Sashe 38
A Babban Gida Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Dukan wasa suka kai mata
Zakiyya tace
“Uhmm Ni fa ba zan yi auren gida ba, duk da cewa Yaya Taj na mugun burge Ni amma ba na jin zan iya aurensa ko da ace ya furta kalmar so gare ni”
Kama baki Nasreen tayi tace “Baki dai falling ma soyayyarsa ba, tuni kuka ba da kai, ku dai duk ina ganin ku, kowa zan ga ina zai je”
“Lallai Zakiyya ɗan'uwan nawa ne kika cewa ba za ki aura ba?” Rumaysa ta faɗa
“Ni kuwa kinga Ya Auwab yana matuƙar burge Ni wallahi, da zai ce yana so na da gudu zan yadda, mu yi auren mu da mun yi candy”
Baki buɗe Nasreen ke kallon su tace
“Allah ya shirya min ku ƙanne na, amma kun ba Ni kunya, Ni dai har Yanzu ban fara tunanin wani aure ba, la'alla sai zuwa nan gaba. Ke kuma Zahrah yauwah”
Gyara zama suka yi don jin me Nasreen ɗin za ta ce
“Wannan guy ɗin da yayi miki liƙi daga ina rai?”
Rau-rau da ido Zahrah tayi tace
“Wanne kenan?”
Dariya dukkansu suka yi, Rumaysa tace
“Ƴar rainin sense wannan abokin Yaya Sadauki ɗan Sarkin Adamawa.”
Zaro idonta tayi tace “Na shiga uku, rufa min asiri Rumaysa wallahi ban san wani ɗan sarki ba, ku yadda da Ni ƙarya take.” ta faɗa tana bin kowannensu da kallo.
“Is ok, na yadda da Zahrah, Please to sleep don ni na gaji”
Da haka aka rufe zancen kowa ya kwanta.
Washegari around eleven pm sai ga ango da abokansa sun fito gaisuwa, Prince Bello dai ƙyalla ido yake yaga ta ina tauraruwar tasa za ta ɓullo. Part ɗin Hajjaty suka fara zuwa, lokacin da suka shigo kuma Zahrah ta biyo Zakiyya da gudu kan ta ba ta lip balm ai ta riga ta yin wanka. Ba su yi tsammani ba kawai suka ji muryar Yaya Khalil yana faɗin
“Hey girls”
A zabure suka juyo duka su biyun daidai lokacin da Prince yayi tozali da abar begensa.
Cike da kunya suka gaishe su, da sauri Zakiyya ta koma bayan ta faki idonsu, Zahrah na shirin wucewa taji Yaya Sadauki ya ce
“Zahrah Please ki sanar da Hajjaty zuwan nu”
Kai ta gyaɗa tare da wucewa Bedroom ɗin Hajjaty.
Shi kuwa Prince sai maimaita sunan yake a ransa. Murmushi yayi yace
“She must be Zahrah, kyanta, komai nata daban yake da na sauran, i love you”
Tunanin sa ya katse ne da fitowar Hajjaty Zahrah na biye da ita. Kitchen ta nufa ta kawo musu drinks da snacks daga nan ta koma Bedroom nata tana cika tana batsewa wai Rumaysa ta jawo musu Yaya Sadauki ya gan su suna gudu.
Dariya suka yi don ba su ga abun ɓata ran ba, Nainarh ta ajiye wata killer smile kan fuskarta tace “Saura kaɗan”
A tare suka ce “A yi me?” waskewa tayi tace “Nithing ooo, kun san dai this week za a Fara registration na jamb ko?”
“E eh haka fa, wallahi har na manta”
Zahrah tace “Nima dai na manta, ya kamata mu ci serious mu fara karatu don mu samu na tafiya jami'a, au ashe ku kunce daga nan shikenan, to Allah ya kiyaye”
Kallon banza suka bi ta da shi. Nainarh tace “Sai aka ce miki kuma mun gama, ai za mu yi a gidan mazajen mu ko?”
“Allah???” ta ba ta amsa tana sakin dariya daga haka ta janyo school bag nata ta fara fidda littattafai, duk mai son cin serious sai ya min magana don na sa shi a layi, su ooo kuma zan ce Yaya ya siyo muku littafin soyayya ya yi?” ta idasa tana ɗage musu gira.
Shigowar Aunty Na'eema yasa Zahrah tasowa da sauri ta ɗauki babu Aryan sai washe mata baki yake. Da harara Aunty Na'eema ta bi Nainarh
“Shi ne kika bar Ni Ni ɗaya a can ko?”
