Sashe 18
A Babban Gida Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hannu ya ɗaga mata yace
“Ba na magana sau biyu, kuma ba na maimaita tambaya, just tell me the truth.”
Tsoro ne ya ɗarsu cikin ranta ai kuwa sai taji kawai faɗan gaskiyar ne alkairi.
“Dama Yaya...dama zare idonka kayi kana hararar Yaya Khalil shine fa.”
“Dama kallo na kike kenan?”
Tambayarsa tazo mata a ba zata.
Cikin in'ina tace
“A'a e a'a dama iya lokacin ne na ɗago.”
Fuska kame yace
“Is alright kada ki ƙara, bana son ina waje ma ake yin dariya, Thank God kin bani haƙuri jiya wallahi I'll have smash you into pieces.”
“Kayi haƙuri Yaya, ba Zan ƙara ba.”
“Is alright, Deal?” Kai ta gyaɗa Masa
“In ina magana ba a amsa min da kai, ko ke kurmiya ce?”
“A'a, na yi”
“in kin ƙara na miki me?”
“Punish me.”
“Ok, now about the issue of your Mom. Ina so ki faɗa min yadda komai ya faru.”
Hawayen da suka fara wanke mata fuska ta share, ta buɗe baki zata yi magana ya dakatar da ita
“Na duka ki ne?” da kai ta bashi amsa.
“Ba kya jin magana, ba na ce bana son a amsa min magana da kai ba?”
“I'm sorry” ta faɗa da sauri.
“Ina jin ki.”
Nan ta bashi labari tas har da ƙara wasu abubuwan da ta manta bata faɗa wa su Hajjaty ba. Cike da tausayawa yake kallon ta musamman yadda take kuka tana magana cikin raunin murya.
“Is ok, wipe your tears” ya faɗa yana miƙa mata handkerchief ɗinsa wadda kamar an yi masa wanka da ruwan turare ne. Amsa ta yi ta goge kana ta miƙa masa.
Kai ya jijjiga mata yana faɗin “No, ki riƙe shi a tare da ke, believe In me Zahrah.” sai da ta ɗago ta kalle shi jin ya ambaci sunan ta.
“In har Mamah na raye zan yi iyakar iyawa ta na binciko ta, kuma zan ɗauki hukunci a kan mutanen da suka cutar da ku da sannu. Ki daina kuka kinji? Ki zama jaruma kamar ni, na fi ki tarin damuwoyi amma ba na bari a fahimci hakan a tattare da Ni.”
“Is he that simple?” ta tambayi kanta, a zahiri kuma tace “In sha Allah Yaya, Thank you”
Without minding on her appreciation yace
“Alhaji Baba ya yi magana a kan karatunki ma, aji nawa kike?”
“S.S.S 2 ne sai na daina zuwa.”
“Ok zaki koma kin ji? Ki shirya gobe da safe I'll be taking you to school, Zaki koma final year ne kiyi SSCE.”
Jin maganar sa yasa Zahrah jin wani irin daɗi cikin ranta tana faɗin ashe haka ɗan'uwa yake?.
“Thank You so much Yaya, zuciyarka tana da kyau, kamar yadda ka faranta min Ubangiji ya yaye maka damuwoyin ka kaima ka rayu cikin farin ciki.”
“Amin” daga haka ya fara ƙoƙarin miƙewa.
“Yaya Thank you.”
Murmushi yayi wanda ya jefa ta cikin mamakin dama yana yi? Ganin kallonsa da take yasa ya ce
“Ki kula da kan ki, In kina da damuwa feel free ki same ni, and I promise to be there for you.”
“In Sha Allah, thank you.” daga haka ya bar dining ɗin ya koma parlour, ita kuma Zahrah na tsaye tana mamakin how simple he is tare da yaba kyakkyawar zuciyarsa. Murmushi tayi tana shafa fuskarta kana ta koma dining ɗin taci abincinta hankali kwance sai murmushi take yi.
Tana gamawa ta fito parlourn, lokacin har Yaya Sadauki ya tafi iya Hajjaty je zaune, murmushi tayi tana mai ƙarasawa jikin Hajjatyn ta kwanta.
