Sashe 20
A Zato Na Complete Hausa Novel · about 8 min read
Fuskarta bata nuna komi ba, babu mamaki, farinciki ko akasinsa, sai kai kawai data gyada, tace "bari inyi wankan nima, amma ki dai daure ki bude wayarki, ko ba don shi ba saboda mutane masu nemanki. Yaya Mudan ma ya kirani lokacin da kina wanka, shima dai ya nemi wayarki a kashe".
Sai lokacin naji nayi murmushi, nace "wato har yanzu dai Mudan dinnan yana nan ko? Kinsan Yaya ya tsani sunan nan".
Tayi dariya, "ramawa kura aniyarta kenan!". Daga haka ta shige bandaki. Nayi dariya kawai naci gaba da shirina.
Zuwa lokacin dana gama hada komi da zan bukata, Janan ta fito daga wanka itama ta fara shiri. Da wayarta nayi amfani na kira Yaya, yana jin ni ce ya fara zuba min korafin ina na shiga? Excuse din dana bashi shine 'wayar ce babu caji tun jiya'.
Yace "su Malam ne nima suka dameni da kira tun safiyar yau, wai suna ta kiran wayarki su ji in kin sauka lafiya kuma a kashe, shine hankalinsu ya tashi!".
Ni gabadaya na ma manta ban kira su ba a jiyan. Na manta yadda suke ne, musamman idan zanyi tafiya, hankalinsu baya kwanciya sai sunji muryata na tabbatar musu da saukata lafiya sannan.
Nace "afuwan, ka basu hakuri don Allah. Wallahi mantawa nayi ban kira su ba, idan nayi caji zuwa anjima zan kira su".
Yace "to shikenan, Antynki tana gaishe ki", daga nan inda yake ina jiyo sautin muryarta tana kiran sunana, nayi murmushi nace "a gaishe ta itama, sai anjima". Na kashe wayar tare da ajiyeta a gefena.
Ina zaune har Janan ta gama shirinta, ta dauki jaka tana zuba jotters da handouts dake tsakiyar dakin a yashe inda muka barsu jiya da muka gama karatu. Na mike nima ina kara gyara kayan jikina. Muna gamawa muka fita daga dakin, ina kallo tasa key ta rufe dakin ta maida key din cikin jakarta.
Har yanzu falon babu kowa, gabadaya gidan ma shiru kake ji kamar babu masu rai.
Sai da muka fita daga gidan muka dauki hanyar da zata sada mu da babban titi inda zamu hau bus, tace "Yaya sauri yake yi, shi yasa bai tsaya kun gaisa ba, ya bar sakon gaisuwa dai".
Nayi murmushi, "babu damuwa, idan ya dawo zamu gaisa ai in da rabo".
Ta zage zip din bayan jakarta ta ciro dubu biyar, sababbi kar ta miko min, na amsa ina kallonta fuskata cike da alamun tambaya, nace "me zanyi dasu?".
Ta daga kafada, "Yaya yace a baki!".
Na zaro ido, "what?...," a lokaci daya kuma ina mika mata kudin, "A'ah, gaskiya ba zan amsa ba, this is way too much!".
Ta harareni, "sai ki bari in yazo ki maida mishi da hannunki. Kafin kuma ki fara wani tunani, wannan ba wani abu bane. Kamar kudin albashi ne daya saba bamu gabadayanmu har su Haleemo, saboda hidimar makaranta da sauransu, kin gane?".
Na karkata hankalina gabadaya na maida kanta, "duk sati yake baku 5k, kawai saboda hidimar makaranta?".
Ta gyada kai tana kallona, irin ba wani big deal bane a wajenta.
Nayi yar dariya, "Woah, dole a makale a gida aki tafiya, kuma dole ace kwadayi nazo yi ba wani abu ba. Maganar gaskiya though, ba zan iya amsar kudin nan ba gaskiya, kiyi hakuri ki amsa".
