Sashe 8
A Babban Gida Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*My esteem fans a nuna min ƙauna ta hanyar reacting please, Ina son ku da yawa da yawa, kada ku mance ni ɗin taku ce 🤗 😍 😘 💕*
[10/20, 6:12 PM] Diamond Bhatool:
*Typing 📲*
🏡 *A BABBAN GIDA* 🏡
_(All in a big family 🏠)_
★TAKUN ƘARSHE★
[Labari/Rubutawa]
*Fadimatu Adamu Hassan*💎
*A.k.A Diamond Bhatool*
*(Famanté)*
Wattpad: @diamond_bhatool
Arewabooks: @diamondbhatool
_Ƙirƙirarren labari mai cike da ƴan'uwantaka, gwagwarmayar rayuwa, makirci, mugunta, hassada, munafurci, rashin tausayi da kuma dauwamammiyar soyayya maras iyaka_
_Creative work of love vs. societal expectations., family bonds and loyalty, Identity and self-acceptance, Hypocrisy and jealousy's destructive power._
*PAGE* 0️⃣6️⃣
_Dedicated to Moonlight writer's Association_
_Masu neman labarin daga farko kuyi following channel ɗin nan zaku samu_
﷽
Hira suke sosai abunsu, tuni Zahrah ta saki jiki kamar ba ita ba. Suna cikin hirarsu Nasreen ta ce “Zahrah ajinki nawa ne yanzu?”
Sai a lokacin Zahrah ta tuna da batun wata makaranta. Cikin raunin murya tace “Eh da ina zuwa lokacin da Mama na nan, mun kai SS 2 kuma sai na daina zuwa sosai, amma dai ban gama ba?”
Fuskar Nasreen ɗauke da ayar tambaya tace “Ban gane ba Zahrah?”
Kau da kai gefe Zahrah tayi tana faɗin “Mance kawai Nasreen”
Sauran da basu faɗin komai tun bayan introducing kansu suka haɗa baki wurin faɗin “Haba Zahrah, a mance kuma”
Haka kawai ta ji wani iri ganin sun nuna concern Nasu a kanta, At least sun cancanci su san komai nata.
“Kinyi shiru” Nainarh ta ƙara fada fuakarta fal damuwa.
“Eh am dama fita nayi a makarantar”
Dafa kafaɗarta Zakiyya tayi tace “Feel free, mu nan duka ƴan uwa ki ne Zahrah ”
Rumaysa ta ƙara da faɗin “Ki ɗauke mu kamar yadda muka ɗauke ki Please, mu dukkanmu ƴan uwa kuma ƙawaye muke gare ki, don Allah Zahrah ki faɗa mana”
Zuciyarta ne ta karaya da yadda suke maganar, hakan yasa ta basu labarin Dalilin barinta makaranta.
Sun tausaya mata sosai. Nasreen ta ce “Kada ki damu Zahrah, zaki koma makaranta, makarantar ma wacce ba'a yi tsammani ba, kiyi haƙuri kin ji?” kai ta gyaɗa sai Nainarh ta ce “Ni fa Zahrah wallahi kin matuƙar yi min kama da wata yarinya wacce da take trending a social media, what's that her name?, Rumaysa kin gano yarinyar nan da kwanaki muka ga video nata tana speech lokacin muna JSS three ne kamar dai”
Rumaysa ta ce “Ƙwarai kuwa Nainarh, nima na fuskanci hakan, sunan ta Zahrah ne kamar dai?”
Zakiyya ta ce “Kai wallahi inaga wannan Zahrahn ce, kun san me yasa?”
Duk suka jijjiga kai banda Zahrah da ke binsu da ido.
“Kun tuna lokacin da muka ga news na best in BECE a Bauchi State a parlourn Alhaji Baba?”
Kansu suka ƙara gyaɗa mata.
“To wallahi lokacin nan sai da Alhaji Baba yace anya wannan ba jininsa bace?, amma ke Zahrah daga wane gari kika taho?”