Hajjaty ma murmushi tayi tace
“Zahrah'u Yayanku yace a faɗa miki da yamma ki shirya zai miƙa ki ki yi shopping.”
Zaune ta miƙe tana duban Hajjaty da mamaki. Ganin hakan kuma yasa Hajjatyn ƙara faɗaɗa murmushinta tace
“Dama na ce miki shi nake jira ya dawo ya kai ki, ban ma masa maganar ba ya tunkare Ni, yana son ƴan'uwansa shi kam, Zahrah naga wasu abubuwa tattare da shi game da ke, Please be with him, ki kula da shi kuma ki ƙarfafe shi a kowanne hali ok?”
Kai Zahrah ta gyaɗa daga nan suka ci gaba da hirarsu wacce yawanci Zahrah ke bawa Hajjaty labarin Mamah da kuma tsohuwar rayuwar su, haka kawai take jin daɗin hakan duk da ba labarin jin daɗi bane amma tana enjoying when narrating it to others, atleast yana rage mata damuwar rashin Mamah duk da cewa yanzu ma bata rasa komai ba, she's sorrounded by supporters everywhere. Fatanta Allah ta bayyana Mamah itama ta rayu da ahalinta.
Sun daɗe suna hirarsu har lokacin azahar, yau dai Zahrah ba a shiga kitchen girkin Rana ba. Ko da suka yi sallah bata fito ba sai da ta watsa ruwa. Bayan ta dawo parlourn bata ga Hajjaty ba sai ta bi ta Bedroom ɗinta. A lokacin kuma Hajjaty ta ajiye wayarta alamar dai ƙira ta amsa.
“Ƴar halak ga ki nan ma, dama Yayanku ne yace wai ki taimaka ki masa girki amma ba yanzu ba sai around 3:00pm zai shigo.”
“To Hajjaty.”
Bayan sun yi lunch Zahrah ta ɗan kwanta, bata yi aune ba taji hayaniyar su ai kuwa ta miƙe da sauri tana dirowa sannan ta nufe su da gudu tana rungume su.
“Kai sisters, daga school duk sai ku daina nema na?, Na yi fushi ma.” ta faɗa tana zame jikinta daga nasu lokaci ɗaya.
“Haba sister, ba haka bane wallahi, yanzu dai mu zauna sai ki hukunta mu.”
Zakiyya ta faɗa tana kwaɓe fuska har sai da gabaɗayansu suka dara.
“Ke dai Zakiyya ba kya rabuwa da ban dariya wallahi.”
“Ba wannan ba dai, tun da na sanya murmushi kan fuskarki na cancanci Ni kaɗai ki yafe min, kowa ta sa ta fisshe shi.” ta faɗa tana ƙara sakin dariya.
Dukan wasa suka kai mata ai kuwa Zahrah ta tare tana faɗin
“Kwa dake ta kuma? Kowa tasa ta fisshe shi. Jama'ar nan dan kun koka school sai ku mance Ni?”
“Sorry Zahrah kin san ko kowa ya manta da ke Ni ba zan manta da ke ba, ina matuƙar ji da ke shalelen hajjaty.”
Nainarh ta faɗa ita ma tana addu'ar Allah yasa ta kauce. Ƴar harara Zahrah ta banka mata kana tace
“Kin ci Sa'a ina ji da ke ai.”
Dariya ita ma tayi ta dawo ɓangaren da Zahrah da Zakiyya suke tana yi wa su Nasreen gwalo.
“Yanzu Sis Zahrah kina gani har gwalo Nainarh ke min saboda mun ɓata, dom Allah mu bawa maraɗa kunya.” Nasreen ta faɗa tana ɗagewa Zahrah gira.
“Kin ci Sa'a kema.” Zahrah ta faɗa tana janyo hannun Nasreen zuwa ɓangarensu ya rage iya Rumaysa wacce ta kwaɓe fuska tace
“Shikenan tunda Ni kaɗai ce ba a so, bari na koma kawai.” ƙofa ta nufa kamar zata fita, caraf dukkansu suka taho suka rungume juna.
“We're sorry” suka kama kunnuwansu “We all love you.”