Dariya Nainarh tayi tace
“Naga Yaya Junaid yana nan”
*React and share please*
[1/16, 5:19 PM] Diamond Bhatool:
*🏡A BABBAN GIDA🏡*
*TAKUN ƘARSHE*
*©Diamond Bhatool*
*💎💍ELITE DIAMOND WRITERS💍💎*
_Where diamonds shine, words ignite_
_Wattpad: @diamond_bhatool_
_Arewabooks: @diamondbhatool3_
Please follow
*PAGE* 2️⃣8️⃣
﷽
Tun da suka fito yake damun Yaya Sadauki akan Zahrah amma ko ƙala bai ce masa ba, kamar maye haka yake ta masa magana.
“Allah AU Abatcha I'm in love with her, and aurenta zan yi, don Allah ka haɗa Ni da ita”
Banza ya ƙara masa amma an ce akan abun da kake so ba ka fushi. Da ya gaji sai ya dawo gun Yaya Khalil,
“Aboki ko ina da wani hali ne da yasa ba za ku bani ita ba, wallahi i do love her with all my heart!”
“Ai ga ka ga ta, babu wanda yayi maka Shamaki da ita”
Amsar da Yaya Khalil ya bayar yasa Yaya Sadauki juyowa ya aika masa da wani irin kallo.
Bayan sun gama da Estate ɗin suka nufi gidan Mommy Nasiba da gida Hajja, sosai Hajja tayi farin ciki da ganin jikan nata sai zuba masa addu'a take yi. Kamar daga sama Mommah ta jiyo muryarsa, su da sauri ta fito don tabbatarwa. Ganin shi ne da gaske cikin manyan kaya da suka mugun yi masa kyau ga wani fresh da yayi yasa ta sauƙe ajiyar zuciya. Ƙarasowa tayi suka gaida ta cike da girmamawa sai ta tsinci kanta da kasa yi masa magana kamar yadda ta kudurta da ta gan shi. Jan ta ƙasa ta juya za ta koma Yaya Khalil yace
“Mommah” ba tare da ta juyo ba tsaya, ko da ya isa sai ya ce “Don Allah Mommah magana nake so mu yi” kasa yi masa musu tayi sai ta nuna masa ɗakinta, gaba tayi ya bi bayanta.
Bayan sun shiga ya sunkuyar da kansa ƙasa sannan ya tsugunna gabanta yace
“Mommah don Allah ki yi haƙuri ki dawo, sai jiya naji ashe kin baro gida, ki yi wa Allah da Manzonsa ki taimaka ki dawo ko dan saboda su Ra'ees, yaron har ya rame saboda rashin ki, don Allah Mommah ki dawo” ta yi niyyar ta hau shi da Masifa ne amma sai ta kasa, hawaye na zubo mata tace
“Ai ba Ni na taho da kai na ba, Daddynsu ne ya ce na dawo, la'alla an gama zaman tunda har yau bai zo ba, In na Kira shi ba ya ɗagawa.”
Kamar zai yi kuka shima yace
“Ki yi haƙuri Mommah, In Sha Allah zan yi wa Alhaji Baba magana za ki dawo, za mu wuce ga wannan.” ya ajiye mata bunch na 1k da ba ta san bawa bane sannan ya wuce. Kuɗin ta ɗaga tana hawaye tace
“Shi ma ya bar Ni, sai abokinsa ne ma ya damu da Ni!”
*Couple of weeks later*
Sosai Yaya Sadauki da Aunty Mabruka suke zaune lafiya, tana ba shi girmansa yadda ya kamata shima kuma yana ganin kimarta, sosai duk su biyun suka yi fresh kamar ba su ba. A safiyar yau yake so ya gana da mutumin da yace ya san yadda Mama take, itama kuma yau take son komawa bakin aikinta, da wuri suka shirya, bayan sun yi breakfast ta fito ɗauke da briefcase nasa a hannunta cikin shigar ta ta lauyoyi. Ganin har ya shiga Mota yasa tayi sauri ta ajiye briefcase ɗin nasa a back seat ta koma ta ɗauko laptop Bata da basket ɗin da ta haɗa masa abinci ko zai ji yunwa tunda yace ba lallai ya dawo da wuri ba. Entrance door ɗin ta rufe sannan ta shiga motar, bayan gateman ya buɗe suka wuce.
Ita ya fara sauƙewa kafin ya tafi ta tuna masa da briefcase nasa da abincin a back seat tukun ta fice tana waving Masa hand. Ko da ta shiga ciki ta haɗu da su Barrister Raudha da Ma'eesha sosai aka buɗe banin hira daga ƙarshe suka buge da zolayarta ko har an samu rabo, murmushi kawai tayi tace “Tukunna dai”
Raudha tace “Allah wannan freshness ya Yi yawa, gaskiya ba ke ɗaya ba.” shashantar da zancen tayi ta mai da hankalinta kan aikin da ke gabanta.
