Sashe 34
A Babban Gida Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cikin kwana ɗayan da ta yi a gidansu ta galabaita, ta saba kwana kan makeken gado ta juya yadda taso wai yau ita ce kan gayar tabarma, a can gidan mijinta ta kan manta da wata halitta ta sauro amma daren nan haka sauro suka hana ta rintsawa, da ta juya nan sai wannan ya mall mata. Da safe fuskar nan Tata ta kumbura suntum saboda rashin samun bacci, ko ina na jikinta ban da ciwo babu abun da yake yi, maimakon ta risina sai ma ƙara zafi da tayi, alwashin ta sha ma kanta tabbas aka yi auren nan sai ta hana su zaman auren nan.
Babbar magana, su Mommah an saba da samun ruwa ko yaushe sai da ta shiga wanka ta tarar ashe babu ruwa ko ɗiso, haka ta fito ranta ɓace, Hajja ta tarar a parlourn amma ko kallo ba ta samu ba, gaida ta tayi ta amsa kamar dai jiya daga haka ta ɗauke kanta. Cikin ta ne ya ba da sautin ƙulululuu, nan ta tuna rabin ta da abinci tun jiya da safe. Kamar za ta yi kuka ta ƙira sunan Hajja.
“Hajja” kallo ɗaya Hajja ta mata ta ɗauke kanta
“Ina abinci na?”
Wani kallo da Hajja ta aika mata sai da ƴaƴan hanjin cikinta suka motsa
“Dama nauyin ciyar da ke a wuya na yake Sughrah?, Ba dai ke kin isa da kan ki ba? Sai ki yi zaman gidan idan daɗi ne da shi aka ce miki, ga fili ga mai doki.”
Daga haka Hajja ta miƙe ta bar parlourn ranta na ƙuna.
Baki sake Mommah ke kallon ta, “ko meye na ɗaukan zafin rai?” Ta tambayi kanta. Daga haka ta kyaɓe baki ta wuce zuwa ɓangaren Yaya Kabir, bayan sun gaisa da Aunty Rahina sai ta rasa mai zata ce mata, ga shi yunwa take ji ga kuma izza ta hana ta faɗin abun da ya kawo ta, sarai ita ma Aunty Rahina ta fahimta amma sai ta kafse ta ci gaba da wankin kayan yaran da take yi.
“Don Allah nace ba” Mommah ta faɗa ranta na ƙuna tare da kawar da kanta gefe.
“Idan akwai abinci ki bani”
“Babu” shi ne kaɗai amsar da ta samu daga gareta. Daga haka Aunty Rahina ta ci gaba da wankin ta. Ran Mommah ina ya yi dubu to yau ya ɓaci, haka ta fice a hasale, ta shiga ƙofar Yaya Sa'ad, gwanda Aunty Rahina ta amsa mata, Aunty Maryama ko kallonta bata yi ba har ya gaji da tsayuwa ta fito don kanta.
Part ɗin ƙaninta Sadiq ta shiga, amaryarsa tace ita ma gaskiya ba isanta zai yi ba bare ta ba wani. Rai ɓace Mommah ta dawo Bedroom ɗin da aka bata, wayar ta ta ciro tana doka wa Sadauki kira amma har yau numbern ba ta shiga, hankalinta ne ya tashi amma sai ta tuna ba iya shi ta haifa ba, hakan ya sa ta ƙira ɗan'uwansa sai dai shi ma bai yi picking ba.
Ta ma rasa ta ina za ta fara ga yunwar da ta sako ta gaba, can ta yanke shawarar sayar da wayarta idan ya so ta siyo abubuwan buƙata da kuɗin kafin ta samu su yi magana da Junaid. Da wannan shawara Mommah ta fice, cikin samarin unguwar ta samu wani Ɗahiru ta bashi wayar ya sayar mata, bayan ya dawo ya bashi 3k sannan ta je ta yi siyayyar abun da za ta buƙata, indomie, macaroni, da sauran abubuwan amfani. Yara ne suka shigo mata da su har ɗakin da aka bata, ƴar katifar ta irin ta ƴan boarding school ɗin nan ta ajiye, sannan ta ƙara fitowa ta samu wasu yara suka siyo mata petrol ta tayar da generator tukun ta samu ruwan amfani.
