Sashe 13
A Zato Na Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ina zaune a inda suka barni ina wasa da kan wayata ta dawo, tace "bari in shirya sai mu fita ko? Abincin sai mu tafi dashi gidan Yaseerah mu ci".
Na gyada kai, "haka za ayi".
Ta shige can kuryar daki ni kuma na cigaba da danne-danne na har ta fito sanye da riga da zani na atamfa, hannunta rike da jaka da hijabi. Na bita da kallo kafin inyi sequeling na fara tsalle akan kujera, "ke matar Yaya sai kice kin kusa sauke mana baby!".
Tayi sauri ta ja rigarta kasa tana hararata kasa-kasa, "ni kada ki min ihu anan. Don mayuntaka har kin hango abinda ko wata uku bai rufa ba!".
Na daga mata gira ina dariya, "haba mata, kada kiyi underestimating dina ta wannan fannin!".
Ta shafa cikin tana dan murmushi, "ku dai taya mu da addu'a dai kawai, Allah yasa mai tsayawa ne".
Murmushin tsokanar kan fuskata ya dusashe, sau biyu tana yin barin ciki, likitoci sun ce mahaifarta bata da karfin da zata dauki ciki ne, saboda haka aka mata daurin mahaifa.
Na dafa kafadarta ina murmushi reassuringly, nace "da yardar Allah babu abinda zai faru, zaki haifo mana babynmu lafiya lau, in samu takwara!".
Hakan yasa ta saki dariya a tausashe, ni kuma nayi murmushi, tace "muje, Yaseerah har ta fara danno min flashing".
Nayi dariya tare da ciccibar kwandon da ta saka abincin data ajiye mana, muka fita.
Yaseerah diyar Baba Adama kanwar Mama ce. Su hudu ne a wajen su Bako duka mata, Inna Talatu ita ce ta farko, tana aure a Damaturu, sai Mama na, Iya Lami da Adama, su duka suna nan Gashua ne. Yaseerah, ni, Sailuba, Ma'u kanwar Sailuba da Lawisa kanwar Yaseerah duk tare muka taso dasu, kusan duk sa'annin juna ne mu. Yaseerah a shekara daya aka aurar dasu ita da Sailuba. Yanzu har tana da yar diyarta Hafsat.
Gidan Yaseerah muka fara zuwa, a shirye muka sameta tsaf tana jiranmu. Bayan mun gaisa da yin yar hirar yaushe gamo, muka ci abinci, daga nan muka fita.
Gidan Iya Lami dake nan unguwar su Yaseerah muka fara shiga muka gaidata. Daga can muka biya gidan Marigayi Malam Mati muka yi gaisuwa.
Yinin ranar dai a haka muka gama shi. Shiga nan fita can, sai wajen karfe biyar muka koma gidan Sailuba.
Yaseerah da Ma'u suka koma gidanta, ni na tsaya wajen Sailuba. Sai da na taya ta tayi girkin abincin dare, sannan na mata sallama na tafi, lokacin har an gama sallar magriba.
Nayi sallama na shiga dakin Fatsu. Tana zaune akan abin sallah tana lazumi a tsakiyar daki, ta bini da kallo lokacin da nake ajiye hijabin dana cire akan gado.
Tace "wato Na'ilah kina nan da yawon nan naki ko? Yanzu saboda Allah ace kin fita tunda sanyin safiya amma sai yanzu zamu ganki? Saboda kin raina mu ne ko me? Idan a gaban mahaifinki kike kina wannan yawace-yawacen ne na babu gaira babu dalili?".
Nace "haba Fatsu, ya zaki ce wai ina yawo? Ziyarar yan'uwa ce fa nayi, zumunci. Kuma a gida yawon me zanyi? Bani da kowa acan sai nan din dai, kin san haka".
Tace "ai sai kiyi tayi, tunda bakinki bai iya bada hakuri ba balle ya iya amsa laifin da yayi!".
Na koma gefenta na zauna ina yar dariya, "to naji Fatsu na, Allah ya baki hakuri, na tuba na bi Allah na bi ki. In Allah ya yarda gobe babu inda zan je, a kugunki zan wuni. Kinji dadi?".
Ta dan harareni cikin wasa, gefe daya kuma tana kokarin danne murmushin da take yi, tace "Allah yasa, kullum ke dama maganar ki daya, amma baki cikawa!".
Nace "in Allah ya yarda wannan karon da gaske nake, I'll be all yours gobe!".