“Bauchi” ta basu amsa a gajarce.
Baki haɗe suka ce “Wallahi ke ce yarinyar nan!”
Ɗan harararsu tayi tace “Sannu manya”
Dariya dukkansu suka yi. Nainarh ta ce “Kada ki damu Zahrah Kinga muma a SS 3 muke yanzu, Kinga sai muyi paper tare kawai, nasan zaki iya ko don irin yadda kwanaki muka ga kina trending a media da gani ke gifted ce”
“Uhm ba wani nan fa”
“Da gaske wallahi ” Zakiyya ta faɗa.
Haka suka yi ta hirarsu nan Zahrah ta basu labarin makarantar su ta da, da yadda aka yi ta fara zuwa. Yadda ta fara haskawa da kuma yadda ta bar makarantar. Sun matuƙar jinjina mata kuma sun mata alƙawarin kasancewa kamar Ƙawarta Badi'a a gare ta. Sosai suka ƙara jin ƙaunar junansu duk da cewa cikin ransu kowa tsoro yake, don zasu iya cewa a iya sashen Hajjaty ne suke samun wannan kusanci da kuma tattaunawa da juna.
****************
Hajiya Babba ce zaune a parlourn ta cikin shiga ta alfarma wacce ke ƙara bayyanar da kwarjininta a idanun mutane. Sallamar Affan ne tasa ta ɗago idanuwanta tana kallonsa. A gaban ta ya zauna yana faɗin “Barka da safiya Hajiya”
“Barka” ta bashi amsa a gajarce. “An gama meeting ɗin kenan?”
“Eh Hajiya an gama” shiru na ɗan wani lokaci ta ce “Masha Allahu, a kan me aka yi zaman ne?”
Fuska dauke da murmushi ya ce “Hajiya kin san wannan ƴar uwar su Alhaji Babba wacce ta ɓatan nan?, Aunty Madina yauwah kamar dai haka sunan yake!”
“eh me ya faru da ita to?” ta faɗa cike da son sanin abunda ke faruwa.
“Hajiya ai ƴarta ce ta dawo, amma ita ɗin an ce ta ɓata ba'a san yadda take ba.”
Cikin halin ko in kula ta ce “To Allah ya bayyana ta.”
Affan ya ce “Amin Hajiya, kin san mene Hajiya?”
Kai ta jijjiga masa “Yarinyar kina ganinta sai ki ce Hajjaty ce ta haife ta.”
Ba tare da ta ɗago ba ta ce “Ayya, ina Nasreen ne?”
Dariya Affan yayi kafin yace “Hajiya ai ƙafar Zahrah ƙafar Nasreen, tana can part ɗin Hajjaty”
Daga haka bata ƙara ce masa komai ba hakan yasa shima ya tashi ya nufi bedroom ɗinsa.
**************
Su uku ne zaune a katafaren Parlourn da alamu dai suna tattauna wani muhimmin zance ne. Mommah ce ta kalli Ammie da Mami ta ce “Nifah ina cikin matsanancin tashin hankali kwanan nan!”
Ido zare Mami ta ce “Lafiya Hajiya Sughrah?”
“To lafiyar dai, kin san har yanzu Aliyu baya ɗaga kira na?, hankali na ya gama tashi, shi ma wannan yaron Khalil bana samun numbersa, Abu ƙarami Aliyu ya ɗauke shi babba.”
Gyara zama Mami tayi ta ce “Kai Ni na rasa wane irin yaro ne wannan, mutum sai shegen taurin zuciya, gaskiya ina ga da sa hannu akan al'amuran sa fa, dole a duba al'amarin nan.”
Jimm kaɗan Mommah ta ce “Gaskiya ina tunanin hakan, Amma ko yaya za'a yi ai bai ƙarfi na ba, Ni na haife shi, zai dawo ya same ni ne, gabaɗaya kwanan nan da ciwon kai nake kwana, ga BP na ma ya hau wallahi.”
