Sashe 26
A Babban Gida Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Gyara tsayuwar sa yayi sannan ya nuna masa gidan da ke kallonsu.
“Baba don Allah masu gidan nan ko sun yi ƙaura ne?”
Tsohon yace “E to ba zan ce kamai ba amma dai kwanaki na ji mai ɗaki na tana faɗin ko matar gidan ce aka sace ko meye, amaryar gidan kuma kamar dai sun sayar gidan ita da ƴar ta sunyi gaba.”
Zuciyar matashin ne ya tsananta Bugu sakamakon zancen da yake ji daga wurin tsoho. Tattara jarunta da ke shirin barin gangar jikinsa ya yi sannan yace
“To Baba, shi Mai gidan fa?”
“Ai yaro bari in gajarta maka zancen nan, shima Mai gidan babu wanda yasan ina yake.”
“Shikenan ba gode Baba, ga wannan”
Ya faɗa yana miƙo masa kuɗin da ke jikinsa, nan tsoho ya fara godiya, ba tare da ta saurari godiyar ba ya masa sallama tare da nufar motarsa fuskarsa na nuna tsantsar tashin hankali da damuwa, a haka ta figi motar, bai tsaya ko ina ba dai gidansu. Ko da ya Yi parking sai ga Guards ɗin sa sun kewaye shi to see if he's alright saboda taka tsan-tsan da suke da aikin su. Uban gidansu ya musu warning kan shalelen ɗansa, saboda haka ko da ya ce ba zai fita da su ba zaman addu'ar Allah ya dawo da shi lafiya suke yi.
Wannan kenan!
*ABATCHA ESTATE*
*Yayan Lily*
Bayan sallar maghrib ya dawo, kai tsaye part ɗin su ya wuce, sai da yayi wanka tukun ya fito, lokacin kuma Mommah na zaune parlourn ta caɓa uban ado ga kuma yadda ta make fuska babu annuri. Tana ganin fitowar sa ta nufi inda yake.
“Aliyu!” ya dakata jin ta ambaci sunansa sai kuma ya waiwayo yana smiling
“Sannu da gida Mommah”
Ba tare da ta amsa masa ba sai ma cakushe fuska da ta ƙara yi tace
“Aliyu sau nawa zan faɗa maka cewa ka cire zancen auren wannan ƴar iskar a ranka? Me yasa ba ka jin magana ta? Remember Ni Mahaifiyarka ce K kumaum ina da ikon hana wannan auren. Wallahi tun muna shaida juna da arziƙi ka ce musu ka janye!”
Lumshe idanuwansa ya yi ya buɗe waɗanda lokaci guda kuma suka yi jawur, ya gaji da irin wannan hali na mahaifiyarsa, ƙoƙarin controlling temper ɗinsa yayi sannan ya kwantar da Murya
“Mommah Please, ah beg you ki daina batun janye aure, Sanin kan ki ne fa Alhaji Baba da kansa ya yi wannan hukuncin kuma babu wanda ya isa ya ja da shi kin sani, so Please Mommah ki kwantar da hankalin ki kawai ki rungumi ƙaddara.”
A hasale tace
“Na kwantar da hankali na fa kace Aliyu! Ka san kuwa me kake faɗi?”
Ganin ta hau da yawa yasa ya ja hannunta ya zaunar da ita kan ɗaya daga cikin kujerun da ke parlourn sannan ya ɗauki cup da ke kan Centre table ya tsiyaya mata ruwa yana miƙa mata.
“Have this” ganin tana bukatar ruwa yasa ta amsa ta kafa kai, tas ta shanye sannan ta miƙa masa cup ɗin. Ajiyewa yayi shima sai ya zauna gefenta tare da riƙo hannunta, motherhood bond is different, tuni ta fashe da kuka tana faɗin.
“Ni yanzu shikenan so kake na kashe kaina kafin ka haƙura da auren?” ta faɗa sounding so serious.
“Ba Haka ba nee Mommah, get one thing please, cewa sai an fasa aure kin san ba mai yiwuwa ba ne tunda Alhaji da.....”
