Sashe 19
A Babban Gida Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Abayar da Nasreen ta kawo mata ta saka sannan ta fara ƙoƙarin gyara fuskarta, ko da ta gama ta juyo gurin su hannunta riƙe da veil suka tsira mata ido.
She look so awnn and breathtaking. Ganin ta Yi Shirin fita yasa Zakiyya faɗin
“Bari na je na ɗan huta Please, xan dawo anjima kafin nan kun dawo.”
“Nan ɗin ba wurin hutawa ne sai kin koma can?” Zahrah ta tambaya.
“Tsaya muje Zakiyya nima zan wuce, Mommah ta ce min Yaya Sadauki ya dawo, In ya koma bai tarar da Ni ba zai hukunta ni.”
Nan suka wuce suna ɗagawa Zahrah hannu “Ki kawo mana tsaraba kuma.”
Nasreen da Rumaysa zamansu suka yi nan Bedroom ɗin Zahrah ita kuma ta fito parlour tana jiransa.
Few minutes sai ga Yaya Sadauki cikin takunsa na ƙasaita, sanye yake cikin wata back expensive T-shirt gaban an rubuta SPORT sai Kuma blue-black jeans Wanda ya ɗan kama shi kaɗan. Black takalmi ne a ƙafarsa, taku yake kamar wani basarake yayin da ƙamshin turarensa ke isa wuri kafin shi.
Agogonsa da ke ɗaure a tsintsiyar hannu ya duba ganin da sauran lokaci yasa kai tsaye ya nufi Bedroom ɗin Hajjaty ya mata sallama kan sun tafi. Ko da ya fito bai ce mata uffan ba sai yayi waje, ta riga ta gane cewa miskilanci a jininsa ne hakan yasa ta miƙe tabi bayansa.
Motar da ya nufa ta ƙarewa kallo tana ƙara yaba kyanta, horn ɗin da yayi mata yasa ta Zabura ta nufi motar, gidan baya ta buɗe da niyyar shiga ta tsinkayi muryarsa yana faɗin.
“Ni drivern ki ne?” ai tuni ta rufe ta koma front seat ta Zauna.
Wani makeken shopping mall ya nufa da ita yayinda kowannensu ya ƙunshe bakinsa in Banda sautin karatun Minshawiy babu abinda ke tashi yayin da Zahrah ke ɗan satar kallonsa time to time tana ayyana irin nutsuwarsa.
15minutes suka share kafin suka isa, bayan ya daidaita parking ne ya juyo gareta
“Let's go” daga haka ya buɗe side ɗin da yake haka nata ɓangaren ma. Tunda duka fito mutane ke kallonsu musamman Yaya Sadauki da ya shahara a faɗin ƙasar ba don saboda tarin dukiyar da yake da shi ba sai don ƙwazo da ubangiji yayi masa, he's the head as well as founder of NIC, mutumin da ya samu ƙwarewa a fannin bincike sannan kuma the whole CEO of Abatcha Automobiles Wanda ke ji da kuma tashe da samartaka.
A tare suka nufi entrance na makeken mall ɗin, wasu na faɗin
“Anya wannan ba ALIYU UMAR ABATCHA ba ne?” others are worried about the lady he's with Suna fatan ba aure yayi ba, wasu ƴanmatan kuma na faɗin ai ko ya yi aure suna son shi, mathna wa thulatha wa rubā', wasu kuma na faɗin maybe ƙanwarsa ce don da gani ba aure tsakaninsu. To shi ya ma san suna yi ne?”
Kallon Zahrah yayi bayan sun shiga yace
“Go round and pick anything you like, kada ki damu da ya yake just pick it ok?”
Kai ta gyaɗa Masa daga haka ta nufi ciki, tsawon mintuna amma ta kasa zaɓar komai, kamar ya sani kuwa sai ya bi bayanta, ganin babu abunda ta ɗauka yasa ya ɗan ja ƙaramin tsaki.