Mamie ce tayi gyaran murya ta ce “Ai kuwa Ni ne fara zargin anya ba Bakin Hajiya Babba cikin wannan al'amari kuwa?”
“Nima na fara zargin haka, ban san yaushe Hajiya Babba zata bar kowa ya shana da ƴaƴansa ba a gidan nan, duk ta bi ta maƙalƙale kowa kamar nata. Gaskiya dole muyi kyakkyawan shiri akan wannan al'amari” Ammie ta ƙara a kai, murmushi Mami tayi ta ce “Ni na rasa wane irin boka take bi haka, kiga fa abokan zaman ma kamar tsoronta su ke yi!”
“Yo ba dole ba!” Mommah ta faɗa “Ai dole su ji tsoronta, gadararta fa ita aka fara aura a gidan, ke su ma Hajjaty da Alhaji Baban ba haka ta bar su ba, duk irin yadda take tsula tsiyarta basa magana.”
“Mtss Allah dai yayi mana tsari da ita, ke Ni fa na fara zargin anya ba ita ce da yaranta ke zagon ƙasa ga Abatcha Automobiles ba?” Mami ta faɗa fuska ɗaure wanda ke nuna tsantsar takaicin abunda ke faruwa.
Kwanaki an saci billions of Naira daga asusun Companyn, sannan an saci motoci Masu tsadar gaske da bikes gashi duk binciken da za'a yi an kasa ganowa waye ya ɗauke su.
Haka suka ci gaba da hirarsu sai ga Nainarh ta shigo parlourn, kamar zata yi kuka ganin Mamie da Ammie a part ɗin su. Ta rasa me yake kawo su wurin Mommah ko yaushe, su zo suna zancen waccar masifaffiyar Hajiya Babbar.
Fuska ɗaure ta ƙarasa, ƙasa tayi da murya alamar bata so ta ce “Ina yinin ku”
Baki washe Ammie ta amsa da “Lafiya ƙalau Nainarh, an dawo kenan”. Baki taɓe Nainarh ta ce “Eh” tana ƙoƙarin wucewa. Muryar Mamie ce ta tsayarta tana faɗin “Zo mana Nainarh kamar wacce ake kora?” kamar zata yi kuka ta juya tana faɗin “Gani”
Murmushi Mamie tayi tace “An gama meeting ɗin ne?”
“Laa Kinga Ni har na manta ma da batun meeting ɗin” Ammie ta ƙara.
Kamar bata so ta ce “Eh an gama”
Cike da ƙosawa da tambayar ta ce “Zan ɗan shiga toilet ”
Baki washe Ammie ta ce “Babu komai shiga ki fito mana”
Daga haka Nainarh ta nufi bedroom ɗin ta tana sakin ajiyar zuciya. Tunani sosai take akan rayuwar wannan family nasu, a haka zaka ga kamar cikin farin ciki da ƙaunar juna suke amma a gaskiya babu duka biyun, a da yadda taji ana bada labari ƙalau ake zaune, amma tun wani lokaci da ya shuɗe zaman lafiya ya ƙauracewa wannan family, ga dai duniyar ta samu sai son Barka, abu ɗaya suka rasa shine zaman lafiya da kwanciyar hankali don kuwa daga Wannan sai wancan
Kullum cikin cases ake, yau wannan gobe wancan, an rasa gane ina gaskiya take, saran ɓoyen da ake a gidan ya fara wuce misali. Kowa na zargin kowa, cikin matayen gidan ma babu wata jituwa mai kyau, gidan Alhaji Babba dai suna zamansu ƙalau, amma sauran gidajen kam ba'a magana, wasu kansu haɗe musamman amaren hakan iyayengidajen ma.
Idan muka koma ɓangaren yara kuma Alhamdulillah yawancin su kansu haɗe yake, sai dai wasun ba haka bane. Wasun sun tashi ne kuma an raine su da ƙiyayha da kishin juna, yayinda wasu kuma ke zaune cikin farin ciki da sauran.