Kamar yadda nayi alkawari, washegari a gidan na yini, ko nan da kofar gida ban leka ba. Da yake ba wasu ayyuka muka yi a gidan ba, na shiga dakin Malam na fiddo kayan ciki gabadaya na sharo dakin tas, na maida na sake mishi wani sabon shirin.
Da yamma bayan nayi wanka, na dauko littafaina da textbooks dana taho dasu ina bita. Nasan cewa nan da sati daya ne zasu fara zancen mu koma makaranta. Bana bari koda wasa in shantake a gida idan naje hutu, ina da lokuta na musamman da nake warewa, lokaci zuwa lokaci na kan dauko littafaina inyi bita musamman akan courses din da zamu yi a semester ta gaba ko kuma wadda muke cikin yi.
Da dare bayan isha'i muna zaune akan tabarma a tsakar gida. Bura-busko muka ci, (tuwon biski/tuwon tsakin masara ko na gero), wannan karon na masara ne muka yi, da miyar kuka da man shanu. Kamshin tuwon ma kadai ya isa yasa yawun mutum tsinkewa balle dadin da yayi. Malam yayi baki, tare suka ci abincin shi da bakin a dakin soro inda ya saba ajiye baki na nesa.
Bayan mun gama cin abincin, na koma na zauna ina taya Fatsu hade kayan sakar da tayi da zare, kasancewar babu wutar lantarki, hasken farin wata ne tar ya mamaye kafatanin tsakiyar gidan, sai kuma hasken wutar candle dana kunna daya kara taimakawa wajen kara haskake wajen.
Ita tana gaban murhu tana zubawa almajirai abinci. Malam ya dauki nauyin ciyar da kananan almajirai wadanda karfinsu bai gama kaiwa ba. Yanzu ya daina karbar almajirai na nesa ma, sai wadanda suke cikin Yobe kawai, kuma garinsu bai yi nisa ba.
Manyan tsofin almajiranshi kuwa tuni ya yaye su, wasu sun koma garuruwansu. Yayin da wasu suna nan cikin Gashua, wasu sunyi aure, wasu suna sana'o'insu, su da garuruwansu sai dai ziyara.
Da ta gama zuba musu, ta dawo gefena ta zauna muka cigaba da yin aikin tare.
Wani almajiri yayi sallama ya shigo, duk muka amsa mishi. Ya durkusa a gefen Fatsu, yace "wai ance ana sallama da Na'ilah a waje!".
Nayi kasake da zare a hannu ina kallon yaron baki a dage, wa na sani da zai yi sallama dani a garin Gashua ne? Inna ce ta tambayeshi inji wa? Yace "yace wai ace Magaji ne".
Sai lokacin naji na sauke ajiyar zuciyar da ban san dalilinta ba, nace "kace mishi ina zuwa".
Bayan fitarshi Fatsu ta kalleni cikin yin kasa da idanu, murya cike da gargadi tace "kinsan dai Yayanki ba zai ji dadin wannan magana ba ko?".
Na kada idanu, "gaisawa ce fa kawai ba wani abu ba. Beside, babu wata magana a tsakanina da Magaji sai zumunci kawai da girmama juna".
Tace "ai shikenan!". Hijabina na saka na fita.
Magaji kusan zan iya cewa abokin Yaya ne, duk da dai ba aboki bane na kut-da-kut, they were more like classmates. Shekaru kusan uku da suka wuce ya nuna yana da sha'awar aurena, tun ma kafin mu hadu da Umar. Na sanar dashi ban shirya yin wani relationship ba a lokacin, yace ya yarda zai jira ni. Ni dai na fito fili na sanar dashi cewa bani da ra'ayin yin wata alaka data wuce ta mutunci dashi, yace babu laifi, ya amince. Amma lokaci zuwa lokaci ya kan yi min tuni, ko kuma nuna alamun har yanzu fa yana so na, ni kam sai dai in banzatar da maganar kawai.
Yanzu ma gaisawa kawai muka yi, ya sanar dani dama wucewa yazo yi, da yake jiya ya ga wucewar mu ta kofar shagon dinkinshi, shine yace bari yazo ya min barka da zuwa.
Muna tsaye anan Yaya yazo wucewa, na dan duka ina gaida shi, hararar daya daka min kadai tasa naji diyan cikina suna kadawa. Ya ba Magaji hannu suka gaisa yana ta wani basarwa, ya shige cikin gida.
Yana bada baya Magaji ya dube ni yana dan yin murmushi, "to ranki ya dade, bari in koma shago, sai wani lokaci kuma".
