Sashe 9
A Babban Gida Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A ɓangaren su Mommah tun shigar Nainarh bedroom nata suka ci gaba da hirarsu. Ammie ce ta ce “To yanzu ke Hajiya Sughrah meye hukuncin da kika yanke kan shi Aliyun?”
Gyara zamanta tayi tace “Ni me na San zan yanke ne? Gabaɗaya kai na ya kulle, na tura masa messages ma Bana tunanin ya gani, na ce masa yayi haƙuri ya dawo gida za'a shawo kan matsalar amma ya ƙi.” ta idasa cikin raunin murya.
“Gaskiya ban ji daɗin abinda ya faru ba, shi ma Aliyu me ya kai shi ga neman ƴar gida a cikin gida?,gashi yanzu ba'a san ma wane hukunci Alhaji Baba zai yanke ba.” Ammie ta faɗa cike da kulawa.
“Abun da na gani kenan Hajiya Saudatu, sai dai wani hanzarin ba gudu ba, tunda yanzu dai muna hasashen irin hukuncin da Alhaji Babba dai yanke, ina laifin kawai mu haɗa aurensa da Kausar idan ya so Kinga dole Alhaji Baba ya dakatar da wannan hukunci!” Mamie ta faɗa tana son ƙara nunawa Mommah muhimmanci wannan shawarar sai dai Ammie ji take kamar ta ƙwale ta don ta mata shigar sauri.
Jimm kaɗan Mommah tayi tana tunanin yadda abun zai kasance, idan har tayi wasa da wannan damar za'a samu matsala, amma wani ɓangare na zuciyarta na nuna mata illar hakan, musamman in ta tuna da halin Mazan nata, sai kuma Wani ɓangare na zuciyarta ta ce mata “Cikin ku waye ya haifi wani ne kam?”
Tabbas dole yanzu ta nunawa Ya Sadauki iyakarsa, babu yadda ya iya, dole ya bi wannan sharaɗin nata, tunda gashi ƙiri da muzu dai so ake kowa ya tsane shi a gidan. Kullum tana da burin sanin waye ke musu wannan Zagon ƙasa (Khadija candy). Har yau har yanzu ma bata gamsu da cewar Ya Sadaukin zai aikata abinda aka tuhume shi a kai ba.
Ganin shirun da Mommah tayi yasa Ammie jin daɗi ganin dai alamar ƙorafin Mami bai karɓu ba. Ɓangaren Mami ma ras gabanta ya buga, fatan ta dai Allah yasa kar ta bayyana hakan gaban Hajiya Saudatu.
“Kinyi shiru Hajiya Sughrah ”
Wata nauyayyar ajiyar zuciya Mommah ta sauƙe tana faɗin “Gaskiya ne Hajiya Baraka, ina ga shawarar ki ta yi, amma kuna tunanin kuwa Sadauki zai amince da wannan haɗi?”
Cike da son ƙarfafa mata guiwa Mami ta ce “Ƙwarai kuwa ai dolensa ya amince Hajiya Sughrah, ke ce uwar ko shi?”
“Ni ce mana”. Mommah ta bata amsa.
“Idan kuwa ta tabbata hakan ban ga abun tashin hankali ba, yanzu dai amincewar ki kawai nake jira.”
Hararar gefen ido Ammie ta jefawa Mami don ji take kamar ta shaƙo wuyanta ko zata huta, sai dai kawai sai ta danne gudun kada a gani wacece ita ɗin “Ki amince kawai Hajiya, in ba haka ba kuma ki shirya haɗa zuri'a da Hajiya Babba, ta ƙara samun damar mallake ko da ɗan naki tare da dukiyarsa fiye da da .” Ammie ta faɗa yayinda zuciyarta ke ƙuna.