[10/20, 6:12 PM] Diamond Bhatool:
*Typing 📲*
🏡 *A BABBAN GIDA* 🏡
_(All in a big family 🏠)_
★TAKUN ƘARSHE★
[Labari/Rubutawa]
*Fadimatu Adamu Hassan*💎
*A.k.A Diamond Bhatool*
*(Famanté)*
Wattpad: @diamond_bhatool
Arewabooks: @diamondbhatool
_Ƙirƙirarren labari mai cike da ƴan'uwantaka, gwagwarmayar rayuwa, makirci, mugunta, hassada, munafurci, rashin tausayi da kuma dauwamammiyar soyayya maras iyaka_
_Creative work of love vs. societal expectations., family bonds and loyalty, Identity and self-acceptance, Hypocrisy and jealousy's destructive power._
*PAGE* 0️⃣6️⃣
_Dedicated to Moonlight writer's Association_
_Masu neman labarin daga farko kuyi following channel ɗin nan zaku samu_
﷽
Hira suke sosai abunsu, tuni Zahrah ta saki jiki kamar ba ita ba. Suna cikin hirarsu Nasreen ta ce “Zahrah ajinki nawa ne yanzu?”
Sai a lokacin Zahrah ta tuna da batun wata makaranta. Cikin raunin murya tace “Eh da ina zuwa lokacin da Mama na nan, mun kai SS 2 kuma sai na daina zuwa sosai, amma dai ban gama ba?”
Fuskar Nasreen ɗauke da ayar tambaya tace “Ban gane ba Zahrah?”
Kau da kai gefe Zahrah tayi tana faɗin “Mance kawai Nasreen”
Sauran da basu faɗin komai tun bayan introducing kansu suka haɗa baki wurin faɗin “Haba Zahrah, a mance kuma”
Haka kawai ta ji wani iri ganin sun nuna concern Nasu a kanta, At least sun cancanci su san komai nata.
“Kinyi shiru” Nainarh ta ƙara fada fuakarta fal damuwa.
“Eh am dama fita nayi a makarantar”
Dafa kafaɗarta Zakiyya tayi tace “Feel free, mu nan duka ƴan uwa ki ne Zahrah ”
Rumaysa ta ƙara da faɗin “Ki ɗauke mu kamar yadda muka ɗauke ki Please, mu dukkanmu ƴan uwa kuma ƙawaye muke gare ki, don Allah Zahrah ki faɗa mana”
Zuciyarta ne ta karaya da yadda suke maganar, hakan yasa ta basu labarin Dalilin barinta makaranta.
Sun tausaya mata sosai. Nasreen ta ce “Kada ki damu Zahrah, zaki koma makaranta, makarantar ma wacce ba'a yi tsammani ba, kiyi haƙuri kin ji?” kai ta gyaɗa sai Nainarh ta ce “Ni fa Zahrah wallahi kin matuƙar yi min kama da wata yarinya wacce da take trending a social media, what's that her name?, Rumaysa kin gano yarinyar nan da kwanaki muka ga video nata tana speech lokacin muna JSS three ne kamar dai”
Rumaysa ta ce “Ƙwarai kuwa Nainarh, nima na fuskanci hakan, sunan ta Zahrah ne kamar dai?”
Zakiyya ta ce “Kai wallahi inaga wannan Zahrahn ce, kun san me yasa?”
Duk suka jijjiga kai banda Zahrah da ke binsu da ido.
“Kun tuna lokacin da muka ga news na best in BECE a Bauchi State a parlourn Alhaji Baba?”
Kansu suka ƙara gyaɗa mata.
“To wallahi lokacin nan sai da Alhaji Baba yace anya wannan ba jininsa bace?, amma ke Zahrah daga wane gari kika taho?”
“Bauchi” ta basu amsa a gajarce.