Na gyada kai, "to Magaji, na gode". Na shige ciki, shi kuma ya wuce.
Ina yin sallama a gidan, Yaya ya taro ni da fada, "wato Na'ilah kunnen kashi ne dake ko? Sau nawa ina fada miki na hana ki tsayawa da Magajin wannan?".
Nace "ni fa Yaya babu abinda yake tsakaninmu dashi sai mutunci kawai, zuwa ne yayi mu gaisa fa ba wani abu ba!".
Murya cikin fada yace "koma menene, na fada miki na hana. Kuma wannan shine gargadi na karshe da zan miki akan wannan maganar, idan na kara ganinki dashi a tsaye, kinsan hakan ba zai miki dadi ba. Kina ji na?!". Ya shura kafa ya bar gidan tun kafin in ce mishi wani abu.
Na turo baki ina satar kallon Fatsu da take sakar ta kamar bata san abinda yake faruwa ba. Na kara turo baki na wuce daki ina dira kafa.
Washegari a Damaturu na wuni gidan Inna Talatu. Da yamma Hafiz, babban danta namiji ya biyo ni muka dawo gida. Sana'o'in shi yake yi a garin Gashua da sauran kananun garuruwa da kauyuka dake makwaftaka da Gashua.
*
Kwanaki bakwai nayi a Gashua ina shan hutu na. Da za'a tambayeni menene ainihin ma'anar hutu? To ni zan ce hutu a gaban Fatsu da Yaya ne hutu.
Nan kadai ne zan yi rayuwata yadda naga dama ba tare da an juya ni ba. Babu abinda yake burgeni da zama a Gashua sai gani na tare, kuma lullube da dangi, duk inda na juya sune. Babu ranar banza da wani nawa ba zai yi sallama ya shigo gidan Bako ba, ko kuma ni ban je naga wani nawa ba. Wannan kadai, ni abin dadi ne a gareni. Ina son dangina, musamman fannin Mama.
Dangin Babana da yake suna da rufin asirinsu daidai misali, kuma da yake babu wasu na kusa, daga diyan kawunnai sai kannen kakanni. Idan kaje gidajensu sai su yi ta wani daga hanci suna shan mur, ko suna zaton rokonsu kaje yi ne? Shi yasa wasu lokutan idan naje Gashua bai fi in leka su sau daya ba, sai dai ko idan biki ake yi ko wata hidimar.
Na gyada kai, "haka za ayi".
Ta shige can kuryar daki ni kuma na cigaba da danne-danne na har ta fito sanye da riga da zani na atamfa, hannunta rike da jaka da hijabi. Na bita da kallo kafin inyi sequeling na fara tsalle akan kujera, "ke matar Yaya sai kice kin kusa sauke mana baby!".
Tayi sauri ta ja rigarta kasa tana hararata kasa-kasa, "ni kada ki min ihu anan. Don mayuntaka har kin hango abinda ko wata uku bai rufa ba!".
Na daga mata gira ina dariya, "haba mata, kada kiyi underestimating dina ta wannan fannin!".
Ta shafa cikin tana dan murmushi, "ku dai taya mu da addu'a dai kawai, Allah yasa mai tsayawa ne".
Murmushin tsokanar kan fuskata ya dusashe, sau biyu tana yin barin ciki, likitoci sun ce mahaifarta bata da karfin da zata dauki ciki ne, saboda haka aka mata daurin mahaifa.
Na dafa kafadarta ina murmushi reassuringly, nace "da yardar Allah babu abinda zai faru, zaki haifo mana babynmu lafiya lau, in samu takwara!".
Hakan yasa ta saki dariya a tausashe, ni kuma nayi murmushi, tace "muje, Yaseerah har ta fara danno min flashing".
Nayi dariya tare da ciccibar kwandon da ta saka abincin data ajiye mana, muka fita.
Yaseerah diyar Baba Adama kanwar Mama ce. Su hudu ne a wajen su Bako duka mata, Inna Talatu ita ce ta farko, tana aure a Damaturu, sai Mama na, Iya Lami da Adama, su duka suna nan Gashua ne. Yaseerah, ni, Sailuba, Ma'u kanwar Sailuba da Lawisa kanwar Yaseerah duk tare muka taso dasu, kusan duk sa'annin juna ne mu. Yaseerah a shekara daya aka aurar dasu ita da Sailuba. Yanzu har tana da yar diyarta Hafsat.
Gidan Yaseerah muka fara zuwa, a shirye muka sameta tsaf tana jiranmu. Bayan mun gaisa da yin yar hirar yaushe gamo, muka ci abinci, daga nan muka fita.