*My readers! How did you see Mommah's life now? Shin ta cancanci hakan? Anya kuwa an kyauta mata?*
*Ina team Zahrah ne? Kun haƙura da Yaya Sadauki kenan? Muje zuwa*
[1/14, 9:06 PM] Diamond Bhatool:
*🏡A BABBAN GIDA🏡*
*TAKUN ƘARSHE*
*©Diamond Bhatool*
*💎💍ELITE DIAMOND WRITERS💍💎* _Where diamonds shine, words ignite_
_Wattpad: @diamond_bhatool_
_Arewabooks: @diamondbhatool3_
Please follow
*PAGE* 2️⃣5️⃣
﷽
*BAUCHIN YAKUBU, ƘARAMAR HUKUMAR TAFAWAƁALEWA*
Malam Sufi ne zaune da mai ɗakinsa Baba Laure wacce ke dama masa ruwan shayi, tana gamawa ta miƙa masa. Kurɓa ɗaya yayi ya juyo gare ta.
“Uwar yara yau ina so na kammala da aikin Goggo Balki, ki taimakawa maras lafiyar ku zo a kammala.” miƙewa Baba Laure tayi ta nufi cikin gidan, ɗakin da aka sauƙi Inna da maras lafiyarta sai kuma Asma'u da Balkisu ta shiga.
Fuska sake tace
“Goggo Malam yace ko Amina za ta zo a ƙarasa aikin nata”
“Ah ai dole, taimaka mata ku je tare, ko Asma'u da Balkisu ku taya ta in ba za ta iya ba.”
“Dama kuwa taraddadin yadda za mu tafin nake, Takwarar Goggo ku taya Ni mu tayar da ita.”
Da haka suka taya Baba Laure suka ɗaga Baba Amina suka nufi Ɗakin da Malam ke aiki, ko da suka kai ta fitowa suka yi Mallam yace Inna ta Zo Ayi gabanta.
Tabbas Alqur'ani waraka ne, a yau dai Malam ya samu damar warware sihirin da ke jikin baiwar Allahr ta hanyar ladabta shaiɗanin da aka wakilta don juya mata tunani. Nan ta baje kuma sai bacci.
Ba ita ta tashi ba sai wuraren la'asar, a hankali ta fara buɗe idanuwanta da suka yi nauyi cikin ranta tana ayyana wane irin nauyayyan bacci haka ta yi? Bismillah t furta tare da ƙoƙarin tashi ta zauna wanda yayi daidai da shigowar Baba Laure.
Cike da farin ciki ta ce
“Ah! Baiwar Allah kin tashi? Goggo, Goggo!”
Kiran da take ƙwala musu yasa Inna fitowa da gudu ta shigo ɗakin kamar ba ƴar tsohuwar nan ba.
Saboda rashin ƙarfin jiki har ta kusa gama tashi ta koma yaraf ta kwanta. Rintse idanuwanta tayi tana ambaton sunan Allah.
Da sauri Inna ta Zauna kusa da ita ta taimaka mata ta miƙe zaune. Idanuwanta da ta kasa buɗewa ta ƙara ƙoƙarin buɗe wa, alhandulillah kuma sun buɗu, ɗakin ta bi da kallo ba tare da ta furta komai ba, can ƙwaƙwalwarta ta fara tariyo mata last moment da ta yi aiki. A zabure ta furta “Zahrah!”
“Ma sha Allah” Inna ta furta tana faɗin
“Baiwar Allah tashi ki watsa ruwan zafi ko kya ji daɗin jikin ki.”
Sai a lokacin ta Kai dubanta ga Inna wacce ke washe mata baki. Ganin ba ta santa ba yasa ta fara kokonto kan me ya same ta
“Wace ce wannan?” ta tambayi kanta
Ganin shirun ya yi yawa yasa Inna ƙwala ƙiran Asma'u da Balkisu. Suna zuwa Inna ta basu umarnin su taimaka mata ta je ta watsa ruwa wanda tuni Baba Laure ta haɗa shi a bayi.
Ƙoƙarin gocewa matar take tana faɗin
“Ina kika je ne Zahrah?”
Cikin sigar lallashi Inna tace “Yi haƙuri baiwar Allah ki watsa ruwa kin ga jikin ki ba ƙarfi, In kin sa abu a cikin ki kin yi salla sai a yi magana ko?”
Cikin ruɗanin zuciya matar ta gyaɗa kai. Nan su Asma'u suka kai ta har bayin kafin su fito, nan suka baro ta tayi wankan suna jiranta a ɗan nesa kaɗan da bayin.
Tsantsar farin cikin da fuskarsu ta nuna zai tabbatar da irin yanayin da suke ciki.