“I love you too my sisters.”
Duk sai suka kwashe da dariya.
Haka suka yi ta shirmensu, buɗe idon da Zahrah zata yi kan wall clock taga 2:16pm, a zabure ta miƙe tana faɗin “Innalillahi, ashe akwai aiki gaba na”
Da mamaki suke kallonta
Nainarh ta ce
“Aikin me kuma?”
Duk sai suka mayar da kallonsu ga Zahrah seeking for more explanation.
Kanta ta kauda gefe tana faɗin
“Forget it kawai, maza ku tashi mu shiga kitchen.”
“Tab, daga dawowarmu daga school ko hutawa ba muyi ba?” Nainarh da Zakiyya suka faɗa.
“Naga dai ku ne kuka tsayar da Ni da yanzu na gama, Please muje ku taya Ni.”
Babu yadda suka iya haka suka nufi kitchen ɗin, tare suka toya masa sannan suka haɗa miya wacce taji nama sai mitar wai ma ake wa girkin suke, ita dai Zahrah bata ce komai ba illa iyaka ta kalle su ta kauda kai.
Bayan sun gama suka Kai dining suka jera sai ƙorafin sun gaji suke. Daga nan ta ce to su koma su huta abun su ita kuma ta nufi kitchen ɗin ta haɗa Masa fruit salad. Tana gamawa ta kai ta ajiye sannan ya koma Bedroom ɗinta.
A can ta tarar da su sun baje sai hayaniya suke, ita kuwa ta shige toilet ta sheƙa wankanta ta fito. Bata bi ta kansu ba har sai da ta shirya tukun ta zauna.
Hala suka yi ta shirmensu har lokacin da Laraba tazo kiran Zahrah.
A lokacin har Yaya Sadauki ya dawo ashe yana jiran a zo a bashi abinci. Da kanta tayi serving nasa sai surutu take masa shi kuwa ba abun da yake cewa sai dai murmushi ko uhm ko kuma a'a. Cikin ransa kuma yana ƙara yaba mata don girkin nan da yake ci dawowarsa ya tabbatar ba masu aiki ke yi ba kuma ba Hajjaty ba saboda ya san girkinta. Addu'ar sa Allah ya bashi ikon dawo da Mama don kuwa ba ƙaramar gwarzuwa bace, renon da tayi wa ƴar ta ya burge shi musamman ta ɓangaren girki, zai iya cewa cikin familyn nan da wuya a samu wacce ta iya girki ma har manyan ƴan matan gidan.
_Bari na dasa aya a nan, Please kuyi reacting sannan ku taya Ni sharing saboda Allah, in kun yi reacting sosai anjima zan ƙara update. Ina ƙaunar ku my esteem fans._
[12/28, 11:25 AM] Diamond Bhatool:
*🏡A BABBAN GIDA🏡*
*TAKUN ƘARSHE*
*©Diamond Bhatool*
*💎💍ELITE DIAMOND WRITERS💍💎*
_Where diamonds shine, words ignite_
_Wattpad: @diamond_bhatool_
_Arewabooks: @diamondbhatool3_
Please follow
*PAGE* 1️⃣4️⃣
_Wannan shafin kwacakom ɗinsa sadaukarwa ne ga Maman Tajuddeen da kuma Maryam Muhammad, alkhairin Ubangiji ya kai gareku mutanen kirki. Ina matuƙar jin daɗin comments ɗinku wallahi, ILYSM_
﷽
Yana gama ci ta tattare Wurin ta ɗan gyara, nan yace in ya huta zasu fita. Cike da farin ciki ta koma Bedroom ɗinta, har ga Allah ta manta da su Nasreen da ke ciki yayin da murmushin saman fuskarta ya kasa gushewa.
“Ehn Zahrah why this smile?”
Nasreen asked
Ba tare da ta kalle ta ba tace
“Nothing, kawai yau ta kasance rana ta farko da zan fara fita ne.”
“Da wa zaku fita? And where are you guys going?” Rumaysa ta tambaya tana kafe ta ido.
“Ehn knowing where is not important Amma in na dawo zaki gani. Ni da waye shima ban sani ba, Hajjaty dai yanzu take faɗa min cewa in shirya.”