Baki haɗe suka ce “Wallahi ke ce yarinyar nan!”
Ɗan harararsu tayi tace “Sannu manya”
Dariya dukkansu suka yi. Nainarh ta ce “Kada ki damu Zahrah Kinga muma a SS 3 muke yanzu, Kinga sai muyi paper tare kawai, nasan zaki iya ko don irin yadda kwanaki muka ga kina trending a media da gani ke gifted ce”
“Uhm ba wani nan fa”
“Da gaske wallahi ” Zakiyya ta faɗa.
Haka suka yi ta hirarsu nan Zahrah ta basu labarin makarantar su ta da, da yadda aka yi ta fara zuwa. Yadda ta fara haskawa da kuma yadda ta bar makarantar. Sun matuƙar jinjina mata kuma sun mata alƙawarin kasancewa kamar Ƙawarta Badi'a a gare ta. Sosai suka ƙara jin ƙaunar junansu duk da cewa cikin ransu kowa tsoro yake, don zasu iya cewa a iya sashen Hajjaty ne suke samun wannan kusanci da kuma tattaunawa da juna.
****************
Hajiya Babba ce zaune a parlourn ta cikin shiga ta alfarma wacce ke ƙara bayyanar da kwarjininta a idanun mutane. Sallamar Affan ne tasa ta ɗago idanuwanta tana kallonsa. A gaban ta ya zauna yana faɗin “Barka da safiya Hajiya”
“Barka” ta bashi amsa a gajarce. “An gama meeting ɗin kenan?”
“Eh Hajiya an gama” shiru na ɗan wani lokaci ta ce “Masha Allahu, a kan me aka yi zaman ne?”
Fuska dauke da murmushi ya ce “Hajiya kin san wannan ƴar uwar su Alhaji Babba wacce ta ɓatan nan?, Aunty Madina yauwah kamar dai haka sunan yake!”
“eh me ya faru da ita to?” ta faɗa cike da son sanin abunda ke faruwa.
“Hajiya ai ƴarta ce ta dawo, amma ita ɗin an ce ta ɓata ba'a san yadda take ba.”
Cikin halin ko in kula ta ce “To Allah ya bayyana ta.”
Affan ya ce “Amin Hajiya, kin san mene Hajiya?”
Kai ta jijjiga masa “Yarinyar kina ganinta sai ki ce Hajjaty ce ta haife ta.”
Ba tare da ta ɗago ba ta ce “Ayya, ina Nasreen ne?”
Dariya Affan yayi kafin yace “Hajiya ai ƙafar Zahrah ƙafar Nasreen, tana can part ɗin Hajjaty”
Daga haka bata ƙara ce masa komai ba hakan yasa shima ya tashi ya nufi bedroom ɗinsa.
**************
Su uku ne zaune a katafaren Parlourn da alamu dai suna tattauna wani muhimmin zance ne. Mommah ce ta kalli Ammie da Mami ta ce “Nifah ina cikin matsanancin tashin hankali kwanan nan!”
Ido zare Mami ta ce “Lafiya Hajiya Sughrah?”
“To lafiyar dai, kin san har yanzu Aliyu baya ɗaga kira na?, hankali na ya gama tashi, shi ma wannan yaron Khalil bana samun numbersa, Abu ƙarami Aliyu ya ɗauke shi babba.”
Gyara zama Mami tayi ta ce “Kai Ni na rasa wane irin yaro ne wannan, mutum sai shegen taurin zuciya, gaskiya ina ga da sa hannu akan al'amuran sa fa, dole a duba al'amarin nan.”
Jimm kaɗan Mommah ta ce “Gaskiya ina tunanin hakan, Amma ko yaya za'a yi ai bai ƙarfi na ba, Ni na haife shi, zai dawo ya same ni ne, gabaɗaya kwanan nan da ciwon kai nake kwana, ga BP na ma ya hau wallahi.”