Katse shi tayi tana ɗaga masa hannu
“Ya isa haka Aliyu! Na gaji da jin fasawa ba zai yiwu ba, na gaji! sai cewa kake Alhaji Baba ne ya yanke hukunci ba zai yiwu ba nace shi Alhaji Baban Allah ne In ya yi hukunci dole a bi? Nace shi ya haifa min haifa min kai ne da zai ke nuna ikonsa a kanka, let him show his power only on his children muma ya bar mu muyi iko da namu!” ta idasa tana share ƙwallar da ke zubo mata.
Handkerchief ɗin sa ya ɗauko yana share mata hawayen
“Is ok Mommah, ya isa kukan kada ki ja ma kanki ciwo, ina riƙon ki da Allah ku kwantar da hankalin ki kada ki yi abun da za ki zubar da ƙimarki cikin gidan nan.”
A ɗan zafafe tace
“Aliyu ƙima? Maganar ƙima naji kana yi? To ai already ba Ni da ita a gidan nan, Im da a ce ina da ita ai da ba za a yanke hukunci a kan dab na ba tare da an bani damar amincewa ko akasin hakan ba. Wallahi Aliyu ko igiyoyin aure na za su tsinke wallahi ba zan bari a yi auren nan ba.”
Tana faɗin haka ta tashi fuu ta nufi Bedroom ɗinta yayin da ta bar Yaya Sadauki kamar statue. Miƙewa shima yayi jiki ba ƙwari ya fice. Direct Masjid ya tafi ko da aka isar kamar kullum ya biyo su Alhaji Baba suka taho tare da sauran Uncles ɗin shi har da waɗanda bai yi tsammanin gani ba. Ko da suka isa a an parlourn suka yada zango har Hajjaty ta fito suka gaisa sannan shima da ke zaune kan carpet ya gaida Uncles ɗin nashi.
Alhaji Baba ne ya unarve su da su tashi a ci abinci sai a lokacin Hajjaty ta lura da ba Zahrah a wajen. Ba ta ce komai ba ta je ta kira Zahrah. A tare suka ƙaraso Zahrah ta ja ma Hajjaty kujera, bayan ya zauna ta fara gaida Uncles ɗin ta suka amsa fuska sake, nan ya Yi serving kowa including her Heart's desire 😳.
*Na san kuna da tarin tambayoyi gare Ni my esteem readers, ku dai kawai mu je zuwa.*
_React and share please._
[12/31/2024, 10:17 PM] Diamond Bhatool:
https://whatsapp.com/channel/0029VanUFkw5kg7G2ci16o2X
*🏡A BABBAN GIDA🏡*
*TAKUN ƘARSHE*
*©Diamond Bhatool*
*💎💍ELITE DIAMOND WRITERS💍💎*
_Where diamonds shine, words ignite_
_Wattpad: @diamond_bhatool_
_Arewabooks: @diamondbhatool3_
Please follow
*PAGE* 2️⃣0️⃣
﷽
Bayan sun gama dinner dukkan su suka dawo parlourn kamar yadda yake. Alhaji Baba bai ware kowa ba, kai tsaye ya fara magana kan dalilin tara su.
“Kamar yadda kuka sani irin wannan kira na gaggawa na ɗauke da ma'anoni mabanbanta, haka zalika yau ma dai na ƙara tara ku saboda wani muhimmin batu, ɓarakar da aka samu a kwanakin baya tsakanin Sadauki da kuma Mabruka ƴar wajen Sadiƙu, na san dukkan ku abun ha jijjiga ku musamman iyaye a ɓangare biyun, ko da ba su nuna wa juna ba tabbas zukatan su sun munana. Dalilin haka ya sa na yanke hukuncin ɗaura aure a tsakaninsu bayan tabbatar da cewa babu komai ɗin da ya faru kawai shiri ne na maƙiya, sai na ga mu toshe bakin maƙiya ta hanyar haɗa auren su zai fi. Ya kuke gani a matsayin ku na iyaye?”
Cike da biyayya kowannensu yayi na'am da hukuncin Alhaji Baba, Nan ya ƙara da faɗin.
