Sashe 64
A Zato Na Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ban kulata ba na tashi na hau gwada kayan. Na cire wata doguwar riga da tsabar tsagar da aka yiwa hannuwanta, baka banbanceta da vest sai idan kaga dogayen lebatun da aka mata, na ja tsaki, nace "gaskiya baki kyauta min ba Janan, wannan ai bata min kaya kawai kika sa aka yi ba wani abu ba".
Janan tayi murmushi, tace "kada ki damu matar Yaya, zaki gode min ne nan gaba".
Haka dai na hada kayan naje na shirya su cikin wardrobe, sai dai bani da niyar sanya su a cikin raina koda kadan. Kawai na riga na gama rayawa raina asarar kaya da kudin dinki Janan tayi.
Na koma falo muka cigaba da hirarmu ni da ita, har yamma tayi, Is'hak da zai kaita gida ya mana sallama da yake yau zata koma gida. Na rakata har bakin motar muka yi sallama da ita cike da kewa da kauna.
Anan muka hadu da Mimah itama tazo mata sallama, naja hannunta muka koma sashena, na kunno mata cartoons tana kallo, ni kuma na shiga kicin na fara hada dinner.
Da dare sai ga Yaya Bilal ya dawo da sabuwar waya kar a kwalinta, da sabin sims guda biyu.
Nace "ita fa waccan wayar tawa?".
Bai ko kalleni ba, yana ta tura abincin dana girka mishi, yace "nayi kyauta da ita!".
Na turo baki gaba kamar zanyi kuka, nace "amma fa akwai lambobin mutane da dama da zan rasa, kuma za ayi ta kirana ba'a samuna!".
Yace "manufar hakan kenan ai dama, ba zai yiwu in zauna in rabbe hannu a kirji ba ina kallo wasu gardawan kawai na kira min mata ba. Ban yarda ki ba kowa lambar wayarki ba sai wanda ya dace, kina ji na?".
Duk da na jinjina wannan karfin iko da mallaka, hakan bai hana ni amsa shi ba, nace "to, nagode, Allah ya kara budi".
Ko baiyi tunanin zan amince cikin sauki ba ne? Ya kalleni cikin mamaki, kafin yayi murmushi yace "yauwa baby na, ko ke fa?". Muka cigaba da cin abincinmu.
Bayan mun gama, ya wuce dakinshi zai watsa ruwa a cewarshi, ni kuma na koma dakina nima. Nayi brush, na fito na sanya kayan barci, nayi shafa'i da wutiri, sannan na kwanta.
Ban jima da kwanciyar ba sai gashi ya turo kofar dakin ya shigo. Ya kashe wutar dakin tare da hayowa kan gadon da nake, ya janyo ni cikin jikinshi.
Gabana dukan uku-uku yake yi, musamman lokacin da naji ya fara aika min nauyayan sakonni a cikin sassan jikina. Sai da tafiya tayi nisa, ni a kaina na fara fita daga hayyacina, naji tausassan sautin minshari yana tashi a kusa dani. Sai dai wannan karon, ban samu kaina da darawa kamar jiya ba, daga kai nayi ina kallonshi cike da mamakin abinda yake faruwa. Wani abu a tattare da wannan lamari just seems off.
*
Wasa-wasa abin dariya fa yake neman juyewa ya zama abin kuka. Kullum haka abin yake kasancewa, wani abin mamaki ma shi Yayan kamar bai san hakan tana faruwa ba. Saboda washegari normal zamu tashi ni dashi, babu wata alama ta ya tuna abinda ya faru a daren daya gabata a tattare dashi. Damuwa ta fara lullubeni, tunani ya fara addabata, tabbas akwai wata a kasa. Sai dai kafin in tono abinda yake a kasan, har ranar Lahdi ta zagayo, ranar dana fita girki, ranar da zamu koma Abuja kuma.
Ranar tun da safe na gama hada duk wasu kaya da zan tafi dasu. Duk wadanda yakamata mu yi sallama dasu, mun riga mun yi.
Karfe hudu Yaya ya leko yace min in fito zamu tafi, tun dazun aka fitar da kayan dana riga na shirya. Su kuma kayan dakin na samu manyan ledoji na lullubesu saboda kura.
Na fito tare da kulle kofata, na saka makullin cikin jakata.