Ta fara huro hanci alamun na fara bata haushi, "sai kiyi kuma tunda kin saba, ni na gaya miki sako aka bani na baki, in kinga dama kada kiyi amfani dasu, ki jira har sai Yaya ya dawo sai ki maida mishi ki gani idan amsa zai yi!".
Na dan dakata da tafiyar da nake yi, "meye abin fushi kuma anan Jan?".
Tace "ke din ce ai idan ba gani kika yi ana miki wuta ba, baki cika fahimtar abu ba".
Nace "to naji, na karba, kuma na gode, Allah ya saka da alkahiri".
Ta harareni cikin wasa, "abinda yakamata ki ce tun dazu kenan, ba ki tsaya neman magana ba!".
Nayi dariya kawai jin abinda tace. Muka cigaba da takawa har muka fita bakin titi. Shatar keke-napep kawai muka yi saboda lokaci daya fara kurewa.
Allah ya taimaka muka isa akan lokaci. Kasancewar duk practicals ne muka yi, kuma abubuwa basu fara yin nisa ba, yasa bamu jima ba muka taho gida. Karfe biyu ma bata karasa ba muka dawo.
Wannan karon ma napep muka hau. Muna sauka, wata hadaddiyar Range Rover tana shiga gidan. Muka bita a baya muma muka shiga gidan. Ganin ta gangara can bangaren Yaya Jameel, yasa na kalli Janan, "Anty Sarah ta sake mota kenan?".
Tace "da alama, ko kuma ta gidansu ce. Tunda ko yau da safe motar bata nan".
Wadda muke maganar a kanta ta bude gidan gaba ta fito. Matar Yaya Jameel ce. Saratu da muke kira, ko ince ake kira da Sarah, cikakkiyar yar gayu ce, wadda tasan fashion, kodayake kamar akan abinda naji ance tayi karatu kenan, ko kuma dai wani abu mai kama da hakan. Daga yanayin yadda take shigarta, takunta da gudanar da al'amuran rayuwarta, zaka tabbatar da cewa wayayyiyar mace ce, wadda ilimin boko ya ratsa ta. Gidansu gabadayansu yan boko ne. Kai ita kanta a kasar Germany naji ance taje ta hado degree dinta. Matsalarta daya, rashin shiga mutane. Zaku iya kwashe sati cikakke baku hadu da junanku ba, ni da yake dama ba zuwa gidan nake yi sosai ba, zan iya cewa na kwashe watanni fiye da biyar ban ganta ba.
Muka karasa wajen da take, daidai lokacin da diyarsu mai kimanin shekaru biyar, Ruqayyah wadda suke kira Mimah, ta fito daga daya gefen mai zaman banza dauke da jakarta da lunch box.
A lokaci daya muka gaidata ni da Janan, ta amsa tana kama hannun Mimah da take kokarin isowa gareme, jininmu ya hadu da ita sosai. Halin mahaifiyarta na shiga part dinta ta rufe ta kuma hanata fitowa yasa bamu haduwa da ita sosai, sai lokaci zuwa lokaci.
Tana gamawa amsawa ta latsa key tasa motarta a lock, taja hannun diyarta suka tafi.
Duk da haka sai da Mimah ta juyo tana daga mana hannu, mu duka muka daga mata hannun muna murmushi har suka shige part dinsu, ta rufo. Ni da Janan muka kalli juna muka sake yin murmushi, kafin muma muka shige nasu part din.
Adi, da Haleemo suna kicin lokacin da muka shiga, Raheemah kuma tana zaune tana sana'ar kallo, ban san ina Salama ta shiga ba tunda bamu ganta ba. Mu dai muka musu sannu, muka shige daki ba tare da mun damu da kallon banza da aka bimu dashi ba.