“Ma sha Allah, ina ƙara godewa Allah da ya bani ƴaƴa masu tarbiyya waɗanda ba su taɓa ja da hukuncin da na zartar, Ubangiji ya baku masu yi muku biyayya kwatankwacin yadda kuka min.”
Nan suka amsa da “Amin!” Alhaji Baba ya ɗaura da
“Saboda gabatowar azumi nan da wata ɗaya, na yanke ranar bikin cikin makonni biyu ma su zuwa, kowa sai ya fara shirye-shirye.”
Nan gaba ɗaya su Daddy, Appa, Abie da sauran suka fara addu'ar Allah ya sanya alkhairi. Daga nan kuma suka fara taɗin su na ƴaƴan da iyaye.
*Ina Zahrah?*
Tun da ta fahimci akwai abun da za a tattauna ta fara tashi daga dining ɗin sai ta fice daga apartment ɗin ta tsaya bakin ƙofar saboda ta samu damar ji. (Babu kyau gulma fa Zahrah?”
A lokacin da ta ji Alhaji Baba ya ce an yanke ranar bikin Yayanta in 2weeks time ji ta yi kamar an ɗiga mata wani tafasasshen ruwa a zuciyarta. A zabure ta fice ta zagaya ta ƙofar baya, da ƙyar da taimakon Ubangiji ta isa Bedroom ɗinta.
Tana shiga ta faɗa kan Bed ɗin ta tare da fashewa da wani matsanancin kuka, ta rasa ina za ta jefa ranta ta ji sanyi a duniyar nan, ga shi babu kafaɗar wanda za ta kwanta ta zubda ƙwallarta. Nan zuciyarta ta fara tariyo mata moments ɗin da yayanta, why ta yi sauri falling in to his love? Ashe son sa take tsawon lokacin nan?
“No, ba na sonsa, kawai dai ɗan'uwa na ne!” ta faɗa a bayyane.
Da sauri zuciyarta ta ƙaryata ta da faɗin
“Idan har you're not in love with him why kike jin kishinsa?”
Da sauri ta furta
“Kishi? Kishinsa nake?, Noooooo!” ta faɗa tana buga pillown da ke hannunta
“That's impossible!”
Zuciyarta ta ƙara ce mata “Is Possible Zahrah, ki dawo hankalin ki, idan ba kishi ba ne why kike jin zafin aurensa?”
“Wayyooo Allah...” ta faɗa tana dafe kanta da hannayen ta biyu sakamakon yadda kan nata ke juyawa. Daga haka kuma ta yi luuuu ta koma ta baya kamar wacce aka zarewa rai.
Hot love kenan! Su Zahrah yau an yi ƙaramar hauka.
**************************************
Fitowa yayi daga motar kamar wadda aka zarewa laka, a haka ya shiga ciki, Thanks to Allah bai tarar da kowa ba kamar yadda yayi tsammani, a haka ya fara haye benen har ƙafarsa na harɗewa. Daidai Bedroom ɗin da ke nuna mallakinsa ne ya murɗa handle tare da shigewa. Ba tare da ya zare mask ɗin sa ba ya faɗa Bed ɗin.
Numfashin sa ne ke ƙoƙarin kokawa yana shirin barin gangar jikinsa, da ƙyar ya iya cire mask ɗin. Ai ba shiri mai ɗauko report ta ja baya ganin fuskarsa.
Yaya Ishaq ne tabbas sai dai ba wancan Ishaq ɗin da mai karatu ya sani a baya ba ne, wannan Ishaq ɗin wayewa ta bayyana tsantsa a fuskarsa duk da yana cikin tashin hankali.
Wani irin numfashi yake ja tare da fesarwa yana kuma juyi kan katafaren Bed ɗin sa.
“Why angel? Why? Ina kika tafi kika bar Ni? Angel angel! Ko'ina kike in dai a doron duniya kike sai na nemo ki, ke ɗin rayuwa ta ce, na so ko tun baki san kanki ba, ina sonki har yanzu kuma zan kasance mai cigaba da son ki har zuwa numfashi na na ƙarshe, to my last breath angel.!” ya idasa yana fashewa da kuka mai tsuma zuciya.
