← Book details A Zato Na Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 49 OF 95

Sashe 49

A Zato Na Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ba son kai ba, aure nake so inyi mai cike da kwanciyar hankali Janan, ba zan baro masifar kishiya ba, sannan kuma in fada cikin wata wadda ma tafi waccan, kuma ina sane. Idan nayi haka ban yiwa kaina adalci ba. Na fa san komi Janan, ba yau aka auren soyayya ba a gaban idanunmu ba, amma tun kafin aje ko'ina kiga labari ya sha banban. Wannan wadanda ba zaune suke da kishiya bama fa kenan, ina ga wadanda zasu zauna da kishiya? Allah ya gani, so nake in shimfida rayuwar aure mai ma'ana, daga ni sai mijina sai 'ya'yan da zamu haifa. Wannan itace rayuwar dana dinga hangowa kaina Janan, bana kuma tunanin zan iya kauda kai, ina ji ina gani, in kai kaina cikin kabari na!".

Ina dire maganar ta tare ni, "to wa yace miki ba zaki iya irin rayuwar da kike hangowa ba da Yaya Bilal? Kin gwada ne kin gani?".

Nayi dan murmushi cike da kunar zuciya, nace "Janan kenan! Ke baki san kaidi irin na kishiya ba, baki san komi game da sharri da kissa da kisisina irin ta kishiya ba, bana kuma tunanin zaki taba sani. Don haka ki kama bakinki kawai ki ja, ni naga abinda na gani da idanun nan nawa, abinda na gani kuma ba abu bane mai kyau, don haka tarihi fa ba zai maimaita kansa a kaina ba Janan! To dame ma zan ji ne? Da miji zan ji, ko kuwa tashin hankalin kishiya? Barni dai inji da abu daya, hankalina zai fi kwanciya!".

Janan kallona take yi kamar wata sabuwar halitta, nasan yadda na hakikance ne abin yake bata mamaki. Bazan damu ba though, ance wai riga-kafi yafi magani, kuma hanyar lafiya a bita da shekara. Gwanda dai in tsaya kyam akan ra'ayina, idan zuciyata ta fara rawa akan wannan maganar, me zai faru kenan? Na san it's only a matter of time, da zan manta da wani Yaya Bilal. Balle duka mai ya rage mana a Zaria? Yan watanni ne kawai. Idan na samu na lallabi zuciyata, na lallaba na bar Zaria, nasan ikon Allah ne kawai zai sake dawo da ni cikinta. Kenan idan na tafi, ta ina zan ga Yaya balle har wani tunanin zama dashi da masifaffun matanshi ya darsu a cikin raina? Abinda nake bukatar inyi kawai shine in daure, in kuma yi kokarin mantawa dashi.
Sai dai fadar, tafi aikatawar dadin fada.

Janan ta girgiza kanta cikin rashin sanin abin cewa, tace "gaskiya kinyi nisa da yawa, Allah ya ganar dake".
Nima na girgiza mata kaina, nace "ba zaki taba ganewa ba Janan, ba zaki gane ba!".

Bata ce komi ba, ta cigaba da tafiya. Nima na bi bayanta.
Tun daga wannan yar sa'insa da muka yi, babu wanda ya sake tado maganar har lokacin tashinmu yayi. Kai babu ma wata doguwar magana data sake hada mu da ita, naga kamar ma wani haushi na take ji. Ni ma da yake raina a dagule yake, ban wani damu ba. Lokacin tashi yana yi, na bar ward din. Ranar ko sallama bamu yi ba.

Ina komawa daki na dora indomie, ba wata yunwa nake ji ba, amma tunda ranar garin yau ta waye babu komi a cikin cikina sai biskit din pure bliss da hot chocolate. Ina gama dafawa na dora ruwan shayi, na dauki lemun tsami na matse a cikin shayin na juye a cikin mug. Dana gama na daukesu zuwa gefen katifata na ajiye, ni kuma na zauna. Laptop dina na dauka na kunna kallon wani American film, 'Another Cinderella Story' na fara kallo ina kuma cin indomin. Kallo kawai nake yi, amma bana wani fahimtar kallon. Har na gama na kauda kayan, na dawo na cigaba da kallon. Ina nan zaune Esther ta dawo, na mata sannu da zuwa, na maida hankalina kacokam ga film din da nake kallo don bani da kuzarin zama yin hira da ita. To da yake ma ba zama ya kawo ta ba, kayan jikinta kawai ta canza ta sake fita.
Ina cikin yin kallon barci ya kwashe ni.

*☆⋆28⋆☆*

Ban jima da fara barcin ba amma, kiran daya shigo cikin wayata ya katse min shi.
Na zabura na tashi zaune tare da lalubar wayata, duk da kalar ringtone din, hakan bai hana ni kara duba sunan mai kiran ba domin in tabbatar da cewa da gaske ne ba mafarki ba.
Ban san dalilin da yasa na kasa goge lambar Yaya Bilal daga cikin wayata ba, kai ko suna har yanzu ban iya canza mishi ba. Har yau 'Muhammadu na' ne a jiki, shine kuma yake tsalle yana karawa akan screen din wayata.