Bayan la'asar muka fita waje ni da Janan muka sayo fruits a bakin titi. Muka zo muka hada fruits salad da kayan shan ruwa. Muna cikin soya yam balls, Salama ta shigo kicin din. Babu wanda ta yiwa ko sannu a cikinmu, ta dauki plate kawai sai ganin tana zuba yam balls din a plate din muka yi. Ta debi iya wanda zata dauka, ta fita daga kicin din. Duk kallo muka bita dashi har ta fita. Maimakon abin ya bani haushi, sai ya ma bani dariya. Na girgiza kai kawai, a zuciyata ina furta 'Allah ya kyauta!'.
Sai bayan mun sha ruwa sannan na kunna wayata. Messages, missed calls, voice mails, messages din whatsapp da voice notes babu iyaka daga Umar, duk abu daya yake tambaya, 'don Allah in daga wayata', na harari wayar tawa kamar shine a gabana, in daga wayata in ce mishi me?!
*☆⋆09⋆☆*
Har washegari Umar bai daina kiran wayata ba, nima kuma ban daga ba. Zuwa lokacin missed calls dinshi sun fi a kirga.
Da safe ina browsing din wasu procedures a wayata lokacin da nake jiran Jan ta fito daga wanka, don na rigata shiryawa. Wata bakuwar lamba ta min sallama ta whatsapp. Daga farko nayi zaton ko Umar ne, sai dana bi ta cikin description dinshi sannan naga kwata-kwata komi nashi bai yi shige da na Umar ba. Na farko dai Umar daya zauna ya zubo miki layi biyu a rubuce, ya gwammace kuyi awa biyu akan waya kuna hira. Shi yasa yanzun haka voice notes dinshi ne suka cika min waya.
Kamar wanda yake jira, ina amsawa ana maido da amsar ya nake? Fatan na tashi lafiya?.
Nace lafiya lau, ko wanene yake magana?
Sai aka turo, 'ba lallai ki sanni ba gaskiya, amma ni na sanki farin sani. Ba tun yau ba nake ta so in miki magana, sai yau Allah ya yarda. Sunana Muhammad'.
Na rubuta, 'to Malam Muhammad ko zaka iya sanar dani inda ka sanni? Don bana tunanin nasan wani Muhammad anan inda nake'.
Yace 'in shaa Allah zaki sanni nan ba da jimawa ba, na miki wannan alkawarin. Magana ta gaskiya yanzu bana gari shi yasa, amma da zarar na shigo zan zo in same ki, nasan lokacin kuna shika'.
Na daga gira cikin mamaki, ta alama mutumin nan ya sanni fiye da yadda nayi tsammani. Nace 'ta yaya aka yi kasan haka?', ina tura mishi amsar Jan tana fitowa daga bandaki, na kashe datar na sauka daga kan WhatsApp din ina kallonta. Zama tayi ta gama shirinta a nutse. Tana gamawa muka ci pancake da muka yi da ruwan shayi, da muka gama muka dauki sauran da muka yi muka kai kicin muka wuce.
*
Yau sai yamma likis muka dawo daga asibitin. Da yake yau a bakin titi muka sauka, akan kafafunmu muka gangaro zuwa gidan Yaya.
A kofar gidan, Umar ne tsaye ya jingina da motar shi. Na danyi turus da ganinshi, gabana yana faduwa, kafin na dake muka cigaba da tafiya.
Da sauri ya tari gabanmu, "Na'ilah, sweetie, don Allah ki dakata, don Allah ki saurareni, wallahi na tuba, don Allah....".
Jan ta kalleni, yadda na hade fuska kamar naga wani dan aiken mutuwata, yasa ta fara raba idanu tsakanina da Umar. Yaci gaba da zuba magiya yayin da na zagaya ta gefenshi na tunkari kofar gidan gadan-gadan. Janan ta riko hannuna, na juya ina kallonta, tace "meye haka Na'ilah? Ban san ki da wulakanta mutane ba sam".