Na leka sashen Anty Sarah na sanar da ita zamu wuce, ta saba Rabi'ah a kafadarta muka fito ni da ita.
Yaya Bilal da Yaya Jameel suna tsaye a gaban motar suna tattaunawa, muka tsaya anan gefensu muna jiran Raheemah ta fito. Sai yau kannen nata suka hada kan kayansu suka tafi. Da safe naga ana ta fita da kaya da tarkace, kusan zaryarsu biyu. Wani saurayin Salame ne yake ta zaryar kai kayan da dawowa ya lodi wasu. Na fito daga sashen Anty Sarah da safen, naci karo dasu sun fito kowacce na jan akwati kamar zasu je ci rani. Suna ta kwashewa mai motar albarkar saboda ya tsaida su suna ta jiran shi, suka daka min harara lokacin da suka ganni, ni kuwa na daga kafada na wuce abina.
Sai da muka kusa yin mintuna biyar muna jiranta a wajen, har sai da Yaya ya kai ga kiranta ya tunatar da ita muna jiranta fa, amma babu ita babu alamunta.
Yaya ya shaka, ya bude min gaba tare da umartata akan in shiga mu tafi, Yaya Jameel yace "kai kuwa ayi haka? Ku dan kara jiranta mana".
Yaya yace "yo ai ko aikina kenan zaman jira, yaci ace an zo an sallameni. A kanta zan kare ne?".
Yana tashin motar, sai gata ta fito tana takunta dagwas-dagwas kamar bata shanya mutane suna jiranta ba. Tazo ta gefen inda nake a zaune, ta bude kofar tayi wani kerere, ita bata juya ba, ita kuma bata ce komi ba, sai muzurai.
Yaya ya kalleta cikin kullewa, "idan ba zaki tafi bane, ki maida mana murfin motar mu mu wuce".
Bata ce komi ba, ta maida murfin motar da karfi ta rufe kamar zata balla shi. Ta bude baya ta shiga tana harare-harare da muzurai.
Su Yaya Jameel suka mana addu'ar Allah ya tsare, Yaya Bilal ya tashi motar muka fita daga gidan.
Daga farko nayi tunanin ko zamu biya ta gidan Anty Ameerah ne mu daukota, amma sai naga Yaya ya dauki hanyar fita daga Zaria straight.
A raina na raya tunda ita din shafaffiya ce da mai, yar gaban goshi, tana da motar hawa ta kanta, kila da kanta ta tafi.
Tafiya muke cikin madaidaicin gudu, bayan sautin radio da take ta aikin yi, baka jin motsin komi a cikin motar.
Yaya ya fara katse mana shirun ta hanyar fara tambayata yanayin yadda tsarin internship dinmu zai kasance. Nan da nan hira ta barke a tsakaninmu. Muna cikin yin hirar, zaka ji Raheemah itama ta tsoma nata bakin a ciki. Duk da ba tamu hirar take sanyawa baki ba, tata kalar hirar daban. Na kula tun karfinta take kokarin janye hankalin Yaya daga kaina.
Daga karshe dai da abin ya ishe ni, sai na kwantar da kaina akan kujera na kyalesu suna ta hirar su kamar ina yin barci.
🙏🙏🙏
#F.W.A
*☆⋆38⋆☆*
Gidan Yaya Bilal babba ne, mai kyau na gaban kwatance. Lokacin da muka fara shiga Abuja barci ya fara daukata, haka na bude idanu ina kallon gari. Duk da cewa ba wannan ne karona na farko zuwa Abuja ba, amma kuma na jima kwarai rabona da garin. Shi yasa yanzu nake ganina kamar wata sabuwar zuwa.
Yaya yayi ta ratsa tituna da ginunnuka har muka isa wata unguwa da tun daga bakin gate naga an rubuta Maitama. Duk yawace-yawacena ban taba biyowa ta nan wajajen ba. Daga gani babu tambaya unguwa ce ta masu hannu da shuni, tun daga kan ginunnukan da kuma tsari da yanayin unguwar. Ba karamin burgeni tayi ba.
Yaya ya tsaya a kofar wani madaidaicin gida, yayi amfani da remote, gate din gidan daya kasance ruwan zuma mai cizawa, da wata irin raga-raga daga tsakiya wadda take baka damar hango tanfatsetsen ginin dake ciki, ya bude da kanshi. Yaya Bilal ya silala kan motar ta shiga ciki, muna shiga gate din gidan ya koma ya rufe.
