watsawa sauraronta kawai nake yi ba wai don ina fahimtarta ba, duk wucewar dakika daya, fargabar dake cikin zuciyata karuwa take yi. Nerves sun cika min ciki.
Nace mata "ni duk ban damu da irin wadannan abubuwan ba, fatana kawai ya karbeni a yadda nake. Zan fi son ya ganni a ainihin wacece ni, ba wai kyale-kyalin banza ba".
Tace "kinyi yar gaskiya kuma". Ni dai na kauda kaina gefe kawai don bana jin zan iya tsayawa yin doguwar hira a halin da nake ciki yanzu.
Karfe biyar da rabi daidai, sai ga kiran wayarshi. Hannuwana har rawa suke yi lokacin dana dauki wayar na karata a saitin kunnena. Nace "hello?", da kyar kamar wadda take koyon magana.
Yace "yanzu na karaso kofar hostel din, ina daga waje ina jiranki", cikin wani irin husky voice, deep and soothing a lokaci guda. Sai naji kamar yau na taba jin muryar. Naji wata irin rawar cikin jiki ta ziyarceni, kamar na fito waje cikin muku-mukun sanyinnan, na kakaro sautin "to", daga can kasan makoshi na kamar an shake ni. Na kashe wayar na ajiye a gefena ina maida numfashi da sauri da sauri kamar wadda tayi gudun ceton rai.
Sai dana tabbatar da natsuwata ta dawo cikin jikina, sannan na tashi tsaye, duk da haka sai da naji kamar zan kifa saboda yadda kafafuna suke rawa. Wani tray dana amsa wajen Esther, mai fadi ne ba laifi, da zanen manyan jajayen furanni a jiki. A cikin jug dinshi na zuba zobon da nayi, na yanka cucumber da kankana kanana a ciki bayan na cire 'ya'yan, su kuma kananun cups din jug din na kifa guda biyu akan tray din.
Na shirya meat pie din akan wani karamin plate, na kawo foil paper na rufe shi. Na dora lemun dana amso da ruwan akan tray din, aka yi sa'a ya kwashe duka.
Na kara duba fuskata a cikin madubi naga lafiya lau, na dauki gyale mai dan fadi nayi yafawar zamani, na kawo turaren fantasy na kara badawa a jikina. Duk wadannan abubuwa da nake yi, cikin takatsan-tsan da rawar jiki nake yinsu. Na dauki takalmi mai dan tudu baki na saka, sannan na dauki tray din wannan da wayata na fita.
Akwai wani karamin waje daga can gefen hostel din, yawanci dalibai kanyi karatu a ciki musamman irin group assignment da aka hada maza da mata a ciki, nan suke zuwa suyi karatun. Ko kuma idan wata daliba tayi baki nan take zuwa dasu idan maza ne. Nima can na fito da rana na samu wata yar kwana, inda babu yawan giccin mutane sosai na share na kuma goge kujerun da aka kera na sumunti a wajen da niyar nan zan jagoranci Muhammad din idan yazo.
Lokacin dana fito waje ban ga kowa ba, da alamu a can wajen gate ya tsaya, don haka na fara kai kayan hannuna wajen da zamu zauna na ajiye su, sannan na taka a hankali zuwa wajen gate din. Idan wani ya kalleni a lokacin, nasan babu bata lokaci zai ce tafiyar yanga ce nake yi, sai dai a zahirin gaskiya, tsananin fargaba da tsoro ne suka sa nake tafiya kamar wadda take jan kafarta. Ban san dalilin wannan sudden tsoro da naji ya dirar min ba, amma nafi danganta hakan da cewa kila saboda kawai haduwarmu ta farko kenan yau.
Na fita daga gate din, idanuwana suka fara karade ilahirin wajen da kallo, ina duba gefena na dama, na hango shi. Jingine da motar rav4 baka kirin, sanye yake da wata jikakkiyyar danyar shaddar getzner ruwan kasa mai haske, ta sha dinkin surfani na zare shima ruwan kasa amma mai duhu sosai, takalmin kafarshi shima ruwan kasar ne irin flats dinnan na maza, ko ba'a fada maka ba kasan ba karamin kudi da daraja zasu yi ba. Daga inda nake, babu abinda zan iya karaswa game da features dinshi, kawai dai nasan dogo ne, ya danyi min nisa, ban hangi komi a fuskarshi ba, musamman da yake a daidai wannan lokacin ya nutsa wayar tashi cikin wayar hannunshi. Sai hular kanshi kawai.
Na samu kaina da takawa a hankali zuwa inda yake, kaina a kasa ban iya dagowa na kalleshi ba saboda wani irin nauyinshi da naji ya dirar min, amma duk da kan nawa a kasa yake, ina jin zafin kallonshi a cikin jikina. Sai dana fara ganin kyawawan jerin dogaye kuma zara-zaran yatsun kafarshi da suka yi matukar kyawu cikin kyakkyawan takalmin kafarshi, sannan na iya daga kaina a hankali.
'Assalamu Alaik...", sallamar da nayi niyar yi mishi, ta makale a makoshina lokacin da na dago kai a lokacin, muka hada idanu hur-hudu dashi.
Fuskarshi bata nuna mamaki, al'ajabi ko rikicewar tunani kamar yadda na tabbatar suna zane akan fuskata ba baro-baro. A tsaye take kyam, maimakon hakan ma, sai wani tattausan murmushi daya bayyana akan fatar bakinshi.