*Zahrah*
Sosai suka mayar da hankalinsu kan karatu, Islamiyya already sun yi sauƙarsu, Zahrah har an ɗauke ta koyarwa a can, kullum Yaya ya kan shigo, idan ta fita ya shigo zai bar sakon zuwansa a hannun Hajjaty. Hidimar da yake mata bai daina ba har yanzu, In ya ga abu zai siya huɗu yace a basu. Ba don ta daina son shi ba haka ta danne zuciyarta ta hakura da shi, ta kuma yi alkawarin ko da wasa ba za ta ƙara barin so ya yaudare ta ba, In fact ba ma za tai sake ba, babu ruwan ta da kowa, karatun ta shine a gabanta.
*Yaya Sadauki*
Duk da cewa yana kewar Mommahnsa amma ya yi alkawarin ma Daddy cewa ba zai je gurin ta ba, hak Hajja ma ta sa shi ya ɗau alƙawarin nan. Ko da ya isa kan abinda ya kai shi ya sauƙa. Ko five minutes da zuwansa ba'a yi ba sai ga mutumin ya zo, bayan izinin shiga da ya samu ya shiga ya zauna. Ganin babban mutum ne yasa Yaya Sadauki gaida shi cike da girmamawa. Bayan ya amsa yace
“Baba kai ne aka ce ka san yadda wannan baiwar Allahn take?”
Murmushi tsohon yayi yace
“Ƙwarai kuwa, Madina dai mai masa a kasuwa da naje garin iyaye na can Toro kwana biyu da suka wuce na ganta, har muka gaisa, na tambaye ta yarinyar ta da suke zuwa kasuwar tare tace ai tana tare da iyayenta.”
Ajiyar zuciya Yaya Sadauki ya sauƙe yana faɗin
“To Baba yanzu ma za mu biya maka kuɗin jirgi ka koma, za ku je can ɗin da Detective Musa Wanda yake riƙe da case ɗin, ina dai ka san takamaimai inda take?”
“Ƙwarai kuwa” ya ba shi amsa “Ai da jikokin Cikin umma ta na gan su.”
Zakiyya tace
“Uhmm Ni fa ba zan yi auren gida ba, duk da cewa Yaya Taj na mugun burge Ni amma ba na jin zan iya aurensa ko da ace ya furta kalmar so gare ni”
Kama baki Nasreen tayi tace “Baki dai falling ma soyayyarsa ba, tuni kuka ba da kai, ku dai duk ina ganin ku, kowa zan ga ina zai je”
“Lallai Zakiyya ɗan'uwan nawa ne kika cewa ba za ki aura ba?” Rumaysa ta faɗa
“Ni kuwa kinga Ya Auwab yana matuƙar burge Ni wallahi, da zai ce yana so na da gudu zan yadda, mu yi auren mu da mun yi candy”
Baki buɗe Nasreen ke kallon su tace
“Allah ya shirya min ku ƙanne na, amma kun ba Ni kunya, Ni dai har Yanzu ban fara tunanin wani aure ba, la'alla sai zuwa nan gaba. Ke kuma Zahrah yauwah”
Gyara zama suka yi don jin me Nasreen ɗin za ta ce
“Wannan guy ɗin da yayi miki liƙi daga ina rai?”
Rau-rau da ido Zahrah tayi tace
“Wanne kenan?”
Dariya dukkansu suka yi, Rumaysa tace
“Ƴar rainin sense wannan abokin Yaya Sadauki ɗan Sarkin Adamawa.”
Zaro idonta tayi tace “Na shiga uku, rufa min asiri Rumaysa wallahi ban san wani ɗan sarki ba, ku yadda da Ni ƙarya take.” ta faɗa tana bin kowannensu da kallo.
“Is ok, na yadda da Zahrah, Please to sleep don ni na gaji”
Da haka aka rufe zancen kowa ya kwanta.
Washegari around eleven pm sai ga ango da abokansa sun fito gaisuwa, Prince Bello dai ƙyalla ido yake yaga ta ina tauraruwar tasa za ta ɓullo. Part ɗin Hajjaty suka fara zuwa, lokacin da suka shigo kuma Zahrah ta biyo Zakiyya da gudu kan ta ba ta lip balm ai ta riga ta yin wanka. Ba su yi tsammani ba kawai suka ji muryar Yaya Khalil yana faɗin
“Hey girls”
A zabure suka juyo duka su biyun daidai lokacin da Prince yayi tozali da abar begensa.