Mamie ce tayi gyaran murya ta ce “Ai kuwa Ni ne fara zargin anya ba Bakin Hajiya Babba cikin wannan al'amari kuwa?”
“Nima na fara zargin haka, ban san yaushe Hajiya Babba zata bar kowa ya shana da ƴaƴansa ba a gidan nan, duk ta bi ta maƙalƙale kowa kamar nata. Gaskiya dole muyi kyakkyawan shiri akan wannan al'amari” Ammie ta ƙara a kai, murmushi Mami tayi ta ce “Ni na rasa wane irin boka take bi haka, kiga fa abokan zaman ma kamar tsoronta su ke yi!”
“Yo ba dole ba!” Mommah ta faɗa “Ai dole su ji tsoronta, gadararta fa ita aka fara aura a gidan, ke su ma Hajjaty da Alhaji Baban ba haka ta bar su ba, duk irin yadda take tsula tsiyarta basa magana.”
“Mtss Allah dai yayi mana tsari da ita, ke Ni fa na fara zargin anya ba ita ce da yaranta ke zagon ƙasa ga Abatcha Automobiles ba?” Mami ta faɗa fuska ɗaure wanda ke nuna tsantsar takaicin abunda ke faruwa.
Kwanaki an saci billions of Naira daga asusun Companyn, sannan an saci motoci Masu tsadar gaske da bikes gashi duk binciken da za'a yi an kasa ganowa waye ya ɗauke su.
Haka suka ci gaba da hirarsu sai ga Nainarh ta shigo parlourn, kamar zata yi kuka ganin Mamie da Ammie a part ɗin su. Ta rasa me yake kawo su wurin Mommah ko yaushe, su zo suna zancen waccar masifaffiyar Hajiya Babbar.
Fuska ɗaure ta ƙarasa, ƙasa tayi da murya alamar bata so ta ce “Ina yinin ku”
Baki washe Ammie ta amsa da “Lafiya ƙalau Nainarh, an dawo kenan”. Baki taɓe Nainarh ta ce “Eh” tana ƙoƙarin wucewa. Muryar Mamie ce ta tsayarta tana faɗin “Zo mana Nainarh kamar wacce ake kora?” kamar zata yi kuka ta juya tana faɗin “Gani”
Murmushi Mamie tayi tace “An gama meeting ɗin ne?”
“Laa Kinga Ni har na manta ma da batun meeting ɗin” Ammie ta ƙara.
Kamar bata so ta ce “Eh an gama”
Cike da ƙosawa da tambayar ta ce “Zan ɗan shiga toilet ”
Baki washe Ammie ta ce “Babu komai shiga ki fito mana”
Daga haka Nainarh ta nufi bedroom ɗin ta tana sakin ajiyar zuciya. Tunani sosai take akan rayuwar wannan family nasu, a haka zaka ga kamar cikin farin ciki da ƙaunar juna suke amma a gaskiya babu duka biyun, a da yadda taji ana bada labari ƙalau ake zaune, amma tun wani lokaci da ya shuɗe zaman lafiya ya ƙauracewa wannan family, ga dai duniyar ta samu sai son Barka, abu ɗaya suka rasa shine zaman lafiya da kwanciyar hankali don kuwa daga Wannan sai wancan
Kullum cikin cases ake, yau wannan gobe wancan, an rasa gane ina gaskiya take, saran ɓoyen da ake a gidan ya fara wuce misali. Kowa na zargin kowa, cikin matayen gidan ma babu wata jituwa mai kyau, gidan Alhaji Babba dai suna zamansu ƙalau, amma sauran gidajen kam ba'a magana, wasu kansu haɗe musamman amaren hakan iyayengidajen ma.
Idan muka koma ɓangaren yara kuma Alhamdulillah yawancin su kansu haɗe yake, sai dai wasun ba haka bane. Wasun sun tashi ne kuma an raine su da ƙiyayha da kishin juna, yayinda wasu kuma ke zaune cikin farin ciki da sauran.