Komawa yayi sai ga shi tare da ɗaya daga cikin ma'aikatan wurin, pointing ma Mai aikin Zahrah yayi wacce ke tsaye still ko uban me take. Ban ji me yace masa ba sai ga Zahrah ta dawo wurin sa da zuwan mutumin. Daga nan Yaya Sadauki yace su fito su jira a mota.
Ba musu tabi bayansa suka koma. Kusan 10 minutes sai ga mutumin nan da wasu masu irin kayansa sun fito su uku yayin da hannuns kowannensu ke ɗauke da akwati. Motar su Yaya Sadauki suka nufa, dama booth a buɗe yake, so basu sha wahala ba suka ajiye kana mutumin yazo ta saitin da Yaya Sadauki yake ya miƙa masa ATM card ɗinsa, har ya karɓa mutumin na shirin juyawa ya tsayar da shi sannan ya miƙa masa wasu kuɗaɗe masu ɗan yawa.
“Thank you” mutumin ya fara godiya kenan Yaya Sadauki ya ɗaga masa hannu. Nan ya basu hanya su kuma suka wuce abun su.
Ba tare da Yaya Sadauki ya kalli Zahrah ba yace
“Why didn't you pick anything? Ko babu abun da ya burge ki a wurin ne?”.
Har ta jijjiga kai ta tuna da ba ya so, da sauri ta buɗe baki tace
“A'a ban san ya kuɗin abubuwan zai kasance ba, kada na ɗauki masu tsada da yawa na karar maka da kuɗinka.”
Statement ɗinta na ƙarshe ne ya bashi dariya har sai da ya murmusa ita kuma sai kallonsa take ganin yadda wani sihirtaccen kyau ke fitowa daga gare shi cikin ranta ta furta “Tabarakallahu Ahsanul Khaliqin”.
“An ce miki kuɗi na zai ƙare ne for common shopping da zaki yi? Ai ko mall ɗin zan siye babu wani giɓi da kuɗaɗe na zasu samu.”
A ba zata ta furta
“Ka ji daɗin ka”
“Ke ma kina son kuɗin ne?”
Dariya Zahrah ta kwashe da ita jin ya mata wata irin tambaya har sai da dimples ɗinta suka lotsa, duk irin yadda yaso ya kauda kansa kasawa yayi, sai ya tsinci kansa da faɗin
“Kina da kyau” tukun ya mayar da dubansa ga titi.
“Kai Yaya ai kuwa ka fi Ni, duk duniyar nan ban taɓa ganin kyakkyawa kamar ka ba, da ina cewa Yaya Ishaq ne amma tun da na ganka na tabbatar babu ya kai.”
Kalamanta sun masa daɗi ta ɗaya ɓangaren kuma sun bashi dariya amma a wannan karan dariyarsa yayi ga yadda fararen haƙwarensa suka bayyana, Zahrah kam kasa daina kallonsa tayi.
“You're funny Zahrah, Wai kina nufin na fi kowa da, to ina batun Indian”
“Allah Yaya ka fi su musamman when you smile, sai ka ƙara kyau.”
“Uhm” kawai yace ganin sun doso katafaren gate na estate ɗin su. Bayan sun iso yayi parking a apartment ɗin Hajjaty.
A hankali ya furta “You can go, Ni zan wuce part ɗin mu, Please in baki gaji ba cook something for me.”
“Ok Yaya thank you, may God bless your wealth and Grant you jannah.”
Ya ji daɗi sosai da addu'arta har sai da ya murmusa sannan yace
“Amin Lily, Zan sa a shigo da kayanki yanzu, take care.”
“Ok bye” ta faɗa tana waving hand ɗinta sannan ta shige ciki shi kuma ya ja motarsa zuwa part ɗin su.
Ashe duk abun da ke faruwa a idon Rumana ne wacce ta kusa mutuwa don mamaki da tsananin kishi, wai a wannan yarinyar Yaya Sadauki yake wa murmushi? Yaushe ma yazo?, Tsabagen yadda zuciyarta ke tafasa da gudu ta tafi tana kuka har part ɗinsu without minding the distance.