Murmushi Mami tayi jin yadda Ammie ta sauƙaƙa mata plan ɗinta. “Ina sauraron ki Hajiya Sughrah ”
Kamar zata yi kuka tace “Babu komai, yanzu dai Allah yasa ya dawo gidan, in ya dawo ko baya so dole ne ya amince da auren nan, don wallahi ban isa ba haɗa zuri'a da dangin Mayu masu mallake zukatan jama'a ba ”
Cike da farin ciki Mami ta ce “Kar ki wani damu Hajiya Sughrah, akwai malamin da yake min addu'a, gobe goben nan zan samu na je wurinsa, cikin kwana uku zaki ga Sadauki ya dawo gida” fuska sake Mommah ta ce “Da kuwa kin samu kyauta mai tsoka matsayin tukuicin ki.”
“Baki da damuwa Hajiya, Ni dai tunda kin amince zan kula da komai.”
Ammie ce ta fara miƙewa da niyyar wucewa, Mani ta ce “Hajiya Saudatu ki ɗan jira Ni don Allah sai mu wuce”
Fuska sake Ammie ta ce “To kin san ina so ne naji yaya akan me suka tattauna yau, fata na Allah yasa ba batun Sadauki bane ”
Ɗan ƙaramin tsaki Nainarh da ta fito daga bedroom ɗinta tayi, steps ɗin takalminta Ammie ta ji hakan yasa ta waiwayo don ganin ko Hajiya Baraka ce. Ganin Nainarh yasa ta washe baki tana faɗin “Nainarh, kin fito gashi zamu wuce, ko zaki biyo NI ki karɓi kunun gyaɗar ne?, na riga na gama Shiyasa amma na ajiye miki sanin yadda kike son abun.”
Fuska sake Nainarh ta ce “Kai Amma na gode sosai , bari kawai na bi ki na karɓo”
“To kiyi sauri.”
Daga nan Nainarh ta bi bayan Ammie zuwa shashen ta.
_Don Allah masoya ayi reacting, masu complain cewa basu ganin update kuyi haƙuri don Allah, zan rage ɗaura abu bayan update saboda kuna gani, idan baku samu ba kuma zaku iya yi min magana na tura muku ta 08143760764. Please ayi reacting sannan a taya Ni sharing, zan ƙara yawan update a rana in har na ga sauyi, at least 100 reactions nake son gani._
_Thanks my esteem fans, Love you loads.._
[11/9, 11:45 AM] Diamond Bhatool💎:
*🏡A BABBAN GIDA🏡*
*TAKUN ƘARSHE*
*©Diamond Bhatool*
*💎💍ELITE DIAMOND WRITERS💍💎*
_Where diamonds shine, words ignite_
*PAGE* 0️⃣7️⃣
﷽
Bayan tafiyar su Nainarh ya rage sai iya zahrah wacce ta lula izuwa duniyar tunani, tabbas yanzu ne zata fara gina rayuwarta, amma kuma matsala ɗaya da ta gagara kawar da ita daga ƙwaƙwalwarta shine rashin Mama. Fatanta kullum Allah ya bayyana ta. A wani ɓari na zuciyarta kuma haka kawai take jin wani baƙon yanayi na ziyartarta tun shigowar ta wannan gida, har ta kai ga ta fara tunanin kamar ƙaddarar rayuwarta na shirin canzawa, sai kuma wani abu da ta lura da shi a ƴar hirar da suka yi da cousins nata, amma sai ta kawar jin abun na shirin kai ta wata duniya ta daban.
*****************
*LONDON*
Alhamdulillah zamu iya cewa don a halin yanzu, jikin Ya Sadauki yayi sauƙi sosai, kulawa kam ya same ta daga Ya Khalil da kuma likitansa DR. Arƙam. Abu ɗaya da har yanzu ya kasa fahimta shine tsawon jinyarsa da Ya Khalil yayi bai taɓa ce masa komai ba, idan ya gama masa abunda ya dace a matsayinsa na majinyaci baya ƙara cewa komai, tun yana sharewa saboda miskilanci irin nasa har ya dawo abun ya fara damunsa don tsawon rayuwarsu hakan bata taɓa faruwa ba, sun tashi ne cike da so da ƙaunar juna duk da cewa babu wata alaƙa mai kyau tsakanin iyayensu mata, a irin hali na Ya Khalil, Ya Sadauki kansa ya san shi ke hakuri da shi.