“Baba don Allah masu gidan nan ko sun yi ƙaura ne?”
Tsohon yace “E to ba zan ce kamai ba amma dai kwanaki na ji mai ɗaki na tana faɗin ko matar gidan ce aka sace ko meye, amaryar gidan kuma kamar dai sun sayar gidan ita da ƴar ta sunyi gaba.”
Zuciyar matashin ne ya tsananta Bugu sakamakon zancen da yake ji daga wurin tsoho. Tattara jarunta da ke shirin barin gangar jikinsa ya yi sannan yace
“To Baba, shi Mai gidan fa?”
“Ai yaro bari in gajarta maka zancen nan, shima Mai gidan babu wanda yasan ina yake.”
“Shikenan ba gode Baba, ga wannan”
Ya faɗa yana miƙo masa kuɗin da ke jikinsa, nan tsoho ya fara godiya, ba tare da ta saurari godiyar ba ya masa sallama tare da nufar motarsa fuskarsa na nuna tsantsar tashin hankali da damuwa, a haka ta figi motar, bai tsaya ko ina ba dai gidansu. Ko da ya Yi parking sai ga Guards ɗin sa sun kewaye shi to see if he's alright saboda taka tsan-tsan da suke da aikin su. Uban gidansu ya musu warning kan shalelen ɗansa, saboda haka ko da ya ce ba zai fita da su ba zaman addu'ar Allah ya dawo da shi lafiya suke yi.
Wannan kenan!
*ABATCHA ESTATE*
*Yayan Lily*
Bayan sallar maghrib ya dawo, kai tsaye part ɗin su ya wuce, sai da yayi wanka tukun ya fito, lokacin kuma Mommah na zaune parlourn ta caɓa uban ado ga kuma yadda ta make fuska babu annuri. Tana ganin fitowar sa ta nufi inda yake.
“Aliyu!” ya dakata jin ta ambaci sunansa sai kuma ya waiwayo yana smiling
“Sannu da gida Mommah”
Ba tare da ta amsa masa ba sai ma cakushe fuska da ta ƙara yi tace
“Aliyu sau nawa zan faɗa maka cewa ka cire zancen auren wannan ƴar iskar a ranka? Me yasa ba ka jin magana ta? Remember Ni Mahaifiyarka ce K kumaum ina da ikon hana wannan auren. Wallahi tun muna shaida juna da arziƙi ka ce musu ka janye!”
Lumshe idanuwansa ya yi ya buɗe waɗanda lokaci guda kuma suka yi jawur, ya gaji da irin wannan hali na mahaifiyarsa, ƙoƙarin controlling temper ɗinsa yayi sannan ya kwantar da Murya
“Mommah Please, ah beg you ki daina batun janye aure, Sanin kan ki ne fa Alhaji Baba da kansa ya yi wannan hukuncin kuma babu wanda ya isa ya ja da shi kin sani, so Please Mommah ki kwantar da hankalin ki kawai ki rungumi ƙaddara.”
A hasale tace
“Na kwantar da hankali na fa kace Aliyu! Ka san kuwa me kake faɗi?”
Ganin ta hau da yawa yasa ya ja hannunta ya zaunar da ita kan ɗaya daga cikin kujerun da ke parlourn sannan ya ɗauki cup da ke kan Centre table ya tsiyaya mata ruwa yana miƙa mata.
“Have this” ganin tana bukatar ruwa yasa ta amsa ta kafa kai, tas ta shanye sannan ta miƙa masa cup ɗin. Ajiyewa yayi shima sai ya zauna gefenta tare da riƙo hannunta, motherhood bond is different, tuni ta fashe da kuka tana faɗin.
“Ni yanzu shikenan so kake na kashe kaina kafin ka haƙura da auren?” ta faɗa sounding so serious.
“Ba Haka ba nee Mommah, get one thing please, cewa sai an fasa aure kin san ba mai yiwuwa ba ne tunda Alhaji da.....”