Cike da kunya suka gaishe su, da sauri Zakiyya ta koma bayan ta faki idonsu, Zahrah na shirin wucewa taji Yaya Sadauki ya ce
“Zahrah Please ki sanar da Hajjaty zuwan nu”
Kai ta gyaɗa tare da wucewa Bedroom ɗin Hajjaty.
Shi kuwa Prince sai maimaita sunan yake a ransa. Murmushi yayi yace
“She must be Zahrah, kyanta, komai nata daban yake da na sauran, i love you”
Tunanin sa ya katse ne da fitowar Hajjaty Zahrah na biye da ita. Kitchen ta nufa ta kawo musu drinks da snacks daga nan ta koma Bedroom nata tana cika tana batsewa wai Rumaysa ta jawo musu Yaya Sadauki ya gan su suna gudu.
Dariya suka yi don ba su ga abun ɓata ran ba, Nainarh ta ajiye wata killer smile kan fuskarta tace “Saura kaɗan”
A tare suka ce “A yi me?” waskewa tayi tace “Nithing ooo, kun san dai this week za a Fara registration na jamb ko?”
“E eh haka fa, wallahi har na manta”
Zahrah tace “Nima dai na manta, ya kamata mu ci serious mu fara karatu don mu samu na tafiya jami'a, au ashe ku kunce daga nan shikenan, to Allah ya kiyaye”
Kallon banza suka bi ta da shi. Nainarh tace “Sai aka ce miki kuma mun gama, ai za mu yi a gidan mazajen mu ko?”
“Allah???” ta ba ta amsa tana sakin dariya daga haka ta janyo school bag nata ta fara fidda littattafai, duk mai son cin serious sai ya min magana don na sa shi a layi, su ooo kuma zan ce Yaya ya siyo muku littafin soyayya ya yi?” ta idasa tana ɗage musu gira.
Shigowar Aunty Na'eema yasa Zahrah tasowa da sauri ta ɗauki babu Aryan sai washe mata baki yake. Da harara Aunty Na'eema ta bi Nainarh
“Shi ne kika bar Ni Ni ɗaya a can ko?”
Dariya Nainarh tayi tace
“Naga Yaya Junaid yana nan”
*React and share please*
[1/16, 5:19 PM] Diamond Bhatool:
*🏡A BABBAN GIDA🏡*
*TAKUN ƘARSHE*
*©Diamond Bhatool*
*💎💍ELITE DIAMOND WRITERS💍💎*
_Where diamonds shine, words ignite_
_Wattpad: @diamond_bhatool_
_Arewabooks: @diamondbhatool3_
Please follow
*PAGE* 2️⃣8️⃣
﷽
Tun da suka fito yake damun Yaya Sadauki akan Zahrah amma ko ƙala bai ce masa ba, kamar maye haka yake ta masa magana.
“Allah AU Abatcha I'm in love with her, and aurenta zan yi, don Allah ka haɗa Ni da ita”
Banza ya ƙara masa amma an ce akan abun da kake so ba ka fushi. Da ya gaji sai ya dawo gun Yaya Khalil,
“Aboki ko ina da wani hali ne da yasa ba za ku bani ita ba, wallahi i do love her with all my heart!”
“Ai ga ka ga ta, babu wanda yayi maka Shamaki da ita”
Amsar da Yaya Khalil ya bayar yasa Yaya Sadauki juyowa ya aika masa da wani irin kallo.
Bayan sun gama da Estate ɗin suka nufi gidan Mommy Nasiba da gida Hajja, sosai Hajja tayi farin ciki da ganin jikan nata sai zuba masa addu'a take yi. Kamar daga sama Mommah ta jiyo muryarsa, su da sauri ta fito don tabbatarwa. Ganin shi ne da gaske cikin manyan kaya da suka mugun yi masa kyau ga wani fresh da yayi yasa ta sauƙe ajiyar zuciya. Ƙarasowa tayi suka gaida ta cike da girmamawa sai ta tsinci kanta da kasa yi masa magana kamar yadda ta kudurta da ta gan shi. Jan ta ƙasa ta juya za ta koma Yaya Khalil yace
“Mommah” ba tare da ta juyo ba tsaya, ko da ya isa sai ya ce “Don Allah Mommah magana nake so mu yi” kasa yi masa musu tayi sai ta nuna masa ɗakinta, gaba tayi ya bi bayanta.