Ganin ba shi da wata mafita kuma hakan na ƙarawa zuciyarsa nauyi yasa yayi niyyar tunkarar ɗan'uwan nasa ya ji wani irin babban kuskure ya tafka haka ne har ya iya fushi da shi, fushin ma irin wadda bai taɓa yi ba.
Lumshe fararen idanuwansa yayi yana sauƙe wata nauyayyar ajiyar zuciya.
Shigowar Ya Khalil ne yasa ya buɗe lumsassun idanuwansa da sauri yana kai dubansa gare shi, sai dai abunda ya ƙara bashi mamaki shine yadda Ya Khalil ɗin ya kauda kan sa gefe. Kujerar da ce gefensa ya ja zauna fuskar nan tamau kamar an aika masa da labarin mutuwa. Kamar zai bar maganar sai sun koma sai kuma ya daure, a hankali cikin Muryar da ke nuna cewa mallakinta lafiya bata wadace shi ba ya ce “Dude!”.
Ɓangaren Ya Khalil ya ji sarai sai ya ƙara ɗaure fuska ba tare da ya juyo ba. Zuciyar Ya Sadauki ne ta ɗan karye sai kuma ya tsinci kansa da ƙara ƙiran Ya Khalil ɗin. “Dude!” nan ma ya Khalil bai amsa ba. Hakan ya ƙara tabbatarwa Ya Sadauki irin fushin da ɗan'uwansa yayi da shi. Tunanin yadda za'a yi ya sanyaya zuciyarsa yake amma ya rasa. Karo na farko da murmushi ya sauƙa kan kyakkyawar fuskarsa, alamar dai ya tuna da wani abun ne da ya saka shi nishaɗi.
Lokaci ɗaya kuma ya sarƙafe da tari ba ƙaƙƙautawa, a zabure Yaya Khalil ya miƙe ya nufi yadda yake. “Man! Man!!!, lemme call the Dr.” sai ya juya zai fice a rikice. Dakatawa yayi jin an riƙe shi, tuni ya waigo yana duban Ya Sadaukin da yayi kalar ban tausayi da fuskarsa.
Haɗe fuska Ya Khalil yayi kamar ba shi ya gama nuna kulawarsa ga yanayin ɗan'uwan nasa ba. “Ya dai Malam, let go off me!”
A sanyaye Yaya Sadauki ya ce “Why Dude?” ya idasa cike da raunin murya. “Why all these please?, idan ka juya min baya haka ina ganin babu amfanin cigaba da rayuwa ta, kar ka manta kai ɗaya ne bayan Alhaji Baba Ka kasance garkuwa gare Ni, kada ka yi min haka, idan wani abun nayi maka we need to talk, ba wai ka sauya min ba.” dafe kansa yayi yana gama faɗar hakan tare da lumshe idanunsa.
A sanyaye Yaya Khalil ya juyo yana fuskantar ɗan'uwansa cike da so da kulawa tare da tausayawa rayuwarsa, sai kuma ya ji a ransa cewa bai kyauta ba kan abunda ya aikata, he should haven't act in such a way, but it's not too late. Fuska sake ya riƙo hannun Yaya Sadauki tare da haɗe su wuri ɗaya da nasa.
“I'm sorry man!, I shouldn't have not done such, duk irin yadda muka kasance but I can't hold it more Shiyasa nayi fushi da kai, don Allah Man, ka sanyaya ranka, ka ƙara haƙuri da jajircewa, ƙungiyarku na shirin durƙushewa saboda yadda ka raunana, don Allah ka koma Sadaukin da Abatcha Family ke alfahari da shi, kada ka bari maƙiya suyi dariya, ka koma kan aikinka Sannan ka koma ga Ahalinka, a cikinsu akwai waɗanda suke cikin ƙunci da rashin ka, be linient with them please, Ka koma don Allah, na maka alƙawrin kasancewa by your side.”
Shiru ne ya wanzu tsawon wani lokaci kowa da abunda yake saƙawa cikin ransa, Yaya Khalil na addu'ar ubangiji ya bashi sa'ar kwantar da wannan raunananniyar zuciya shi kuma Yaya Sadauki na addu'ar Allah ya sauƙaƙa masa al'amarin.