Yace "wa alaikumussalam wa rahmatullah... Har kin fito?".
Na tsinci kaina da karkata kaina gefe guda cikin tsananin mamaki, can kasan zuciyata kuma ina maimaita kalmar 'har kin fito?', ko me yake nufi da hakan?.
Na dan duka cike da girmamawa nace "Yaya Bilal ina yini?". Gabadayan idanunshi fuskata suke karewa kaina kallo kamar yau ya taba ganina, yace "lafiya lau Na'ilah! Ya kike?".
Na gyada kai kawai, zuciyata cike da tambayoyi, yayin da a gefe guda kuma naci gaba da dube-dube ko zan hango Muhammad. Ya nake ganin kamar mu kadai ne a gaban hostel din? Ko kuma bai zo ba yace min yazo?.
Na furta tambayar da take ta ci min rai tunda naci karo da Yaya ne, nace "ko kazo wajen wata ne anan ko wani?", a raina nace ko dai wani auren yake nema ne? Na danyi shivering lokacin da tunanin abinda hakan yake nufi ya darsu a cikin raina.
Ya cigaba da jefa min irin wannan kallo da tunda muka hadu dashi yake jefa min, yana kuma gyada kai a hankali, "wata".
Na dan zare ido cikin mamaki, kafin nayi kokarin maida mamakina na kulle, sai anjima Janan zata sha labari, nace "uhmm, to. Dama nima akwai wanda na fito gani ne dama, tunda bai zo ba kuma bari in koma, ka samu wadda kazo ganinta ne ko kuma kana bukatar in dubo maka ita ne?".
Idanuwanshi na fitar da wasu alamu, awe and mischief, yace "a'ah, no need. Nagode. Na ganta ai, gata nan a gabana!".
Na dan juya bayana cikin tunanin in hadu da wadda take nufi din, sai naga wayam. Na girgiza kai kamar wadda take kokarin shaking din wani feeling, gabadaya abinda yake faruwa yanzu yana da matukar daure kai, na kasa banbance tsakanin karya da gaskiya. Ina bukatar in ganni a cikin dakina, in kwanta akan katifa inyi tunanin abinda yake faruwa.
Na gyada kai a hankali, a hankalin dai nace "to shikenan, zan koma ciki ni, a gaida gida". Kafin ma ya samu damar daga baki ya maido min amsa, maybe juya da sauri na daga kafata na fara tafiya.
Yace "Na'ilah, Muhammad ne fa!".
Naji na tsaya cak, kamar wadda aka kafe. A hankali na juya, zuciyata tana bugu da karfin masifa, cikin idanunshi nake kallo directly, ina laluben wani alamu da zai nuna wasa yake yi a cikin idanun nashi. Tunani nake, ta yaya aka yi yasan zance na da Muhammad? Ko dai yana daga cikin abokanshi ne? Haba, babu mamaki. Kila ma Muhammad din abokinshi ne, kila shi yasa zai biyo shi su zo tare ko. Na dauke idanuna daga kanshi zuwa cikin motarshi, so nake inga ko akwai alamun mutum a ciki, amma duhun gilasan motar ya hana in hango komi.
Kallon-kallo muka fara yi dashi, ganin bashi da niyar yi mun karin bayani akan wannan katoton al'amari, yasa ni na bude baki kamar wadda take tsoron magana, nace mishi "a ina kasan Muhammad? Ka san shi ne?".
Akwai wani nag feeling da yake damuna, daga can kasan zuciyata, wani bangarene yake jefo min tambayar, anya? Amma nake danne shi tun karfina, babu wata anya ko tantama, babu abinda yake faruwa. Yaya Bilal ba wani bane face aboki, ko kuma wani daya san zancena da Muhammad, and nothing more!.
Maimakon ya bani amsar tambayar daya min, sai ya daga kafa ya fara takowa a hankali har ya iso daf dani, ni kuma saboda tsabar rikici, na rasa ta yaya zan iya daga kafata inyi baya duk da cewa mun danyi kusanci dashi. A hakan ina iya shakar kamshin turaren daya fesa, kamar tufafin na nutsa a fuskata.
Ya daga yatsarshi manuniya yana nuna saitin kirjinshi, yace "ni nan, Na'ilah, nine dai Muhammad din da kike jira, Muhammad naki, wanda zai so ya ganki!".
Na kura mishi idanu kawai, idan banda bugun zuciyata babu abinda ya canza daga yanayin motsin jikina. Kila ma sandarewa nayi a tsaye ban sani ba. Ban san me yasa Yaya Bilal zai ji bukatar yayi min irin wannan wasan ba, halayenshi na kamewa da rashin son wasa yasa kwata-kwata na kasa yarda da cewa tsokana ce kawai kamar yadda nake nanatawa kaina domin karyata abinda zuciyata take fada min tunda na bayyana a gaban Yaya Bilal yanzu.
Allah kadai yasan iya lokacin dana dauka a haka, kawai ina kallonshi kamar wata bakuwar halitta. Na rasa gane a duniyar da nake, shin duniyar mafarki ce ko kuma ta gaske?.
Na samu kuzarin daga baki da kyar, bayan dogon lokacin nan, nace "wane Muhammad kake magana akai, Yaya?".