“Ba na magana sau biyu, kuma ba na maimaita tambaya, just tell me the truth.”
Tsoro ne ya ɗarsu cikin ranta ai kuwa sai taji kawai faɗan gaskiyar ne alkairi.
“Dama Yaya...dama zare idonka kayi kana hararar Yaya Khalil shine fa.”
“Dama kallo na kike kenan?”
Tambayarsa tazo mata a ba zata.
Cikin in'ina tace
“A'a e a'a dama iya lokacin ne na ɗago.”
Fuska kame yace
“Is alright kada ki ƙara, bana son ina waje ma ake yin dariya, Thank God kin bani haƙuri jiya wallahi I'll have smash you into pieces.”
“Kayi haƙuri Yaya, ba Zan ƙara ba.”
“Is alright, Deal?” Kai ta gyaɗa Masa
“In ina magana ba a amsa min da kai, ko ke kurmiya ce?”
“A'a, na yi”
“in kin ƙara na miki me?”
“Punish me.”
“Ok, now about the issue of your Mom. Ina so ki faɗa min yadda komai ya faru.”
Hawayen da suka fara wanke mata fuska ta share, ta buɗe baki zata yi magana ya dakatar da ita
“Na duka ki ne?” da kai ta bashi amsa.
“Ba kya jin magana, ba na ce bana son a amsa min magana da kai ba?”
“I'm sorry” ta faɗa da sauri.
“Ina jin ki.”
Nan ta bashi labari tas har da ƙara wasu abubuwan da ta manta bata faɗa wa su Hajjaty ba. Cike da tausayawa yake kallon ta musamman yadda take kuka tana magana cikin raunin murya.
“Is ok, wipe your tears” ya faɗa yana miƙa mata handkerchief ɗinsa wadda kamar an yi masa wanka da ruwan turare ne. Amsa ta yi ta goge kana ta miƙa masa.
Kai ya jijjiga mata yana faɗin “No, ki riƙe shi a tare da ke, believe In me Zahrah.” sai da ta ɗago ta kalle shi jin ya ambaci sunan ta.
“In har Mamah na raye zan yi iyakar iyawa ta na binciko ta, kuma zan ɗauki hukunci a kan mutanen da suka cutar da ku da sannu. Ki daina kuka kinji? Ki zama jaruma kamar ni, na fi ki tarin damuwoyi amma ba na bari a fahimci hakan a tattare da Ni.”
“Is he that simple?” ta tambayi kanta, a zahiri kuma tace “In sha Allah Yaya, Thank you”
Without minding on her appreciation yace
“Alhaji Baba ya yi magana a kan karatunki ma, aji nawa kike?”
“S.S.S 2 ne sai na daina zuwa.”
“Ok zaki koma kin ji? Ki shirya gobe da safe I'll be taking you to school, Zaki koma final year ne kiyi SSCE.”
Jin maganar sa yasa Zahrah jin wani irin daɗi cikin ranta tana faɗin ashe haka ɗan'uwa yake?.
“Thank You so much Yaya, zuciyarka tana da kyau, kamar yadda ka faranta min Ubangiji ya yaye maka damuwoyin ka kaima ka rayu cikin farin ciki.”
“Amin” daga haka ya fara ƙoƙarin miƙewa.
“Yaya Thank you.”
Murmushi yayi wanda ya jefa ta cikin mamakin dama yana yi? Ganin kallonsa da take yasa ya ce
“Ki kula da kan ki, In kina da damuwa feel free ki same ni, and I promise to be there for you.”
“In Sha Allah, thank you.” daga haka ya bar dining ɗin ya koma parlour, ita kuma Zahrah na tsaye tana mamakin how simple he is tare da yaba kyakkyawar zuciyarsa. Murmushi tayi tana shafa fuskarta kana ta koma dining ɗin taci abincinta hankali kwance sai murmushi take yi.
Tana gamawa ta fito parlourn, lokacin har Yaya Sadauki ya tafi iya Hajjaty je zaune, murmushi tayi tana mai ƙarasawa jikin Hajjatyn ta kwanta.