Gyara zamanta tayi tace “Ni me na San zan yanke ne? Gabaɗaya kai na ya kulle, na tura masa messages ma Bana tunanin ya gani, na ce masa yayi haƙuri ya dawo gida za'a shawo kan matsalar amma ya ƙi.” ta idasa cikin raunin murya.
“Gaskiya ban ji daɗin abinda ya faru ba, shi ma Aliyu me ya kai shi ga neman ƴar gida a cikin gida?,gashi yanzu ba'a san ma wane hukunci Alhaji Baba zai yanke ba.” Ammie ta faɗa cike da kulawa.
“Abun da na gani kenan Hajiya Saudatu, sai dai wani hanzarin ba gudu ba, tunda yanzu dai muna hasashen irin hukuncin da Alhaji Babba dai yanke, ina laifin kawai mu haɗa aurensa da Kausar idan ya so Kinga dole Alhaji Baba ya dakatar da wannan hukunci!” Mamie ta faɗa tana son ƙara nunawa Mommah muhimmanci wannan shawarar sai dai Ammie ji take kamar ta ƙwale ta don ta mata shigar sauri.
Jimm kaɗan Mommah tayi tana tunanin yadda abun zai kasance, idan har tayi wasa da wannan damar za'a samu matsala, amma wani ɓangare na zuciyarta na nuna mata illar hakan, musamman in ta tuna da halin Mazan nata, sai kuma Wani ɓangare na zuciyarta ta ce mata “Cikin ku waye ya haifi wani ne kam?”
Tabbas dole yanzu ta nunawa Ya Sadauki iyakarsa, babu yadda ya iya, dole ya bi wannan sharaɗin nata, tunda gashi ƙiri da muzu dai so ake kowa ya tsane shi a gidan. Kullum tana da burin sanin waye ke musu wannan Zagon ƙasa (Khadija candy). Har yau har yanzu ma bata gamsu da cewar Ya Sadaukin zai aikata abinda aka tuhume shi a kai ba.
Ganin shirun da Mommah tayi yasa Ammie jin daɗi ganin dai alamar ƙorafin Mami bai karɓu ba. Ɓangaren Mami ma ras gabanta ya buga, fatan ta dai Allah yasa kar ta bayyana hakan gaban Hajiya Saudatu.
“Kinyi shiru Hajiya Sughrah ”
Wata nauyayyar ajiyar zuciya Mommah ta sauƙe tana faɗin “Gaskiya ne Hajiya Baraka, ina ga shawarar ki ta yi, amma kuna tunanin kuwa Sadauki zai amince da wannan haɗi?”
Cike da son ƙarfafa mata guiwa Mami ta ce “Ƙwarai kuwa ai dolensa ya amince Hajiya Sughrah, ke ce uwar ko shi?”
“Ni ce mana”. Mommah ta bata amsa.
“Idan kuwa ta tabbata hakan ban ga abun tashin hankali ba, yanzu dai amincewar ki kawai nake jira.”
Hararar gefen ido Ammie ta jefawa Mami don ji take kamar ta shaƙo wuyanta ko zata huta, sai dai kawai sai ta danne gudun kada a gani wacece ita ɗin “Ki amince kawai Hajiya, in ba haka ba kuma ki shirya haɗa zuri'a da Hajiya Babba, ta ƙara samun damar mallake ko da ɗan naki tare da dukiyarsa fiye da da .” Ammie ta faɗa yayinda zuciyarta ke ƙuna.
Murmushi Mami tayi jin yadda Ammie ta sauƙaƙa mata plan ɗinta. “Ina sauraron ki Hajiya Sughrah ”
Kamar zata yi kuka tace “Babu komai, yanzu dai Allah yasa ya dawo gidan, in ya dawo ko baya so dole ne ya amince da auren nan, don wallahi ban isa ba haɗa zuri'a da dangin Mayu masu mallake zukatan jama'a ba ”
Cike da farin ciki Mami ta ce “Kar ki wani damu Hajiya Sughrah, akwai malamin da yake min addu'a, gobe goben nan zan samu na je wurinsa, cikin kwana uku zaki ga Sadauki ya dawo gida” fuska sake Mommah ta ce “Da kuwa kin samu kyauta mai tsoka matsayin tukuicin ki.”