Wajen ajiye motoci muka fara tararwa, waje na mai fadi da zai cinye motoci akalla guda biyar. Yayi parking din motar, muka fito muna karewa gidan kallo. Motoci biyu ne a garejin, rufe da tampol dinsu. Ya mana jagora zuwa gidan. Daga gefen garejin akwai karamin waje da aka yi shuke-shuken bishiyoyi da furanni da basu fara tsayi ba, da alamu sabon garden ne aka yi. Sai kuwa kofar gidan, kana shiga dogon corridor ne da zai kaika har tsakiyar wani babban falo, kana shiga corridor din zaka ci karo da wata kofa da zata sadaka da kicin.
Babban falon ya dauki saitin royal setting, daga kan kujeru, carpet, labulaye, da fenti, duk golden ne da ratsin royal blue. A cikin babban falon dinning room yake, sai kuwa kicin da kofar su daya da dinning room din, sai babban store.
Kana fita daga babban falon anan dakunan mu suke, suma dai tubarkallah manya ne, daya yana kallon daya, inda nan ne ya nunawa Raheemah daya a matsayin nata, dayan kuma a matsayin na Ameerah da bamu gani ba, kila ita sai anjima ko kuma washegari. Daga gaban nasu kadan nan nawa dakin yake, daga gefen nawa kuma akwai dakuna guda biyu, babu komi a ciki daga carpet sai katifa da labulaye, kila dakin baki ne ko kuma na yara. Daga nan ya jamu, muka bi ta gefen dakunan zuwa master bedroom, inda dakinshi yake. Shima dakine babba mai fadi sosai. Daga dakin nashi muka sake fita zuwa wani falon da bai kai wancan girma ba, shima dai saitin kujeru ne da madaidaiciyar tv, sai tagogin wajen da suka kasance manya, irin daga sama zuwa kasa dinnan na gilasai, kana hango karamin lambun daga nan. Wajen dai ya hadu kwarai, just spectacular. Da ya bude wata kofa daga nan falon, sai muka sake bayyana a babban falo.
Bayan ya gama nuna mana gida da kuma ko'ina da ko'ina dai, sai duk muka wuce dakunanmu domin yin sallah da aka fara kira.
Janan tayi murmushi, tace "kada ki damu matar Yaya, zaki gode min ne nan gaba".
Haka dai na hada kayan naje na shirya su cikin wardrobe, sai dai bani da niyar sanya su a cikin raina koda kadan. Kawai na riga na gama rayawa raina asarar kaya da kudin dinki Janan tayi.
Na koma falo muka cigaba da hirarmu ni da ita, har yamma tayi, Is'hak da zai kaita gida ya mana sallama da yake yau zata koma gida. Na rakata har bakin motar muka yi sallama da ita cike da kewa da kauna.
Anan muka hadu da Mimah itama tazo mata sallama, naja hannunta muka koma sashena, na kunno mata cartoons tana kallo, ni kuma na shiga kicin na fara hada dinner.
Da dare sai ga Yaya Bilal ya dawo da sabuwar waya kar a kwalinta, da sabin sims guda biyu.
Nace "ita fa waccan wayar tawa?".
Bai ko kalleni ba, yana ta tura abincin dana girka mishi, yace "nayi kyauta da ita!".
Na turo baki gaba kamar zanyi kuka, nace "amma fa akwai lambobin mutane da dama da zan rasa, kuma za ayi ta kirana ba'a samuna!".
Yace "manufar hakan kenan ai dama, ba zai yiwu in zauna in rabbe hannu a kirji ba ina kallo wasu gardawan kawai na kira min mata ba. Ban yarda ki ba kowa lambar wayarki ba sai wanda ya dace, kina ji na?".
Duk da na jinjina wannan karfin iko da mallaka, hakan bai hana ni amsa shi ba, nace "to, nagode, Allah ya kara budi".
Ko baiyi tunanin zan amince cikin sauki ba ne? Ya kalleni cikin mamaki, kafin yayi murmushi yace "yauwa baby na, ko ke fa?". Muka cigaba da cin abincinmu.