Nace "kiyi shiru Janan, baki san abinda ya faru ba, don haka kada kiyi kokarin shiga cikin wannan fadan".
Umar yayi tsulum da bakinshi, "don Allah ki saurareni Sweetie, please...".
Sai lokacin naji nayi murmushi, nace "wato har yanzu dai Mudan dinnan yana nan ko? Kinsan Yaya ya tsani sunan nan".
Tayi dariya, "ramawa kura aniyarta kenan!". Daga haka ta shige bandaki. Nayi dariya kawai naci gaba da shirina.
Zuwa lokacin dana gama hada komi da zan bukata, Janan ta fito daga wanka itama ta fara shiri. Da wayarta nayi amfani na kira Yaya, yana jin ni ce ya fara zuba min korafin ina na shiga? Excuse din dana bashi shine 'wayar ce babu caji tun jiya'.
Yace "su Malam ne nima suka dameni da kira tun safiyar yau, wai suna ta kiran wayarki su ji in kin sauka lafiya kuma a kashe, shine hankalinsu ya tashi!".
Ni gabadaya na ma manta ban kira su ba a jiyan. Na manta yadda suke ne, musamman idan zanyi tafiya, hankalinsu baya kwanciya sai sunji muryata na tabbatar musu da saukata lafiya sannan.
Nace "afuwan, ka basu hakuri don Allah. Wallahi mantawa nayi ban kira su ba, idan nayi caji zuwa anjima zan kira su".
Yace "to shikenan, Antynki tana gaishe ki", daga nan inda yake ina jiyo sautin muryarta tana kiran sunana, nayi murmushi nace "a gaishe ta itama, sai anjima". Na kashe wayar tare da ajiyeta a gefena.
Ina zaune har Janan ta gama shirinta, ta dauki jaka tana zuba jotters da handouts dake tsakiyar dakin a yashe inda muka barsu jiya da muka gama karatu. Na mike nima ina kara gyara kayan jikina. Muna gamawa muka fita daga dakin, ina kallo tasa key ta rufe dakin ta maida key din cikin jakarta.
Har yanzu falon babu kowa, gabadaya gidan ma shiru kake ji kamar babu masu rai.
Sai da muka fita daga gidan muka dauki hanyar da zata sada mu da babban titi inda zamu hau bus, tace "Yaya sauri yake yi, shi yasa bai tsaya kun gaisa ba, ya bar sakon gaisuwa dai".
Nayi murmushi, "babu damuwa, idan ya dawo zamu gaisa ai in da rabo".
Ta zage zip din bayan jakarta ta ciro dubu biyar, sababbi kar ta miko min, na amsa ina kallonta fuskata cike da alamun tambaya, nace "me zanyi dasu?".
Ta daga kafada, "Yaya yace a baki!".
Na zaro ido, "what?...," a lokaci daya kuma ina mika mata kudin, "A'ah, gaskiya ba zan amsa ba, this is way too much!".
Ta harareni, "sai ki bari in yazo ki maida mishi da hannunki. Kafin kuma ki fara wani tunani, wannan ba wani abu bane. Kamar kudin albashi ne daya saba bamu gabadayanmu har su Haleemo, saboda hidimar makaranta da sauransu, kin gane?".
Na karkata hankalina gabadaya na maida kanta, "duk sati yake baku 5k, kawai saboda hidimar makaranta?".
Ta gyada kai tana kallona, irin ba wani big deal bane a wajenta.
Nayi yar dariya, "Woah, dole a makale a gida aki tafiya, kuma dole ace kwadayi nazo yi ba wani abu ba. Maganar gaskiya though, ba zan iya amsar kudin nan ba gaskiya, kiyi hakuri ki amsa".
Ta fara huro hanci alamun na fara bata haushi, "sai kiyi kuma tunda kin saba, ni na gaya miki sako aka bani na baki, in kinga dama kada kiyi amfani dasu, ki jira har sai Yaya ya dawo sai ki maida mishi ki gani idan amsa zai yi!".