Ta jima sosai a bayin saboda yanayin tariya da ƙwaƙwalwarta ta faɗa, can dai ta watsa ruwan ta fito, da sauri su Asma'u suka zo suka taimaka mata zuwa ɗakin da aka ba su tun farko. Kayan Baba Laure da yake ba ta cika ƙiba ba aka ba ta ta saka. Nan aka baje mata tsiren da Inna ta sa a siyo takanas don ita. Duk da bakinta babu daɗi a haka ta daure ta saka tsiren ciki, da ƙyar ta iya cin yanka biyar ta sha ruwa sannan ta jinginar da kanta jikin gini. Damuwarta ɗaya ina ƴarta take? Me take a nan kuma su waye waɗannan?”
Cikin ƙarfin hali ganin ba ta ra'ayin magana Inna tace
“Baiwar Allah kin tashi lafiya” sai lokacin ta mayar da kallonta ga Inna.
“Alhamdulillah, yau kusan kimanin shekaru biyu zuwa uku kenan kina kwance sai yau Allah yayi kika dawo daidai, na godewa Allahn da ke warkar da marasa lafiya, ya kuma azurta su da lafiya a karo na gaba.
“Ina yarinya ta Zahrah?”
Murmushi irin na manya Inna tayi tace
“Ke kaɗai muka tsinta Ni da ƴan jikoki na, amma Alhandulillah ki huta zuwa jimawa Mallam zai zo sai mu ji daga bakinsa.
*ABATCHA ESTATE*
A yau juma'a Ya Junaid ya diro ƙasarsa ta haihuwa don shaida auren ɗan'uwansa shi da iyalinsa. Abokinsa Jamal shi ya ɗauko su, kai tsaye Abatcha estate aka wuce da su. Saboda rashin gyara gidansa sakamakon a bagatatan ya zo yasa ya sauƙa Part ɗin su, surprisingly Mommah was nowhere to be found. Daga parlour suka yada trolleys nasu, matar shi Aunty Na'eema ta baje a ɗaya daga cikin kujerun da ke ɗakin shi kuma ya zaga kowanne room Amma ba kowa, fitowa waje yayi niyyar yi suka ci karo da Nainarh wacce ta shigo ɗaukar hand bag nata da zata yi amfani da shi yau.
Da gudu tayi hugging nasa tana faɗin
“Oyoyo big Bro, yaushe ka zo? Kai ɗaya ne? Ina baby Arya” lokaci guda ta jera masa tambayoyi tare da sakin sa tana jiran jin amsoshinta.
Fuska sake ya ja kuncinta yace
“My rigima Sis, waɗannan tambayoyin naki ai sai su sa na ɗimauce, wanne kike so na fara da shi?”
Fuska shagwaɓe tace “Duk nake so ka amsa min, shine kazo babu sanarwa ko?”
Murmushi yayi yace “I'm sorry, ai ban san da zancen bikin ba sai jiya da dare, I've to book flight for us mu zo a yi da mu”
Babbar magana, su Mommah an saba da samun ruwa ko yaushe sai da ta shiga wanka ta tarar ashe babu ruwa ko ɗiso, haka ta fito ranta ɓace, Hajja ta tarar a parlourn amma ko kallo ba ta samu ba, gaida ta tayi ta amsa kamar dai jiya daga haka ta ɗauke kanta. Cikin ta ne ya ba da sautin ƙulululuu, nan ta tuna rabin ta da abinci tun jiya da safe. Kamar za ta yi kuka ta ƙira sunan Hajja.
“Hajja” kallo ɗaya Hajja ta mata ta ɗauke kanta
“Ina abinci na?”
Wani kallo da Hajja ta aika mata sai da ƴaƴan hanjin cikinta suka motsa
“Dama nauyin ciyar da ke a wuya na yake Sughrah?, Ba dai ke kin isa da kan ki ba? Sai ki yi zaman gidan idan daɗi ne da shi aka ce miki, ga fili ga mai doki.”
Daga haka Hajja ta miƙe ta bar parlourn ranta na ƙuna.
Baki sake Mommah ke kallon ta, “ko meye na ɗaukan zafin rai?” Ta tambayi kanta. Daga haka ta kyaɓe baki ta wuce zuwa ɓangaren Yaya Kabir, bayan sun gaisa da Aunty Rahina sai ta rasa mai zata ce mata, ga shi yunwa take ji ga kuma izza ta hana ta faɗin abun da ya kawo ta, sarai ita ma Aunty Rahina ta fahimta amma sai ta kafse ta ci gaba da wankin kayan yaran da take yi.
“Don Allah nace ba” Mommah ta faɗa ranta na ƙuna tare da kawar da kanta gefe.