Bayan mun gama, ya wuce dakinshi zai watsa ruwa a cewarshi, ni kuma na koma dakina nima. Nayi brush, na fito na sanya kayan barci, nayi shafa'i da wutiri, sannan na kwanta.
Ban jima da kwanciyar ba sai gashi ya turo kofar dakin ya shigo. Ya kashe wutar dakin tare da hayowa kan gadon da nake, ya janyo ni cikin jikinshi.
Gabana dukan uku-uku yake yi, musamman lokacin da naji ya fara aika min nauyayan sakonni a cikin sassan jikina. Sai da tafiya tayi nisa, ni a kaina na fara fita daga hayyacina, naji tausassan sautin minshari yana tashi a kusa dani. Sai dai wannan karon, ban samu kaina da darawa kamar jiya ba, daga kai nayi ina kallonshi cike da mamakin abinda yake faruwa. Wani abu a tattare da wannan lamari just seems off.
*
Wasa-wasa abin dariya fa yake neman juyewa ya zama abin kuka. Kullum haka abin yake kasancewa, wani abin mamaki ma shi Yayan kamar bai san hakan tana faruwa ba. Saboda washegari normal zamu tashi ni dashi, babu wata alama ta ya tuna abinda ya faru a daren daya gabata a tattare dashi. Damuwa ta fara lullubeni, tunani ya fara addabata, tabbas akwai wata a kasa. Sai dai kafin in tono abinda yake a kasan, har ranar Lahdi ta zagayo, ranar dana fita girki, ranar da zamu koma Abuja kuma.
Ranar tun da safe na gama hada duk wasu kaya da zan tafi dasu. Duk wadanda yakamata mu yi sallama dasu, mun riga mun yi.
Karfe hudu Yaya ya leko yace min in fito zamu tafi, tun dazun aka fitar da kayan dana riga na shirya. Su kuma kayan dakin na samu manyan ledoji na lullubesu saboda kura.
Na fito tare da kulle kofata, na saka makullin cikin jakata.
Na leka sashen Anty Sarah na sanar da ita zamu wuce, ta saba Rabi'ah a kafadarta muka fito ni da ita.
Yaya Bilal da Yaya Jameel suna tsaye a gaban motar suna tattaunawa, muka tsaya anan gefensu muna jiran Raheemah ta fito. Sai yau kannen nata suka hada kan kayansu suka tafi. Da safe naga ana ta fita da kaya da tarkace, kusan zaryarsu biyu. Wani saurayin Salame ne yake ta zaryar kai kayan da dawowa ya lodi wasu. Na fito daga sashen Anty Sarah da safen, naci karo dasu sun fito kowacce na jan akwati kamar zasu je ci rani. Suna ta kwashewa mai motar albarkar saboda ya tsaida su suna ta jiran shi, suka daka min harara lokacin da suka ganni, ni kuwa na daga kafada na wuce abina.
Sai da muka kusa yin mintuna biyar muna jiranta a wajen, har sai da Yaya ya kai ga kiranta ya tunatar da ita muna jiranta fa, amma babu ita babu alamunta.
Yaya ya shaka, ya bude min gaba tare da umartata akan in shiga mu tafi, Yaya Jameel yace "kai kuwa ayi haka? Ku dan kara jiranta mana".
Yaya yace "yo ai ko aikina kenan zaman jira, yaci ace an zo an sallameni. A kanta zan kare ne?".
Yana tashin motar, sai gata ta fito tana takunta dagwas-dagwas kamar bata shanya mutane suna jiranta ba. Tazo ta gefen inda nake a zaune, ta bude kofar tayi wani kerere, ita bata juya ba, ita kuma bata ce komi ba, sai muzurai.
Yaya ya kalleta cikin kullewa, "idan ba zaki tafi bane, ki maida mana murfin motar mu mu wuce".
Bata ce komi ba, ta maida murfin motar da karfi ta rufe kamar zata balla shi. Ta bude baya ta shiga tana harare-harare da muzurai.
Su Yaya Jameel suka mana addu'ar Allah ya tsare, Yaya Bilal ya tashi motar muka fita daga gidan.
Daga farko nayi tunanin ko zamu biya ta gidan Anty Ameerah ne mu daukota, amma sai naga Yaya ya dauki hanyar fita daga Zaria straight.