Na dan dakata da tafiyar da nake yi, "meye abin fushi kuma anan Jan?".
Tace "ke din ce ai idan ba gani kika yi ana miki wuta ba, baki cika fahimtar abu ba".
Nace "to naji, na karba, kuma na gode, Allah ya saka da alkahiri".
Ta harareni cikin wasa, "abinda yakamata ki ce tun dazu kenan, ba ki tsaya neman magana ba!".
Nayi dariya kawai jin abinda tace. Muka cigaba da takawa har muka fita bakin titi. Shatar keke-napep kawai muka yi saboda lokaci daya fara kurewa.
Allah ya taimaka muka isa akan lokaci. Kasancewar duk practicals ne muka yi, kuma abubuwa basu fara yin nisa ba, yasa bamu jima ba muka taho gida. Karfe biyu ma bata karasa ba muka dawo.
Wannan karon ma napep muka hau. Muna sauka, wata hadaddiyar Range Rover tana shiga gidan. Muka bita a baya muma muka shiga gidan. Ganin ta gangara can bangaren Yaya Jameel, yasa na kalli Janan, "Anty Sarah ta sake mota kenan?".
Tace "da alama, ko kuma ta gidansu ce. Tunda ko yau da safe motar bata nan".
Wadda muke maganar a kanta ta bude gidan gaba ta fito. Matar Yaya Jameel ce. Saratu da muke kira, ko ince ake kira da Sarah, cikakkiyar yar gayu ce, wadda tasan fashion, kodayake kamar akan abinda naji ance tayi karatu kenan, ko kuma dai wani abu mai kama da hakan. Daga yanayin yadda take shigarta, takunta da gudanar da al'amuran rayuwarta, zaka tabbatar da cewa wayayyiyar mace ce, wadda ilimin boko ya ratsa ta. Gidansu gabadayansu yan boko ne. Kai ita kanta a kasar Germany naji ance taje ta hado degree dinta. Matsalarta daya, rashin shiga mutane. Zaku iya kwashe sati cikakke baku hadu da junanku ba, ni da yake dama ba zuwa gidan nake yi sosai ba, zan iya cewa na kwashe watanni fiye da biyar ban ganta ba.
Muka karasa wajen da take, daidai lokacin da diyarsu mai kimanin shekaru biyar, Ruqayyah wadda suke kira Mimah, ta fito daga daya gefen mai zaman banza dauke da jakarta da lunch box.
A lokaci daya muka gaidata ni da Janan, ta amsa tana kama hannun Mimah da take kokarin isowa gareme, jininmu ya hadu da ita sosai. Halin mahaifiyarta na shiga part dinta ta rufe ta kuma hanata fitowa yasa bamu haduwa da ita sosai, sai lokaci zuwa lokaci.
Tana gamawa amsawa ta latsa key tasa motarta a lock, taja hannun diyarta suka tafi.
Duk da haka sai da Mimah ta juyo tana daga mana hannu, mu duka muka daga mata hannun muna murmushi har suka shige part dinsu, ta rufo. Ni da Janan muka kalli juna muka sake yin murmushi, kafin muma muka shige nasu part din.
Adi, da Haleemo suna kicin lokacin da muka shiga, Raheemah kuma tana zaune tana sana'ar kallo, ban san ina Salama ta shiga ba tunda bamu ganta ba. Mu dai muka musu sannu, muka shige daki ba tare da mun damu da kallon banza da aka bimu dashi ba.
Bayan la'asar muka fita waje ni da Janan muka sayo fruits a bakin titi. Muka zo muka hada fruits salad da kayan shan ruwa. Muna cikin soya yam balls, Salama ta shigo kicin din. Babu wanda ta yiwa ko sannu a cikinmu, ta dauki plate kawai sai ganin tana zuba yam balls din a plate din muka yi. Ta debi iya wanda zata dauka, ta fita daga kicin din. Duk kallo muka bita dashi har ta fita. Maimakon abin ya bani haushi, sai ya ma bani dariya. Na girgiza kai kawai, a zuciyata ina furta 'Allah ya kyauta!'.