“Idan akwai abinci ki bani”
“Babu” shi ne kaɗai amsar da ta samu daga gareta. Daga haka Aunty Rahina ta ci gaba da wankin ta. Ran Mommah ina ya yi dubu to yau ya ɓaci, haka ta fice a hasale, ta shiga ƙofar Yaya Sa'ad, gwanda Aunty Rahina ta amsa mata, Aunty Maryama ko kallonta bata yi ba har ya gaji da tsayuwa ta fito don kanta.
Part ɗin ƙaninta Sadiq ta shiga, amaryarsa tace ita ma gaskiya ba isanta zai yi ba bare ta ba wani. Rai ɓace Mommah ta dawo Bedroom ɗin da aka bata, wayar ta ta ciro tana doka wa Sadauki kira amma har yau numbern ba ta shiga, hankalinta ne ya tashi amma sai ta tuna ba iya shi ta haifa ba, hakan ya sa ta ƙira ɗan'uwansa sai dai shi ma bai yi picking ba.
Ta ma rasa ta ina za ta fara ga yunwar da ta sako ta gaba, can ta yanke shawarar sayar da wayarta idan ya so ta siyo abubuwan buƙata da kuɗin kafin ta samu su yi magana da Junaid. Da wannan shawara Mommah ta fice, cikin samarin unguwar ta samu wani Ɗahiru ta bashi wayar ya sayar mata, bayan ya dawo ya bashi 3k sannan ta je ta yi siyayyar abun da za ta buƙata, indomie, macaroni, da sauran abubuwan amfani. Yara ne suka shigo mata da su har ɗakin da aka bata, ƴar katifar ta irin ta ƴan boarding school ɗin nan ta ajiye, sannan ta ƙara fitowa ta samu wasu yara suka siyo mata petrol ta tayar da generator tukun ta samu ruwan amfani.
*My readers! How did you see Mommah's life now? Shin ta cancanci hakan? Anya kuwa an kyauta mata?*
*Ina team Zahrah ne? Kun haƙura da Yaya Sadauki kenan? Muje zuwa*
[1/14, 9:06 PM] Diamond Bhatool:
*🏡A BABBAN GIDA🏡*
*TAKUN ƘARSHE*
*©Diamond Bhatool*
*💎💍ELITE DIAMOND WRITERS💍💎* _Where diamonds shine, words ignite_
_Wattpad: @diamond_bhatool_
_Arewabooks: @diamondbhatool3_
Please follow
*PAGE* 2️⃣5️⃣
﷽
*BAUCHIN YAKUBU, ƘARAMAR HUKUMAR TAFAWAƁALEWA*
Malam Sufi ne zaune da mai ɗakinsa Baba Laure wacce ke dama masa ruwan shayi, tana gamawa ta miƙa masa. Kurɓa ɗaya yayi ya juyo gare ta.
“Uwar yara yau ina so na kammala da aikin Goggo Balki, ki taimakawa maras lafiyar ku zo a kammala.” miƙewa Baba Laure tayi ta nufi cikin gidan, ɗakin da aka sauƙi Inna da maras lafiyarta sai kuma Asma'u da Balkisu ta shiga.
Fuska sake tace
“Goggo Malam yace ko Amina za ta zo a ƙarasa aikin nata”
“Ah ai dole, taimaka mata ku je tare, ko Asma'u da Balkisu ku taya ta in ba za ta iya ba.”
“Dama kuwa taraddadin yadda za mu tafin nake, Takwarar Goggo ku taya Ni mu tayar da ita.”
Da haka suka taya Baba Laure suka ɗaga Baba Amina suka nufi Ɗakin da Malam ke aiki, ko da suka kai ta fitowa suka yi Mallam yace Inna ta Zo Ayi gabanta.
Tabbas Alqur'ani waraka ne, a yau dai Malam ya samu damar warware sihirin da ke jikin baiwar Allahr ta hanyar ladabta shaiɗanin da aka wakilta don juya mata tunani. Nan ta baje kuma sai bacci.
Ba ita ta tashi ba sai wuraren la'asar, a hankali ta fara buɗe idanuwanta da suka yi nauyi cikin ranta tana ayyana wane irin nauyayyan bacci haka ta yi? Bismillah t furta tare da ƙoƙarin tashi ta zauna wanda yayi daidai da shigowar Baba Laure.
Cike da farin ciki ta ce
“Ah! Baiwar Allah kin tashi? Goggo, Goggo!”
Kiran da take ƙwala musu yasa Inna fitowa da gudu ta shigo ɗakin kamar ba ƴar tsohuwar nan ba.
Saboda rashin ƙarfin jiki har ta kusa gama tashi ta koma yaraf ta kwanta. Rintse idanuwanta tayi tana ambaton sunan Allah.