Katse shi tayi tana ɗaga masa hannu
“Ya isa haka Aliyu! Na gaji da jin fasawa ba zai yiwu ba, na gaji! sai cewa kake Alhaji Baba ne ya yanke hukunci ba zai yiwu ba nace shi Alhaji Baban Allah ne In ya yi hukunci dole a bi? Nace shi ya haifa min haifa min kai ne da zai ke nuna ikonsa a kanka, let him show his power only on his children muma ya bar mu muyi iko da namu!” ta idasa tana share ƙwallar da ke zubo mata.
Handkerchief ɗin sa ya ɗauko yana share mata hawayen
“Is ok Mommah, ya isa kukan kada ki ja ma kanki ciwo, ina riƙon ki da Allah ku kwantar da hankalin ki kada ki yi abun da za ki zubar da ƙimarki cikin gidan nan.”
A ɗan zafafe tace
“Aliyu ƙima? Maganar ƙima naji kana yi? To ai already ba Ni da ita a gidan nan, Im da a ce ina da ita ai da ba za a yanke hukunci a kan dab na ba tare da an bani damar amincewa ko akasin hakan ba. Wallahi Aliyu ko igiyoyin aure na za su tsinke wallahi ba zan bari a yi auren nan ba.”
Tana faɗin haka ta tashi fuu ta nufi Bedroom ɗinta yayin da ta bar Yaya Sadauki kamar statue. Miƙewa shima yayi jiki ba ƙwari ya fice. Direct Masjid ya tafi ko da aka isar kamar kullum ya biyo su Alhaji Baba suka taho tare da sauran Uncles ɗin shi har da waɗanda bai yi tsammanin gani ba. Ko da suka isa a an parlourn suka yada zango har Hajjaty ta fito suka gaisa sannan shima da ke zaune kan carpet ya gaida Uncles ɗin nashi.
Alhaji Baba ne ya unarve su da su tashi a ci abinci sai a lokacin Hajjaty ta lura da ba Zahrah a wajen. Ba ta ce komai ba ta je ta kira Zahrah. A tare suka ƙaraso Zahrah ta ja ma Hajjaty kujera, bayan ya zauna ta fara gaida Uncles ɗin ta suka amsa fuska sake, nan ya Yi serving kowa including her Heart's desire 😳.
*Na san kuna da tarin tambayoyi gare Ni my esteem readers, ku dai kawai mu je zuwa.*
_React and share please._
[12/31/2024, 10:17 PM] Diamond Bhatool:
https://whatsapp.com/channel/0029VanUFkw5kg7G2ci16o2X
*🏡A BABBAN GIDA🏡*
*TAKUN ƘARSHE*
*©Diamond Bhatool*
*💎💍ELITE DIAMOND WRITERS💍💎*
_Where diamonds shine, words ignite_
_Wattpad: @diamond_bhatool_
_Arewabooks: @diamondbhatool3_
Please follow
*PAGE* 2️⃣0️⃣
﷽
Bayan sun gama dinner dukkan su suka dawo parlourn kamar yadda yake. Alhaji Baba bai ware kowa ba, kai tsaye ya fara magana kan dalilin tara su.
“Kamar yadda kuka sani irin wannan kira na gaggawa na ɗauke da ma'anoni mabanbanta, haka zalika yau ma dai na ƙara tara ku saboda wani muhimmin batu, ɓarakar da aka samu a kwanakin baya tsakanin Sadauki da kuma Mabruka ƴar wajen Sadiƙu, na san dukkan ku abun ha jijjiga ku musamman iyaye a ɓangare biyun, ko da ba su nuna wa juna ba tabbas zukatan su sun munana. Dalilin haka ya sa na yanke hukuncin ɗaura aure a tsakaninsu bayan tabbatar da cewa babu komai ɗin da ya faru kawai shiri ne na maƙiya, sai na ga mu toshe bakin maƙiya ta hanyar haɗa auren su zai fi. Ya kuke gani a matsayin ku na iyaye?”
Cike da biyayya kowannensu yayi na'am da hukuncin Alhaji Baba, Nan ya ƙara da faɗin.