Hajjaty ma murmushi tayi tace
“Zahrah'u Yayanku yace a faɗa miki da yamma ki shirya zai miƙa ki ki yi shopping.”
Zaune ta miƙe tana duban Hajjaty da mamaki. Ganin hakan kuma yasa Hajjatyn ƙara faɗaɗa murmushinta tace
“Dama na ce miki shi nake jira ya dawo ya kai ki, ban ma masa maganar ba ya tunkare Ni, yana son ƴan'uwansa shi kam, Zahrah naga wasu abubuwa tattare da shi game da ke, Please be with him, ki kula da shi kuma ki ƙarfafe shi a kowanne hali ok?”
Kai Zahrah ta gyaɗa daga nan suka ci gaba da hirarsu wacce yawanci Zahrah ke bawa Hajjaty labarin Mamah da kuma tsohuwar rayuwar su, haka kawai take jin daɗin hakan duk da ba labarin jin daɗi bane amma tana enjoying when narrating it to others, atleast yana rage mata damuwar rashin Mamah duk da cewa yanzu ma bata rasa komai ba, she's sorrounded by supporters everywhere. Fatanta Allah ta bayyana Mamah itama ta rayu da ahalinta.
Sun daɗe suna hirarsu har lokacin azahar, yau dai Zahrah ba a shiga kitchen girkin Rana ba. Ko da suka yi sallah bata fito ba sai da ta watsa ruwa. Bayan ta dawo parlourn bata ga Hajjaty ba sai ta bi ta Bedroom ɗinta. A lokacin kuma Hajjaty ta ajiye wayarta alamar dai ƙira ta amsa.
“Ƴar halak ga ki nan ma, dama Yayanku ne yace wai ki taimaka ki masa girki amma ba yanzu ba sai around 3:00pm zai shigo.”
“To Hajjaty.”
Bayan sun yi lunch Zahrah ta ɗan kwanta, bata yi aune ba taji hayaniyar su ai kuwa ta miƙe da sauri tana dirowa sannan ta nufe su da gudu tana rungume su.
“Kai sisters, daga school duk sai ku daina nema na?, Na yi fushi ma.” ta faɗa tana zame jikinta daga nasu lokaci ɗaya.
“Haba sister, ba haka bane wallahi, yanzu dai mu zauna sai ki hukunta mu.”
Zakiyya ta faɗa tana kwaɓe fuska har sai da gabaɗayansu suka dara.
“Ke dai Zakiyya ba kya rabuwa da ban dariya wallahi.”
“Ba wannan ba dai, tun da na sanya murmushi kan fuskarki na cancanci Ni kaɗai ki yafe min, kowa ta sa ta fisshe shi.” ta faɗa tana ƙara sakin dariya.
Dukan wasa suka kai mata ai kuwa Zahrah ta tare tana faɗin
“Kwa dake ta kuma? Kowa tasa ta fisshe shi. Jama'ar nan dan kun koka school sai ku mance Ni?”
“Sorry Zahrah kin san ko kowa ya manta da ke Ni ba zan manta da ke ba, ina matuƙar ji da ke shalelen hajjaty.”
Nainarh ta faɗa ita ma tana addu'ar Allah yasa ta kauce. Ƴar harara Zahrah ta banka mata kana tace
“Kin ci Sa'a ina ji da ke ai.”
Dariya ita ma tayi ta dawo ɓangaren da Zahrah da Zakiyya suke tana yi wa su Nasreen gwalo.
“Yanzu Sis Zahrah kina gani har gwalo Nainarh ke min saboda mun ɓata, dom Allah mu bawa maraɗa kunya.” Nasreen ta faɗa tana ɗagewa Zahrah gira.
“Kin ci Sa'a kema.” Zahrah ta faɗa tana janyo hannun Nasreen zuwa ɓangarensu ya rage iya Rumaysa wacce ta kwaɓe fuska tace
“Shikenan tunda Ni kaɗai ce ba a so, bari na koma kawai.” ƙofa ta nufa kamar zata fita, caraf dukkansu suka taho suka rungume juna.
“We're sorry” suka kama kunnuwansu “We all love you.”
“I love you too my sisters.”