Ita kuwa Zahrah tana shiga ta tarar da Hajjaty na zaune ita da Ya Auwab, Ya Taj, Ya Aufa da kuma ya Faruq, kan ta ƙasa ta ƙarasa. Fuska sake Hajjaty tace
“A'a Zahrah'u an dawo kenan, ina shi Sadaukin?”
“E Hajjaty ya wuce part ɗin Mommah.”
Shaye da mamaki Ya Auwab ke kallon Hajjatyn kana yace
“Hajjaty wane Sadaukin? Wai Yaya dodon mu?”
Sosai Zahrah ta dara duk da cewa she's not comfortable being in-between them saboda yawan kallo irin na Ya Auwab.
“Shi dai, ai tun jiya ya iso shi da Halilu.”
Zahrah dai wucewa tayi zuwa Bedroom ɗinta, kamar yadda tayi zato none of them was there. Wanka ta Yi ta ɗauro alwala, tana idar da Sallah ta yi zikirorinta sannan ta nufi kitchen don haɗawa Yaya Sadauki abinci.
*Yaya Sadauki*
Lokacin da ya isa ma an fara kiraye-kirayen sallah, hakan yasa ya haye sama don yin alwala, kamar yadda Mommah tayi alƙawari ta sa na gyara masa Bedroom ɗinsa. A gaggauce yayi wanka sannan ya ɗauro alwala, yana saka kaya ya fito sai sauri yake jin an shiga sallah a masallaci.
Bai wani tsaya ba da aka idar kuma bai bi su Alhaji Baba ba sai ya juya zuwa ɓangarensu don samarwa mahaifiyarsa lafiya. Ita ma lokacin tana parlourn ita da Nainarh sai kuma auta Ra'ees. Da gudu Rarrashi ya nufi Yayan nasa yana ihun murna
“Oyoyo Yaya, oyoyo Yaya.”
Hugging nasa yayi shima yana murmushi coz he so much adore that little creature.
Tare suka ƙarasa. Cike da farin ciki Nainarh ta gaishe shi tana faɗin yaushe ya dawo?, Kallon da ya aika mata yasa ta miƙe tsaye ta nufi Bedroom ɗinta. Kallon Ra'ees yayi yace
“My Man, maza ka bi Aunty Nainarh ka ce ta koya maka karatu.”
A shagwaɓe Ra'ees ɗin yace
“Yanzu Aunty Nainarh duka na zata yi, da ba ka nan ma kullum sai ta je wajen Aunty Zahrah da Mommah ta hana naje na ganta,kuma Aunty Nainarh tace kyakkyawa ce, wai haka ne Yaya?”
“Uhm, yanzu kace Ni na aiko ka ba zata dake ka ba kaji.” daga haka Ra'ees ɗin ya wuce shi kuma ya maida dubansa ga Mommah. Cike da girmamawa ya gaida ta ta amsa fuska babu yabo babu fallasa.
Suna gama gaisawa tace
“Aliyu ya zancen aurenka da yarinyar can? Ka samu ka shawo hankalin Alhaji Baba?” dariyar takaici yayi cikin ransa yana ƙara nema mata shiriya.
“Mommah ai babu fashi auren nan, nima ina so fa”
A zabure tace
“Uban me suka ba ka Aliyu, yaushe ma kake kula matan ballantana har ka ce kana son ta, wallahi ƙarya kake kuma baka isa ka auri ɗiyar Hajiya Babba ba.”
Ganin yadda ta ɗau zafi yasa ya kwantar da murya yace
“I'm sorry Mommah, calm down please” tea ɗin da ke ajiye kan Centre table ya miƙa mata
“Shikenan mu bar zancen tunda baki so, mu yi wani daban.”
Haka suka sha hirar su daga nan kuma ya fice saboda lokacin salla da yayi. Bayan an idar kuma ya wuce da Alhaji Baba.
Shi da kansa ya shiga da akwatinan da ya manta bai sa an miƙa mata su ba tun ɗazu. Laraba da ta Ganshi da sauri ta karɓa nan ya faɗa nata inda zata kai. Dayan ya koma ya ɗauko sannan ya nufi ciki.