“Ma sha Allah, ina ƙara godewa Allah da ya bani ƴaƴa masu tarbiyya waɗanda ba su taɓa ja da hukuncin da na zartar, Ubangiji ya baku masu yi muku biyayya kwatankwacin yadda kuka min.”
Nan suka amsa da “Amin!” Alhaji Baba ya ɗaura da
“Saboda gabatowar azumi nan da wata ɗaya, na yanke ranar bikin cikin makonni biyu ma su zuwa, kowa sai ya fara shirye-shirye.”
Nan gaba ɗaya su Daddy, Appa, Abie da sauran suka fara addu'ar Allah ya sanya alkhairi. Daga nan kuma suka fara taɗin su na ƴaƴan da iyaye.
*Ina Zahrah?*
Tun da ta fahimci akwai abun da za a tattauna ta fara tashi daga dining ɗin sai ta fice daga apartment ɗin ta tsaya bakin ƙofar saboda ta samu damar ji. (Babu kyau gulma fa Zahrah?”
A lokacin da ta ji Alhaji Baba ya ce an yanke ranar bikin Yayanta in 2weeks time ji ta yi kamar an ɗiga mata wani tafasasshen ruwa a zuciyarta. A zabure ta fice ta zagaya ta ƙofar baya, da ƙyar da taimakon Ubangiji ta isa Bedroom ɗinta.
Tana shiga ta faɗa kan Bed ɗin ta tare da fashewa da wani matsanancin kuka, ta rasa ina za ta jefa ranta ta ji sanyi a duniyar nan, ga shi babu kafaɗar wanda za ta kwanta ta zubda ƙwallarta. Nan zuciyarta ta fara tariyo mata moments ɗin da yayanta, why ta yi sauri falling in to his love? Ashe son sa take tsawon lokacin nan?
“No, ba na sonsa, kawai dai ɗan'uwa na ne!” ta faɗa a bayyane.
Da sauri zuciyarta ta ƙaryata ta da faɗin
“Idan har you're not in love with him why kike jin kishinsa?”
Da sauri ta furta
“Kishi? Kishinsa nake?, Noooooo!” ta faɗa tana buga pillown da ke hannunta
“That's impossible!”
Zuciyarta ta ƙara ce mata “Is Possible Zahrah, ki dawo hankalin ki, idan ba kishi ba ne why kike jin zafin aurensa?”
“Wayyooo Allah...” ta faɗa tana dafe kanta da hannayen ta biyu sakamakon yadda kan nata ke juyawa. Daga haka kuma ta yi luuuu ta koma ta baya kamar wacce aka zarewa rai.
Hot love kenan! Su Zahrah yau an yi ƙaramar hauka.
**************************************
Fitowa yayi daga motar kamar wadda aka zarewa laka, a haka ya shiga ciki, Thanks to Allah bai tarar da kowa ba kamar yadda yayi tsammani, a haka ya fara haye benen har ƙafarsa na harɗewa. Daidai Bedroom ɗin da ke nuna mallakinsa ne ya murɗa handle tare da shigewa. Ba tare da ya zare mask ɗin sa ba ya faɗa Bed ɗin.
Numfashin sa ne ke ƙoƙarin kokawa yana shirin barin gangar jikinsa, da ƙyar ya iya cire mask ɗin. Ai ba shiri mai ɗauko report ta ja baya ganin fuskarsa.
Yaya Ishaq ne tabbas sai dai ba wancan Ishaq ɗin da mai karatu ya sani a baya ba ne, wannan Ishaq ɗin wayewa ta bayyana tsantsa a fuskarsa duk da yana cikin tashin hankali.
Wani irin numfashi yake ja tare da fesarwa yana kuma juyi kan katafaren Bed ɗin sa.
“Why angel? Why? Ina kika tafi kika bar Ni? Angel angel! Ko'ina kike in dai a doron duniya kike sai na nemo ki, ke ɗin rayuwa ta ce, na so ko tun baki san kanki ba, ina sonki har yanzu kuma zan kasance mai cigaba da son ki har zuwa numfashi na na ƙarshe, to my last breath angel.!” ya idasa yana fashewa da kuka mai tsuma zuciya.