Gidan Iya Lami dake nan unguwar su Yaseerah muka fara shiga muka gaidata. Daga can muka biya gidan Marigayi Malam Mati muka yi gaisuwa.
Yinin ranar dai a haka muka gama shi. Shiga nan fita can, sai wajen karfe biyar muka koma gidan Sailuba.
Yaseerah da Ma'u suka koma gidanta, ni na tsaya wajen Sailuba. Sai da na taya ta tayi girkin abincin dare, sannan na mata sallama na tafi, lokacin har an gama sallar magriba.
Nayi sallama na shiga dakin Fatsu. Tana zaune akan abin sallah tana lazumi a tsakiyar daki, ta bini da kallo lokacin da nake ajiye hijabin dana cire akan gado.
Tace "wato Na'ilah kina nan da yawon nan naki ko? Yanzu saboda Allah ace kin fita tunda sanyin safiya amma sai yanzu zamu ganki? Saboda kin raina mu ne ko me? Idan a gaban mahaifinki kike kina wannan yawace-yawacen ne na babu gaira babu dalili?".
Nace "haba Fatsu, ya zaki ce wai ina yawo? Ziyarar yan'uwa ce fa nayi, zumunci. Kuma a gida yawon me zanyi? Bani da kowa acan sai nan din dai, kin san haka".
Tace "ai sai kiyi tayi, tunda bakinki bai iya bada hakuri ba balle ya iya amsa laifin da yayi!".
Na koma gefenta na zauna ina yar dariya, "to naji Fatsu na, Allah ya baki hakuri, na tuba na bi Allah na bi ki. In Allah ya yarda gobe babu inda zan je, a kugunki zan wuni. Kinji dadi?".
Ta dan harareni cikin wasa, gefe daya kuma tana kokarin danne murmushin da take yi, tace "Allah yasa, kullum ke dama maganar ki daya, amma baki cikawa!".
Nace "in Allah ya yarda wannan karon da gaske nake, I'll be all yours gobe!".
Kamar yadda nayi alkawari, washegari a gidan na yini, ko nan da kofar gida ban leka ba. Da yake ba wasu ayyuka muka yi a gidan ba, na shiga dakin Malam na fiddo kayan ciki gabadaya na sharo dakin tas, na maida na sake mishi wani sabon shirin.
Da yamma bayan nayi wanka, na dauko littafaina da textbooks dana taho dasu ina bita. Nasan cewa nan da sati daya ne zasu fara zancen mu koma makaranta. Bana bari koda wasa in shantake a gida idan naje hutu, ina da lokuta na musamman da nake warewa, lokaci zuwa lokaci na kan dauko littafaina inyi bita musamman akan courses din da zamu yi a semester ta gaba ko kuma wadda muke cikin yi.
Da dare bayan isha'i muna zaune akan tabarma a tsakar gida. Bura-busko muka ci, (tuwon biski/tuwon tsakin masara ko na gero), wannan karon na masara ne muka yi, da miyar kuka da man shanu. Kamshin tuwon ma kadai ya isa yasa yawun mutum tsinkewa balle dadin da yayi. Malam yayi baki, tare suka ci abincin shi da bakin a dakin soro inda ya saba ajiye baki na nesa.
Bayan mun gama cin abincin, na koma na zauna ina taya Fatsu hade kayan sakar da tayi da zare, kasancewar babu wutar lantarki, hasken farin wata ne tar ya mamaye kafatanin tsakiyar gidan, sai kuma hasken wutar candle dana kunna daya kara taimakawa wajen kara haskake wajen.
Ita tana gaban murhu tana zubawa almajirai abinci. Malam ya dauki nauyin ciyar da kananan almajirai wadanda karfinsu bai gama kaiwa ba. Yanzu ya daina karbar almajirai na nesa ma, sai wadanda suke cikin Yobe kawai, kuma garinsu bai yi nisa ba.
Manyan tsofin almajiranshi kuwa tuni ya yaye su, wasu sun koma garuruwansu. Yayin da wasu suna nan cikin Gashua, wasu sunyi aure, wasu suna sana'o'insu, su da garuruwansu sai dai ziyara.
Da ta gama zuba musu, ta dawo gefena ta zauna muka cigaba da yin aikin tare.
Wani almajiri yayi sallama ya shigo, duk muka amsa mishi. Ya durkusa a gefen Fatsu, yace "wai ance ana sallama da Na'ilah a waje!".