Duk da tsananin rawar da hannuna yake yi, da yadda zuciyata take bugawa, da yadda nasan bani da abinda zan ce mishi, hakan bai hana ni dagawa ba.
Hatta da muryata rawa take yi lokacin da naji muryarshi tana ratsawa ta cikin dodon kunnena, na amsa cikin sanyin jiki da murya. Yaushe rabon da inji wannan muryar? Ji nake kamar na shekara da shekaru.

Yaya Bilal yace "hmmm, Na'ilah kenan, manyan kasa. Kin gama fushin ne?".
Nace "fushi kuma, fushin me zan yi?".
Yace "nima ban sani ba Na'ilah, kawai dai nasan kina yin fushi. Amma duk ba wannan ba, kina ganin zamu iya magana yanzu? Are you ready for that?". Nayi shiru ina sauraronshi, ina tunanin ya dauki shirun da nayi a matsayin go ahead, don haka ya fara magana.

Yace "ba kya ganin it's high time, mu ajiye duk wasu abubuwan da suka faru a baya a bayanmu mu fuskanci gaba? Bai kamata ace muna ta tsalle-tsalle a waje daya ba kamar kananan yara, please let's do this like the matured people we are!".

Tabdijam! Naji wani kululu ya makale min a makoshi, cikin nuna alamun bacin rai nace "kana nufin kace min ni yarinya ce ko kuma ina dabi'a irin ta yara?".

Yace "ban ce ko daya daga ciki ba, illa iyaka ina so in nuna miki cewa wannan kauce-kauce da kike yi babu abinda zai haddasa mana sai bata lokacinmu da yake yi kawai. Na'ilah, mu fa ba kananan yara bane, bai kamata ace mun dauki magana daya muna ta nanata ba, bayan muna da yadda zamu fuskanci matsalar mu kuma magance ta. Saboda haka yanzu ki fada min, meye matsalar ki game dani? Kin san ina son ki ko?".

Amsar dana bashi ta fito daga cikin bakina tun ma kafin in tauna ta, kai ban ma san na fade ta ba sai dana ji tana ringing a cikin kunnuwana, da kuma shirun daya biyo bayan na furta ta, da alamun shi kanshi bai yi tsammaninta ba; "nima ina sonka!".

Kusan sakanni biyar da fadin hakan, kafin naji yayi gyaran murya, ni kam sai aka barni da kyafta idanu, yace "good. To menene matsalar? Na riga na fada miki idan ta matana ne baki da matsala da su, gidan ki daban zan ware miki, ba lallai sai kun hadu dasu ba. Wannan ganin damar ki ne, idan kin so haduwa dasu sai ki hadu dasu, idan baki so ba, sai kiyi yadda kike so. Bayan wannan kuma sai me? Ban takura ki ba Na'ilah, zan jira ki gama karatunki kafin a tado maganar auren, bayan nan zan bar ki kiyi aikinki, ba zan hana ki ba. Sai me kike bukata kuma?".

Shi a tunaninshi rashin hada mu gida daya kamar wani solution ne, sai dai a nawa tunanin, wannan ba komi bane. Ya hada mu gida daya ko bai hana ba, duk dai yana da mata ne dai, kuma zamu yi sharing dinshi dasu. Na daga baki nace "bani da wata matsala Yaya, kayi hakuri. Nima ba wai ina jindadin wasa da hankalinka da nake yi bane, amma the fact that zan zauna da kishiya daya ma bana so balle kuma har biyu, kayi hakuri don Allah".

Yace "shi kuma son da muke yiwa juna fa? Kin kasa daukar matsaya daya Na'ilah ki zauna a kanta, daga yau kice wannan, sai gobe ki ce wannan. Kina ganin ina da lokacin zama bin kanki ne? I can't leave my work da duk wasu harkokina, ina chasing dinki Na'ilah! I just can't. Don haka idan zaki zauna ki yanke shawarar da zata fisshemu, gwanda ma tun wuri ki yanke. Haba! Na gaji! Na gaji wallahi!! Wai baki da zuciyar tausayi ne? Ko ke baki san kaddara ba ne? Kada ki manta da cewa Annabinmu ma da muke yin koyi da koyarwa shi bai zauna da mata daya ba. Ke a ganinki rashin zama da kishiya zai hana ki rayuwar farinciki a gidan aurenki bane ko me? Kina ina mata da dama suke baro gidan auren nasu babu kishiya ba kome, gasu nan birjik suna yawo akan titi muna ganinsu, amma kuma masu kishiyar suna zaune a nasu gidan salin-alin suna zaman lafiya? Kin kishiya da kike yi kamar izgilanci ne kike yiwa Allah, tunda kin karanta, kin kuma san cewa ba haramun bane a musulunci. Ita kishiyar hauka ce?!".

Yadda ya hakikance yana fada yasa naji nima raina ya dauko baci, a tunanina idan ba'a lallasheni ba, bai kamata ace za ayi min ihu ba. Nace "da kake maganar kaddara da kuma izgilanci, shi Allah ai baya dorawa rai abinda ba zai iya dauka ba sai dai bawa ya dorawa kanshi. Saboda haka ina ji ina gani ba zan kai kaina wajen wahala ba. Tunda nace ka kyaleni, bana so, ba sai ka kyale ni din ba? Ana dole ne?!!".
Chapter 49 · 0% Book details