A raina na raya tunda ita din shafaffiya ce da mai, yar gaban goshi, tana da motar hawa ta kanta, kila da kanta ta tafi.
Tafiya muke cikin madaidaicin gudu, bayan sautin radio da take ta aikin yi, baka jin motsin komi a cikin motar.
Yaya ya fara katse mana shirun ta hanyar fara tambayata yanayin yadda tsarin internship dinmu zai kasance. Nan da nan hira ta barke a tsakaninmu. Muna cikin yin hirar, zaka ji Raheemah itama ta tsoma nata bakin a ciki. Duk da ba tamu hirar take sanyawa baki ba, tata kalar hirar daban. Na kula tun karfinta take kokarin janye hankalin Yaya daga kaina.
Daga karshe dai da abin ya ishe ni, sai na kwantar da kaina akan kujera na kyalesu suna ta hirar su kamar ina yin barci.
🙏🙏🙏
#F.W.A
*☆⋆38⋆☆*
Gidan Yaya Bilal babba ne, mai kyau na gaban kwatance. Lokacin da muka fara shiga Abuja barci ya fara daukata, haka na bude idanu ina kallon gari. Duk da cewa ba wannan ne karona na farko zuwa Abuja ba, amma kuma na jima kwarai rabona da garin. Shi yasa yanzu nake ganina kamar wata sabuwar zuwa.
Yaya yayi ta ratsa tituna da ginunnuka har muka isa wata unguwa da tun daga bakin gate naga an rubuta Maitama. Duk yawace-yawacena ban taba biyowa ta nan wajajen ba. Daga gani babu tambaya unguwa ce ta masu hannu da shuni, tun daga kan ginunnukan da kuma tsari da yanayin unguwar. Ba karamin burgeni tayi ba.
Yaya ya tsaya a kofar wani madaidaicin gida, yayi amfani da remote, gate din gidan daya kasance ruwan zuma mai cizawa, da wata irin raga-raga daga tsakiya wadda take baka damar hango tanfatsetsen ginin dake ciki, ya bude da kanshi. Yaya Bilal ya silala kan motar ta shiga ciki, muna shiga gate din gidan ya koma ya rufe.
Wajen ajiye motoci muka fara tararwa, waje na mai fadi da zai cinye motoci akalla guda biyar. Yayi parking din motar, muka fito muna karewa gidan kallo. Motoci biyu ne a garejin, rufe da tampol dinsu. Ya mana jagora zuwa gidan. Daga gefen garejin akwai karamin waje da aka yi shuke-shuken bishiyoyi da furanni da basu fara tsayi ba, da alamu sabon garden ne aka yi. Sai kuwa kofar gidan, kana shiga dogon corridor ne da zai kaika har tsakiyar wani babban falo, kana shiga corridor din zaka ci karo da wata kofa da zata sadaka da kicin.
Babban falon ya dauki saitin royal setting, daga kan kujeru, carpet, labulaye, da fenti, duk golden ne da ratsin royal blue. A cikin babban falon dinning room yake, sai kuwa kicin da kofar su daya da dinning room din, sai babban store.
Kana fita daga babban falon anan dakunan mu suke, suma dai tubarkallah manya ne, daya yana kallon daya, inda nan ne ya nunawa Raheemah daya a matsayin nata, dayan kuma a matsayin na Ameerah da bamu gani ba, kila ita sai anjima ko kuma washegari. Daga gaban nasu kadan nan nawa dakin yake, daga gefen nawa kuma akwai dakuna guda biyu, babu komi a ciki daga carpet sai katifa da labulaye, kila dakin baki ne ko kuma na yara. Daga nan ya jamu, muka bi ta gefen dakunan zuwa master bedroom, inda dakinshi yake. Shima dakine babba mai fadi sosai. Daga dakin nashi muka sake fita zuwa wani falon da bai kai wancan girma ba, shima dai saitin kujeru ne da madaidaiciyar tv, sai tagogin wajen da suka kasance manya, irin daga sama zuwa kasa dinnan na gilasai, kana hango karamin lambun daga nan. Wajen dai ya hadu kwarai, just spectacular. Da ya bude wata kofa daga nan falon, sai muka sake bayyana a babban falo.
Bayan ya gama nuna mana gida da kuma ko'ina da ko'ina dai, sai duk muka wuce dakunanmu domin yin sallah da aka fara kira.