Sai bayan mun sha ruwa sannan na kunna wayata. Messages, missed calls, voice mails, messages din whatsapp da voice notes babu iyaka daga Umar, duk abu daya yake tambaya, 'don Allah in daga wayata', na harari wayar tawa kamar shine a gabana, in daga wayata in ce mishi me?!
*☆⋆09⋆☆*
Har washegari Umar bai daina kiran wayata ba, nima kuma ban daga ba. Zuwa lokacin missed calls dinshi sun fi a kirga.
Da safe ina browsing din wasu procedures a wayata lokacin da nake jiran Jan ta fito daga wanka, don na rigata shiryawa. Wata bakuwar lamba ta min sallama ta whatsapp. Daga farko nayi zaton ko Umar ne, sai dana bi ta cikin description dinshi sannan naga kwata-kwata komi nashi bai yi shige da na Umar ba. Na farko dai Umar daya zauna ya zubo miki layi biyu a rubuce, ya gwammace kuyi awa biyu akan waya kuna hira. Shi yasa yanzun haka voice notes dinshi ne suka cika min waya.
Kamar wanda yake jira, ina amsawa ana maido da amsar ya nake? Fatan na tashi lafiya?.
Nace lafiya lau, ko wanene yake magana?
Sai aka turo, 'ba lallai ki sanni ba gaskiya, amma ni na sanki farin sani. Ba tun yau ba nake ta so in miki magana, sai yau Allah ya yarda. Sunana Muhammad'.
Na rubuta, 'to Malam Muhammad ko zaka iya sanar dani inda ka sanni? Don bana tunanin nasan wani Muhammad anan inda nake'.
Yace 'in shaa Allah zaki sanni nan ba da jimawa ba, na miki wannan alkawarin. Magana ta gaskiya yanzu bana gari shi yasa, amma da zarar na shigo zan zo in same ki, nasan lokacin kuna shika'.
Na daga gira cikin mamaki, ta alama mutumin nan ya sanni fiye da yadda nayi tsammani. Nace 'ta yaya aka yi kasan haka?', ina tura mishi amsar Jan tana fitowa daga bandaki, na kashe datar na sauka daga kan WhatsApp din ina kallonta. Zama tayi ta gama shirinta a nutse. Tana gamawa muka ci pancake da muka yi da ruwan shayi, da muka gama muka dauki sauran da muka yi muka kai kicin muka wuce.
*
Yau sai yamma likis muka dawo daga asibitin. Da yake yau a bakin titi muka sauka, akan kafafunmu muka gangaro zuwa gidan Yaya.
A kofar gidan, Umar ne tsaye ya jingina da motar shi. Na danyi turus da ganinshi, gabana yana faduwa, kafin na dake muka cigaba da tafiya.
Da sauri ya tari gabanmu, "Na'ilah, sweetie, don Allah ki dakata, don Allah ki saurareni, wallahi na tuba, don Allah....".
Jan ta kalleni, yadda na hade fuska kamar naga wani dan aiken mutuwata, yasa ta fara raba idanu tsakanina da Umar. Yaci gaba da zuba magiya yayin da na zagaya ta gefenshi na tunkari kofar gidan gadan-gadan. Janan ta riko hannuna, na juya ina kallonta, tace "meye haka Na'ilah? Ban san ki da wulakanta mutane ba sam".
Nace "kiyi shiru Janan, baki san abinda ya faru ba, don haka kada kiyi kokarin shiga cikin wannan fadan".
Umar yayi tsulum da bakinshi, "don Allah ki saurareni Sweetie, please...".