“Baki da damuwa Hajiya, Ni dai tunda kin amince zan kula da komai.”
Ammie ce ta fara miƙewa da niyyar wucewa, Mani ta ce “Hajiya Saudatu ki ɗan jira Ni don Allah sai mu wuce”
Fuska sake Ammie ta ce “To kin san ina so ne naji yaya akan me suka tattauna yau, fata na Allah yasa ba batun Sadauki bane ”
Ɗan ƙaramin tsaki Nainarh da ta fito daga bedroom ɗinta tayi, steps ɗin takalminta Ammie ta ji hakan yasa ta waiwayo don ganin ko Hajiya Baraka ce. Ganin Nainarh yasa ta washe baki tana faɗin “Nainarh, kin fito gashi zamu wuce, ko zaki biyo NI ki karɓi kunun gyaɗar ne?, na riga na gama Shiyasa amma na ajiye miki sanin yadda kike son abun.”
Fuska sake Nainarh ta ce “Kai Amma na gode sosai , bari kawai na bi ki na karɓo”
“To kiyi sauri.”
Daga nan Nainarh ta bi bayan Ammie zuwa shashen ta.
_Don Allah masoya ayi reacting, masu complain cewa basu ganin update kuyi haƙuri don Allah, zan rage ɗaura abu bayan update saboda kuna gani, idan baku samu ba kuma zaku iya yi min magana na tura muku ta 08143760764. Please ayi reacting sannan a taya Ni sharing, zan ƙara yawan update a rana in har na ga sauyi, at least 100 reactions nake son gani._
_Thanks my esteem fans, Love you loads.._
[11/9, 11:45 AM] Diamond Bhatool💎:
*🏡A BABBAN GIDA🏡*
*TAKUN ƘARSHE*
*©Diamond Bhatool*
*💎💍ELITE DIAMOND WRITERS💍💎*
_Where diamonds shine, words ignite_
*PAGE* 0️⃣7️⃣
﷽
Bayan tafiyar su Nainarh ya rage sai iya zahrah wacce ta lula izuwa duniyar tunani, tabbas yanzu ne zata fara gina rayuwarta, amma kuma matsala ɗaya da ta gagara kawar da ita daga ƙwaƙwalwarta shine rashin Mama. Fatanta kullum Allah ya bayyana ta. A wani ɓari na zuciyarta kuma haka kawai take jin wani baƙon yanayi na ziyartarta tun shigowar ta wannan gida, har ta kai ga ta fara tunanin kamar ƙaddarar rayuwarta na shirin canzawa, sai kuma wani abu da ta lura da shi a ƴar hirar da suka yi da cousins nata, amma sai ta kawar jin abun na shirin kai ta wata duniya ta daban.
*****************
*LONDON*
Alhamdulillah zamu iya cewa don a halin yanzu, jikin Ya Sadauki yayi sauƙi sosai, kulawa kam ya same ta daga Ya Khalil da kuma likitansa DR. Arƙam. Abu ɗaya da har yanzu ya kasa fahimta shine tsawon jinyarsa da Ya Khalil yayi bai taɓa ce masa komai ba, idan ya gama masa abunda ya dace a matsayinsa na majinyaci baya ƙara cewa komai, tun yana sharewa saboda miskilanci irin nasa har ya dawo abun ya fara damunsa don tsawon rayuwarsu hakan bata taɓa faruwa ba, sun tashi ne cike da so da ƙaunar juna duk da cewa babu wata alaƙa mai kyau tsakanin iyayensu mata, a irin hali na Ya Khalil, Ya Sadauki kansa ya san shi ke hakuri da shi.