Duk sai suka kwashe da dariya.
Haka suka yi ta shirmensu, buɗe idon da Zahrah zata yi kan wall clock taga 2:16pm, a zabure ta miƙe tana faɗin “Innalillahi, ashe akwai aiki gaba na”
Da mamaki suke kallonta
Nainarh ta ce
“Aikin me kuma?”
Duk sai suka mayar da kallonsu ga Zahrah seeking for more explanation.
Kanta ta kauda gefe tana faɗin
“Forget it kawai, maza ku tashi mu shiga kitchen.”
“Tab, daga dawowarmu daga school ko hutawa ba muyi ba?” Nainarh da Zakiyya suka faɗa.
“Naga dai ku ne kuka tsayar da Ni da yanzu na gama, Please muje ku taya Ni.”
Babu yadda suka iya haka suka nufi kitchen ɗin, tare suka toya masa sannan suka haɗa miya wacce taji nama sai mitar wai ma ake wa girkin suke, ita dai Zahrah bata ce komai ba illa iyaka ta kalle su ta kauda kai.
Bayan sun gama suka Kai dining suka jera sai ƙorafin sun gaji suke. Daga nan ta ce to su koma su huta abun su ita kuma ta nufi kitchen ɗin ta haɗa Masa fruit salad. Tana gamawa ta kai ta ajiye sannan ya koma Bedroom ɗinta.
A can ta tarar da su sun baje sai hayaniya suke, ita kuwa ta shige toilet ta sheƙa wankanta ta fito. Bata bi ta kansu ba har sai da ta shirya tukun ta zauna.
Hala suka yi ta shirmensu har lokacin da Laraba tazo kiran Zahrah.
A lokacin har Yaya Sadauki ya dawo ashe yana jiran a zo a bashi abinci. Da kanta tayi serving nasa sai surutu take masa shi kuwa ba abun da yake cewa sai dai murmushi ko uhm ko kuma a'a. Cikin ransa kuma yana ƙara yaba mata don girkin nan da yake ci dawowarsa ya tabbatar ba masu aiki ke yi ba kuma ba Hajjaty ba saboda ya san girkinta. Addu'ar sa Allah ya bashi ikon dawo da Mama don kuwa ba ƙaramar gwarzuwa bace, renon da tayi wa ƴar ta ya burge shi musamman ta ɓangaren girki, zai iya cewa cikin familyn nan da wuya a samu wacce ta iya girki ma har manyan ƴan matan gidan.
_Bari na dasa aya a nan, Please kuyi reacting sannan ku taya Ni sharing saboda Allah, in kun yi reacting sosai anjima zan ƙara update. Ina ƙaunar ku my esteem fans._
[12/28, 11:25 AM] Diamond Bhatool:
*🏡A BABBAN GIDA🏡*
*TAKUN ƘARSHE*
*©Diamond Bhatool*
*💎💍ELITE DIAMOND WRITERS💍💎*
_Where diamonds shine, words ignite_
_Wattpad: @diamond_bhatool_
_Arewabooks: @diamondbhatool3_
Please follow
*PAGE* 1️⃣4️⃣
_Wannan shafin kwacakom ɗinsa sadaukarwa ne ga Maman Tajuddeen da kuma Maryam Muhammad, alkhairin Ubangiji ya kai gareku mutanen kirki. Ina matuƙar jin daɗin comments ɗinku wallahi, ILYSM_
﷽
Yana gama ci ta tattare Wurin ta ɗan gyara, nan yace in ya huta zasu fita. Cike da farin ciki ta koma Bedroom ɗinta, har ga Allah ta manta da su Nasreen da ke ciki yayin da murmushin saman fuskarta ya kasa gushewa.
“Ehn Zahrah why this smile?”
Nasreen asked
Ba tare da ta kalle ta ba tace
“Nothing, kawai yau ta kasance rana ta farko da zan fara fita ne.”
“Da wa zaku fita? And where are you guys going?” Rumaysa ta tambaya tana kafe ta ido.
“Ehn knowing where is not important Amma in na dawo zaki gani. Ni da waye shima ban sani ba, Hajjaty dai yanzu take faɗa min cewa in shirya.”