She look so awnn and breathtaking. Ganin ta Yi Shirin fita yasa Zakiyya faɗin
“Bari na je na ɗan huta Please, xan dawo anjima kafin nan kun dawo.”
“Nan ɗin ba wurin hutawa ne sai kin koma can?” Zahrah ta tambaya.
“Tsaya muje Zakiyya nima zan wuce, Mommah ta ce min Yaya Sadauki ya dawo, In ya koma bai tarar da Ni ba zai hukunta ni.”
Nan suka wuce suna ɗagawa Zahrah hannu “Ki kawo mana tsaraba kuma.”
Nasreen da Rumaysa zamansu suka yi nan Bedroom ɗin Zahrah ita kuma ta fito parlour tana jiransa.
Few minutes sai ga Yaya Sadauki cikin takunsa na ƙasaita, sanye yake cikin wata back expensive T-shirt gaban an rubuta SPORT sai Kuma blue-black jeans Wanda ya ɗan kama shi kaɗan. Black takalmi ne a ƙafarsa, taku yake kamar wani basarake yayin da ƙamshin turarensa ke isa wuri kafin shi.
Agogonsa da ke ɗaure a tsintsiyar hannu ya duba ganin da sauran lokaci yasa kai tsaye ya nufi Bedroom ɗin Hajjaty ya mata sallama kan sun tafi. Ko da ya fito bai ce mata uffan ba sai yayi waje, ta riga ta gane cewa miskilanci a jininsa ne hakan yasa ta miƙe tabi bayansa.
Motar da ya nufa ta ƙarewa kallo tana ƙara yaba kyanta, horn ɗin da yayi mata yasa ta Zabura ta nufi motar, gidan baya ta buɗe da niyyar shiga ta tsinkayi muryarsa yana faɗin.
“Ni drivern ki ne?” ai tuni ta rufe ta koma front seat ta Zauna.
Wani makeken shopping mall ya nufa da ita yayinda kowannensu ya ƙunshe bakinsa in Banda sautin karatun Minshawiy babu abinda ke tashi yayin da Zahrah ke ɗan satar kallonsa time to time tana ayyana irin nutsuwarsa.
15minutes suka share kafin suka isa, bayan ya daidaita parking ne ya juyo gareta
“Let's go” daga haka ya buɗe side ɗin da yake haka nata ɓangaren ma. Tunda duka fito mutane ke kallonsu musamman Yaya Sadauki da ya shahara a faɗin ƙasar ba don saboda tarin dukiyar da yake da shi ba sai don ƙwazo da ubangiji yayi masa, he's the head as well as founder of NIC, mutumin da ya samu ƙwarewa a fannin bincike sannan kuma the whole CEO of Abatcha Automobiles Wanda ke ji da kuma tashe da samartaka.
A tare suka nufi entrance na makeken mall ɗin, wasu na faɗin
“Anya wannan ba ALIYU UMAR ABATCHA ba ne?” others are worried about the lady he's with Suna fatan ba aure yayi ba, wasu ƴanmatan kuma na faɗin ai ko ya yi aure suna son shi, mathna wa thulatha wa rubā', wasu kuma na faɗin maybe ƙanwarsa ce don da gani ba aure tsakaninsu. To shi ya ma san suna yi ne?”
Kallon Zahrah yayi bayan sun shiga yace
“Go round and pick anything you like, kada ki damu da ya yake just pick it ok?”
Kai ta gyaɗa Masa daga haka ta nufi ciki, tsawon mintuna amma ta kasa zaɓar komai, kamar ya sani kuwa sai ya bi bayanta, ganin babu abunda ta ɗauka yasa ya ɗan ja ƙaramin tsaki.
Komawa yayi sai ga shi tare da ɗaya daga cikin ma'aikatan wurin, pointing ma Mai aikin Zahrah yayi wacce ke tsaye still ko uban me take. Ban ji me yace masa ba sai ga Zahrah ta dawo wurin sa da zuwan mutumin. Daga nan Yaya Sadauki yace su fito su jira a mota.