Nayi kasake da zare a hannu ina kallon yaron baki a dage, wa na sani da zai yi sallama dani a garin Gashua ne? Inna ce ta tambayeshi inji wa? Yace "yace wai ace Magaji ne".
Sai lokacin naji na sauke ajiyar zuciyar da ban san dalilinta ba, nace "kace mishi ina zuwa".
Bayan fitarshi Fatsu ta kalleni cikin yin kasa da idanu, murya cike da gargadi tace "kinsan dai Yayanki ba zai ji dadin wannan magana ba ko?".
Na kada idanu, "gaisawa ce fa kawai ba wani abu ba. Beside, babu wata magana a tsakanina da Magaji sai zumunci kawai da girmama juna".
Tace "ai shikenan!". Hijabina na saka na fita.
Magaji kusan zan iya cewa abokin Yaya ne, duk da dai ba aboki bane na kut-da-kut, they were more like classmates. Shekaru kusan uku da suka wuce ya nuna yana da sha'awar aurena, tun ma kafin mu hadu da Umar. Na sanar dashi ban shirya yin wani relationship ba a lokacin, yace ya yarda zai jira ni. Ni dai na fito fili na sanar dashi cewa bani da ra'ayin yin wata alaka data wuce ta mutunci dashi, yace babu laifi, ya amince. Amma lokaci zuwa lokaci ya kan yi min tuni, ko kuma nuna alamun har yanzu fa yana so na, ni kam sai dai in banzatar da maganar kawai.
Yanzu ma gaisawa kawai muka yi, ya sanar dani dama wucewa yazo yi, da yake jiya ya ga wucewar mu ta kofar shagon dinkinshi, shine yace bari yazo ya min barka da zuwa.
Muna tsaye anan Yaya yazo wucewa, na dan duka ina gaida shi, hararar daya daka min kadai tasa naji diyan cikina suna kadawa. Ya ba Magaji hannu suka gaisa yana ta wani basarwa, ya shige cikin gida.
Yana bada baya Magaji ya dube ni yana dan yin murmushi, "to ranki ya dade, bari in koma shago, sai wani lokaci kuma".
Na gyada kai, "to Magaji, na gode". Na shige ciki, shi kuma ya wuce.
Ina yin sallama a gidan, Yaya ya taro ni da fada, "wato Na'ilah kunnen kashi ne dake ko? Sau nawa ina fada miki na hana ki tsayawa da Magajin wannan?".
Nace "ni fa Yaya babu abinda yake tsakaninmu dashi sai mutunci kawai, zuwa ne yayi mu gaisa fa ba wani abu ba!".
Murya cikin fada yace "koma menene, na fada miki na hana. Kuma wannan shine gargadi na karshe da zan miki akan wannan maganar, idan na kara ganinki dashi a tsaye, kinsan hakan ba zai miki dadi ba. Kina ji na?!". Ya shura kafa ya bar gidan tun kafin in ce mishi wani abu.
Na turo baki ina satar kallon Fatsu da take sakar ta kamar bata san abinda yake faruwa ba. Na kara turo baki na wuce daki ina dira kafa.
Washegari a Damaturu na wuni gidan Inna Talatu. Da yamma Hafiz, babban danta namiji ya biyo ni muka dawo gida. Sana'o'in shi yake yi a garin Gashua da sauran kananun garuruwa da kauyuka dake makwaftaka da Gashua.
*
Kwanaki bakwai nayi a Gashua ina shan hutu na. Da za'a tambayeni menene ainihin ma'anar hutu? To ni zan ce hutu a gaban Fatsu da Yaya ne hutu.
Nan kadai ne zan yi rayuwata yadda naga dama ba tare da an juya ni ba. Babu abinda yake burgeni da zama a Gashua sai gani na tare, kuma lullube da dangi, duk inda na juya sune. Babu ranar banza da wani nawa ba zai yi sallama ya shigo gidan Bako ba, ko kuma ni ban je naga wani nawa ba. Wannan kadai, ni abin dadi ne a gareni. Ina son dangina, musamman fannin Mama.
Dangin Babana da yake suna da rufin asirinsu daidai misali, kuma da yake babu wasu na kusa, daga diyan kawunnai sai kannen kakanni. Idan kaje gidajensu sai su yi ta wani daga hanci suna shan mur, ko suna zaton rokonsu kaje yi ne? Shi yasa wasu lokutan idan naje Gashua bai fi in leka su sau daya ba, sai dai ko idan biki ake yi ko wata hidimar.