Ganin ba shi da wata mafita kuma hakan na ƙarawa zuciyarsa nauyi yasa yayi niyyar tunkarar ɗan'uwan nasa ya ji wani irin babban kuskure ya tafka haka ne har ya iya fushi da shi, fushin ma irin wadda bai taɓa yi ba.
Lumshe fararen idanuwansa yayi yana sauƙe wata nauyayyar ajiyar zuciya.
Shigowar Ya Khalil ne yasa ya buɗe lumsassun idanuwansa da sauri yana kai dubansa gare shi, sai dai abunda ya ƙara bashi mamaki shine yadda Ya Khalil ɗin ya kauda kan sa gefe. Kujerar da ce gefensa ya ja zauna fuskar nan tamau kamar an aika masa da labarin mutuwa. Kamar zai bar maganar sai sun koma sai kuma ya daure, a hankali cikin Muryar da ke nuna cewa mallakinta lafiya bata wadace shi ba ya ce “Dude!”.
Ɓangaren Ya Khalil ya ji sarai sai ya ƙara ɗaure fuska ba tare da ya juyo ba. Zuciyar Ya Sadauki ne ta ɗan karye sai kuma ya tsinci kansa da ƙara ƙiran Ya Khalil ɗin. “Dude!” nan ma ya Khalil bai amsa ba. Hakan ya ƙara tabbatarwa Ya Sadauki irin fushin da ɗan'uwansa yayi da shi. Tunanin yadda za'a yi ya sanyaya zuciyarsa yake amma ya rasa. Karo na farko da murmushi ya sauƙa kan kyakkyawar fuskarsa, alamar dai ya tuna da wani abun ne da ya saka shi nishaɗi.
Lokaci ɗaya kuma ya sarƙafe da tari ba ƙaƙƙautawa, a zabure Yaya Khalil ya miƙe ya nufi yadda yake. “Man! Man!!!, lemme call the Dr.” sai ya juya zai fice a rikice. Dakatawa yayi jin an riƙe shi, tuni ya waigo yana duban Ya Sadaukin da yayi kalar ban tausayi da fuskarsa.
Haɗe fuska Ya Khalil yayi kamar ba shi ya gama nuna kulawarsa ga yanayin ɗan'uwan nasa ba. “Ya dai Malam, let go off me!”
A sanyaye Yaya Sadauki ya ce “Why Dude?” ya idasa cike da raunin murya. “Why all these please?, idan ka juya min baya haka ina ganin babu amfanin cigaba da rayuwa ta, kar ka manta kai ɗaya ne bayan Alhaji Baba Ka kasance garkuwa gare Ni, kada ka yi min haka, idan wani abun nayi maka we need to talk, ba wai ka sauya min ba.” dafe kansa yayi yana gama faɗar hakan tare da lumshe idanunsa.
A sanyaye Yaya Khalil ya juyo yana fuskantar ɗan'uwansa cike da so da kulawa tare da tausayawa rayuwarsa, sai kuma ya ji a ransa cewa bai kyauta ba kan abunda ya aikata, he should haven't act in such a way, but it's not too late. Fuska sake ya riƙo hannun Yaya Sadauki tare da haɗe su wuri ɗaya da nasa.
“I'm sorry man!, I shouldn't have not done such, duk irin yadda muka kasance but I can't hold it more Shiyasa nayi fushi da kai, don Allah Man, ka sanyaya ranka, ka ƙara haƙuri da jajircewa, ƙungiyarku na shirin durƙushewa saboda yadda ka raunana, don Allah ka koma Sadaukin da Abatcha Family ke alfahari da shi, kada ka bari maƙiya suyi dariya, ka koma kan aikinka Sannan ka koma ga Ahalinka, a cikinsu akwai waɗanda suke cikin ƙunci da rashin ka, be linient with them please, Ka koma don Allah, na maka alƙawrin kasancewa by your side.”
Shiru ne ya wanzu tsawon wani lokaci kowa da abunda yake saƙawa cikin ransa, Yaya Khalil na addu'ar ubangiji ya bashi sa'ar kwantar da wannan raunananniyar zuciya shi kuma Yaya Sadauki na addu'ar Allah ya sauƙaƙa masa al'amarin.