Ba musu tabi bayansa suka koma. Kusan 10 minutes sai ga mutumin nan da wasu masu irin kayansa sun fito su uku yayin da hannuns kowannensu ke ɗauke da akwati. Motar su Yaya Sadauki suka nufa, dama booth a buɗe yake, so basu sha wahala ba suka ajiye kana mutumin yazo ta saitin da Yaya Sadauki yake ya miƙa masa ATM card ɗinsa, har ya karɓa mutumin na shirin juyawa ya tsayar da shi sannan ya miƙa masa wasu kuɗaɗe masu ɗan yawa.
“Thank you” mutumin ya fara godiya kenan Yaya Sadauki ya ɗaga masa hannu. Nan ya basu hanya su kuma suka wuce abun su.
Ba tare da Yaya Sadauki ya kalli Zahrah ba yace
“Why didn't you pick anything? Ko babu abun da ya burge ki a wurin ne?”.
Har ta jijjiga kai ta tuna da ba ya so, da sauri ta buɗe baki tace
“A'a ban san ya kuɗin abubuwan zai kasance ba, kada na ɗauki masu tsada da yawa na karar maka da kuɗinka.”
Statement ɗinta na ƙarshe ne ya bashi dariya har sai da ya murmusa ita kuma sai kallonsa take ganin yadda wani sihirtaccen kyau ke fitowa daga gare shi cikin ranta ta furta “Tabarakallahu Ahsanul Khaliqin”.
“An ce miki kuɗi na zai ƙare ne for common shopping da zaki yi? Ai ko mall ɗin zan siye babu wani giɓi da kuɗaɗe na zasu samu.”
A ba zata ta furta
“Ka ji daɗin ka”
“Ke ma kina son kuɗin ne?”
Dariya Zahrah ta kwashe da ita jin ya mata wata irin tambaya har sai da dimples ɗinta suka lotsa, duk irin yadda yaso ya kauda kansa kasawa yayi, sai ya tsinci kansa da faɗin
“Kina da kyau” tukun ya mayar da dubansa ga titi.
“Kai Yaya ai kuwa ka fi Ni, duk duniyar nan ban taɓa ganin kyakkyawa kamar ka ba, da ina cewa Yaya Ishaq ne amma tun da na ganka na tabbatar babu ya kai.”
Kalamanta sun masa daɗi ta ɗaya ɓangaren kuma sun bashi dariya amma a wannan karan dariyarsa yayi ga yadda fararen haƙwarensa suka bayyana, Zahrah kam kasa daina kallonsa tayi.
“You're funny Zahrah, Wai kina nufin na fi kowa da, to ina batun Indian”
“Allah Yaya ka fi su musamman when you smile, sai ka ƙara kyau.”
“Uhm” kawai yace ganin sun doso katafaren gate na estate ɗin su. Bayan sun iso yayi parking a apartment ɗin Hajjaty.
A hankali ya furta “You can go, Ni zan wuce part ɗin mu, Please in baki gaji ba cook something for me.”
“Ok Yaya thank you, may God bless your wealth and Grant you jannah.”
Ya ji daɗi sosai da addu'arta har sai da ya murmusa sannan yace
“Amin Lily, Zan sa a shigo da kayanki yanzu, take care.”
“Ok bye” ta faɗa tana waving hand ɗinta sannan ta shige ciki shi kuma ya ja motarsa zuwa part ɗin su.
Ashe duk abun da ke faruwa a idon Rumana ne wacce ta kusa mutuwa don mamaki da tsananin kishi, wai a wannan yarinyar Yaya Sadauki yake wa murmushi? Yaushe ma yazo?, Tsabagen yadda zuciyarta ke tafasa da gudu ta tafi tana kuka har part ɗinsu without minding the distance.