Bayan sun shiga ya sunkuyar da kansa ƙasa sannan ya tsugunna gabanta yace
“Mommah don Allah ki yi haƙuri ki dawo, sai jiya naji ashe kin baro gida, ki yi wa Allah da Manzonsa ki taimaka ki dawo ko dan saboda su Ra'ees, yaron har ya rame saboda rashin ki, don Allah Mommah ki dawo” ta yi niyyar ta hau shi da Masifa ne amma sai ta kasa, hawaye na zubo mata tace
“Ai ba Ni na taho da kai na ba, Daddynsu ne ya ce na dawo, la'alla an gama zaman tunda har yau bai zo ba, In na Kira shi ba ya ɗagawa.”
Kamar zai yi kuka shima yace
“Ki yi haƙuri Mommah, In Sha Allah zan yi wa Alhaji Baba magana za ki dawo, za mu wuce ga wannan.” ya ajiye mata bunch na 1k da ba ta san bawa bane sannan ya wuce. Kuɗin ta ɗaga tana hawaye tace
“Shi ma ya bar Ni, sai abokinsa ne ma ya damu da Ni!”
*Couple of weeks later*
Sosai Yaya Sadauki da Aunty Mabruka suke zaune lafiya, tana ba shi girmansa yadda ya kamata shima kuma yana ganin kimarta, sosai duk su biyun suka yi fresh kamar ba su ba. A safiyar yau yake so ya gana da mutumin da yace ya san yadda Mama take, itama kuma yau take son komawa bakin aikinta, da wuri suka shirya, bayan sun yi breakfast ta fito ɗauke da briefcase nasa a hannunta cikin shigar ta ta lauyoyi. Ganin har ya shiga Mota yasa tayi sauri ta ajiye briefcase ɗin nasa a back seat ta koma ta ɗauko laptop Bata da basket ɗin da ta haɗa masa abinci ko zai ji yunwa tunda yace ba lallai ya dawo da wuri ba. Entrance door ɗin ta rufe sannan ta shiga motar, bayan gateman ya buɗe suka wuce.
Ita ya fara sauƙewa kafin ya tafi ta tuna masa da briefcase nasa da abincin a back seat tukun ta fice tana waving Masa hand. Ko da ta shiga ciki ta haɗu da su Barrister Raudha da Ma'eesha sosai aka buɗe banin hira daga ƙarshe suka buge da zolayarta ko har an samu rabo, murmushi kawai tayi tace “Tukunna dai”
Raudha tace “Allah wannan freshness ya Yi yawa, gaskiya ba ke ɗaya ba.” shashantar da zancen tayi ta mai da hankalinta kan aikin da ke gabanta.
*Zahrah*
Sosai suka mayar da hankalinsu kan karatu, Islamiyya already sun yi sauƙarsu, Zahrah har an ɗauke ta koyarwa a can, kullum Yaya ya kan shigo, idan ta fita ya shigo zai bar sakon zuwansa a hannun Hajjaty. Hidimar da yake mata bai daina ba har yanzu, In ya ga abu zai siya huɗu yace a basu. Ba don ta daina son shi ba haka ta danne zuciyarta ta hakura da shi, ta kuma yi alkawarin ko da wasa ba za ta ƙara barin so ya yaudare ta ba, In fact ba ma za tai sake ba, babu ruwan ta da kowa, karatun ta shine a gabanta.
*Yaya Sadauki*
Duk da cewa yana kewar Mommahnsa amma ya yi alkawarin ma Daddy cewa ba zai je gurin ta ba, hak Hajja ma ta sa shi ya ɗau alƙawarin nan. Ko da ya isa kan abinda ya kai shi ya sauƙa. Ko five minutes da zuwansa ba'a yi ba sai ga mutumin ya zo, bayan izinin shiga da ya samu ya shiga ya zauna. Ganin babban mutum ne yasa Yaya Sadauki gaida shi cike da girmamawa. Bayan ya amsa yace
“Baba kai ne aka ce ka san yadda wannan baiwar Allahn take?”
Murmushi tsohon yayi yace
“Ƙwarai kuwa, Madina dai mai masa a kasuwa da naje garin iyaye na can Toro kwana biyu da suka wuce na ganta, har muka gaisa, na tambaye ta yarinyar ta da suke zuwa kasuwar tare tace ai tana tare da iyayenta.”
Ajiyar zuciya Yaya Sadauki ya sauƙe yana faɗin
“To Baba yanzu ma za mu biya maka kuɗin jirgi ka koma, za ku je can ɗin da Detective Musa Wanda yake riƙe da case ɗin, ina dai ka san takamaimai inda take?”
“Ƙwarai kuwa” ya ba shi amsa “Ai da jikokin Cikin umma ta na gan su.”