Da sauri Inna ta Zauna kusa da ita ta taimaka mata ta miƙe zaune. Idanuwanta da ta kasa buɗewa ta ƙara ƙoƙarin buɗe wa, alhandulillah kuma sun buɗu, ɗakin ta bi da kallo ba tare da ta furta komai ba, can ƙwaƙwalwarta ta fara tariyo mata last moment da ta yi aiki. A zabure ta furta “Zahrah!”
“Ma sha Allah” Inna ta furta tana faɗin
“Baiwar Allah tashi ki watsa ruwan zafi ko kya ji daɗin jikin ki.”
Sai a lokacin ta Kai dubanta ga Inna wacce ke washe mata baki. Ganin ba ta santa ba yasa ta fara kokonto kan me ya same ta
“Wace ce wannan?” ta tambayi kanta
Ganin shirun ya yi yawa yasa Inna ƙwala ƙiran Asma'u da Balkisu. Suna zuwa Inna ta basu umarnin su taimaka mata ta je ta watsa ruwa wanda tuni Baba Laure ta haɗa shi a bayi.
Ƙoƙarin gocewa matar take tana faɗin
“Ina kika je ne Zahrah?”
Cikin sigar lallashi Inna tace “Yi haƙuri baiwar Allah ki watsa ruwa kin ga jikin ki ba ƙarfi, In kin sa abu a cikin ki kin yi salla sai a yi magana ko?”
Cikin ruɗanin zuciya matar ta gyaɗa kai. Nan su Asma'u suka kai ta har bayin kafin su fito, nan suka baro ta tayi wankan suna jiranta a ɗan nesa kaɗan da bayin.
Tsantsar farin cikin da fuskarsu ta nuna zai tabbatar da irin yanayin da suke ciki.
Ta jima sosai a bayin saboda yanayin tariya da ƙwaƙwalwarta ta faɗa, can dai ta watsa ruwan ta fito, da sauri su Asma'u suka zo suka taimaka mata zuwa ɗakin da aka ba su tun farko. Kayan Baba Laure da yake ba ta cika ƙiba ba aka ba ta ta saka. Nan aka baje mata tsiren da Inna ta sa a siyo takanas don ita. Duk da bakinta babu daɗi a haka ta daure ta saka tsiren ciki, da ƙyar ta iya cin yanka biyar ta sha ruwa sannan ta jinginar da kanta jikin gini. Damuwarta ɗaya ina ƴarta take? Me take a nan kuma su waye waɗannan?”
Cikin ƙarfin hali ganin ba ta ra'ayin magana Inna tace
“Baiwar Allah kin tashi lafiya” sai lokacin ta mayar da kallonta ga Inna.
“Alhamdulillah, yau kusan kimanin shekaru biyu zuwa uku kenan kina kwance sai yau Allah yayi kika dawo daidai, na godewa Allahn da ke warkar da marasa lafiya, ya kuma azurta su da lafiya a karo na gaba.
“Ina yarinya ta Zahrah?”
Murmushi irin na manya Inna tayi tace
“Ke kaɗai muka tsinta Ni da ƴan jikoki na, amma Alhandulillah ki huta zuwa jimawa Mallam zai zo sai mu ji daga bakinsa.
*ABATCHA ESTATE*
A yau juma'a Ya Junaid ya diro ƙasarsa ta haihuwa don shaida auren ɗan'uwansa shi da iyalinsa. Abokinsa Jamal shi ya ɗauko su, kai tsaye Abatcha estate aka wuce da su. Saboda rashin gyara gidansa sakamakon a bagatatan ya zo yasa ya sauƙa Part ɗin su, surprisingly Mommah was nowhere to be found. Daga parlour suka yada trolleys nasu, matar shi Aunty Na'eema ta baje a ɗaya daga cikin kujerun da ke ɗakin shi kuma ya zaga kowanne room Amma ba kowa, fitowa waje yayi niyyar yi suka ci karo da Nainarh wacce ta shigo ɗaukar hand bag nata da zata yi amfani da shi yau.
Da gudu tayi hugging nasa tana faɗin
“Oyoyo big Bro, yaushe ka zo? Kai ɗaya ne? Ina baby Arya” lokaci guda ta jera masa tambayoyi tare da sakin sa tana jiran jin amsoshinta.
Fuska sake ya ja kuncinta yace
“My rigima Sis, waɗannan tambayoyin naki ai sai su sa na ɗimauce, wanne kike so na fara da shi?”
Fuska shagwaɓe tace “Duk nake so ka amsa min, shine kazo babu sanarwa ko?”
Murmushi yayi yace “I'm sorry, ai ban san da zancen bikin ba sai jiya da dare, I've to book flight for us mu zo a yi da mu”