Ita kuwa Zahrah tana shiga ta tarar da Hajjaty na zaune ita da Ya Auwab, Ya Taj, Ya Aufa da kuma ya Faruq, kan ta ƙasa ta ƙarasa. Fuska sake Hajjaty tace
“A'a Zahrah'u an dawo kenan, ina shi Sadaukin?”
“E Hajjaty ya wuce part ɗin Mommah.”
Shaye da mamaki Ya Auwab ke kallon Hajjatyn kana yace
“Hajjaty wane Sadaukin? Wai Yaya dodon mu?”
Sosai Zahrah ta dara duk da cewa she's not comfortable being in-between them saboda yawan kallo irin na Ya Auwab.
“Shi dai, ai tun jiya ya iso shi da Halilu.”
Zahrah dai wucewa tayi zuwa Bedroom ɗinta, kamar yadda tayi zato none of them was there. Wanka ta Yi ta ɗauro alwala, tana idar da Sallah ta yi zikirorinta sannan ta nufi kitchen don haɗawa Yaya Sadauki abinci.
*Yaya Sadauki*
Lokacin da ya isa ma an fara kiraye-kirayen sallah, hakan yasa ya haye sama don yin alwala, kamar yadda Mommah tayi alƙawari ta sa na gyara masa Bedroom ɗinsa. A gaggauce yayi wanka sannan ya ɗauro alwala, yana saka kaya ya fito sai sauri yake jin an shiga sallah a masallaci.
Bai wani tsaya ba da aka idar kuma bai bi su Alhaji Baba ba sai ya juya zuwa ɓangarensu don samarwa mahaifiyarsa lafiya. Ita ma lokacin tana parlourn ita da Nainarh sai kuma auta Ra'ees. Da gudu Rarrashi ya nufi Yayan nasa yana ihun murna
“Oyoyo Yaya, oyoyo Yaya.”
Hugging nasa yayi shima yana murmushi coz he so much adore that little creature.
Tare suka ƙarasa. Cike da farin ciki Nainarh ta gaishe shi tana faɗin yaushe ya dawo?, Kallon da ya aika mata yasa ta miƙe tsaye ta nufi Bedroom ɗinta. Kallon Ra'ees yayi yace
“My Man, maza ka bi Aunty Nainarh ka ce ta koya maka karatu.”
A shagwaɓe Ra'ees ɗin yace
“Yanzu Aunty Nainarh duka na zata yi, da ba ka nan ma kullum sai ta je wajen Aunty Zahrah da Mommah ta hana naje na ganta,kuma Aunty Nainarh tace kyakkyawa ce, wai haka ne Yaya?”
“Uhm, yanzu kace Ni na aiko ka ba zata dake ka ba kaji.” daga haka Ra'ees ɗin ya wuce shi kuma ya maida dubansa ga Mommah. Cike da girmamawa ya gaida ta ta amsa fuska babu yabo babu fallasa.
Suna gama gaisawa tace
“Aliyu ya zancen aurenka da yarinyar can? Ka samu ka shawo hankalin Alhaji Baba?” dariyar takaici yayi cikin ransa yana ƙara nema mata shiriya.
“Mommah ai babu fashi auren nan, nima ina so fa”
A zabure tace
“Uban me suka ba ka Aliyu, yaushe ma kake kula matan ballantana har ka ce kana son ta, wallahi ƙarya kake kuma baka isa ka auri ɗiyar Hajiya Babba ba.”
Ganin yadda ta ɗau zafi yasa ya kwantar da murya yace
“I'm sorry Mommah, calm down please” tea ɗin da ke ajiye kan Centre table ya miƙa mata
“Shikenan mu bar zancen tunda baki so, mu yi wani daban.”
Haka suka sha hirar su daga nan kuma ya fice saboda lokacin salla da yayi. Bayan an idar kuma ya wuce da Alhaji Baba.
Shi da kansa ya shiga da akwatinan da ya manta bai sa an miƙa mata su ba tun ɗazu. Laraba da ta Ganshi da sauri ta karɓa nan ya faɗa nata inda zata kai. Dayan ya koma ya ɗauko sannan ya nufi ciki.