Sashe 42
A Babban Gida Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ajiyar zuciya Yaya Khalil ya sau'ke ganin convoy na motocin iyayensu sun shigo. Juyawa yayi ba tare da ya motsa daga yadda yake ba yayin da su kuma gabansu ya yanke da juyawarsa ba tare da ya amsa tambayar Hajjaty ba. A tsanake suka fito fuskarsu kame kamar ba abunda ke damunsu, sai dai fuskar Papa da Alhaji Babba ba ta iya 'boye yanayin da suke ciki. Haka suka tunkaro part 'din Hajjatyn a jere, abun da ya 'daurewa Hajjaty kai shine babu wanda yayi magana, ganin hakan yasa Alhaji Baba da ya kasa furta komai bayan bugun zuciyarsa da yake saurara ya ce
"Mu shiga ciki"
Babu musu suka bi bayansa kowa ya koma, a matu'kar tsorace kowa yake ta yadda za ka fahimci hakan parlourn ya koma kamar wani graveyard ko sautin numfarfashinsu ba a ji yayin da kowa idanuwansa ke 'kasa.
Cike da dakiya Daddy ya yi sallama, bayan sun amsa ya fara jawabi.
"Kamar yadda muka sani duk abunda ya faru da bawa mu'kaddari ne daga mahaliccinsa, ita 'kaddara kan zowa kowa ta fuskoki mabanbanta, kada mu mance duk abunda ya faru da bawa to a rubuce yake cikin zanen rayuwarsa, babu yadda kuma bawa zai yi ya tsallake abunda ubangiji ya gindaya a kansa."
Shiru yayi yayin da zuciyarsa ke wani irin bugu, cike da danne emotions nasa ya bu'de baki zi ci gaba, ku kiyasta cewa ku ne a wannan mataki kuke jiran jin me Daddy zai fa'da, kamar haka su ma mutanen da ke zaune a parlourn suka shiga hali irin na ru'du musamman wa'danda ba su san me yake faruwa ba.
"Ubaniji shi ke da ikon busa mana numfashi haka kuma yana da damar ya tsayar da shi a lokacin da yaso saboda cikar wa'adin numfashin da ya rubuta za mu yi tsawon rayuwarmu! Ubangiji kan 'dauki ran wani daga cikin mutane ba don ba ya son sa ba, kamar yadda ya 'dauke ran habibinsa kuma shugabanmu Annabi muhammad, zai iya 'daukar kowa duk kuwa yadda mutane ke tsananin sonsa, ko da kuwa duk duniya za su sadaukar da numfashin su saboda wannan rai 'daya, ubangiji ba zai dakatar da 'kudurinsa ba."
Shiru ya kuma yi, i zuwa wannan lokaci hankalin duk wani mazaunin parlourn ya kai ga 'kololuwar tashi yayin da masu raunin cikinsu suke share hawaye saboda zukatansu ba za su iya 'daukar wannan al'amari ba.
*React and share please*
[1/22, 4:40 PM] Diamond Bhatool:
*🏡A BABBAN GIDA🏡*
*TAKUN ƘARSHE*
*©Diamond Bhatool*
*💎💍ELITE DIAMOND WRITERS💍💎*
_Where diamonds shine, words ignite_
_Wattpad: @diamond_bhatool_
_Arewabooks: @diamondbhatool3_
Please follow
*PAGE* 3️⃣1️⃣
﷽
Shi kansa Daddy a wannan ga'bar jarumtarsa ta kusa gushewa, muryarsa na rawa ya ci gaba da magana.
"Na san kun 'kosa ku ji meyasa nake wannan dogon sharhi, ina so ku dubi maganganu na ku musu kyakkyawar fahimta, ku yi imani da 'kaddara mai kyau ko akasin haka, ku amshe ta hannu biyu kada ku yiwa ubangiji butulci."
Hajjaty da zuwa yanzu jikinta ke karkarwa ga yadda zuciyarta ta yanke tace
"Muna sauraronka Umar, ka fa'da mana me yake faruwa."
Murmushin da na kasa fahimtar na meye Daddy yayi, shi ka'dai yasan yadda zuciyarsa ke yi. Daurewa yayi yace.
"Tabbas mun yi babban rashi cikin wannan family, mun tafka rashi wanda in mun kar'ba da hannu biyu hala ubangiji ya kawo mana kwatankwanci."
"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'una" gaba'daya parlourn ya 'dau salallami, wa'danda ba sa kuka ma tuni sun fara saboda yadda sa'kon rashi ya bugi zuciyarsutun kafin su ji wanene ma ya Rasu.
Shima Daddy sai da ya faki idanuwansu ya share 'kwallar da ta zubo masa.
"Ubangijin da ya ba mu Sadauki yau ya 'dauki abunsa sakamakon ha'darin jirgin sama da ya afku, a halin yanzu babu abunda yake bu'kata daga gare mu matsayin masoyansa face addu'a, babu shakka kowanne mai rai mamaci ne."
Yana gama rufe bakinsa Hajjaty ta sulale 'kasa sumammiya, Alhaji Baba kam hawaye ne kawai ke sintiri daga idanuwansa. Shikenan! Shikenan ya rasa jikansa mafi soyuwa gare shi?
Zahrah kuwa tun lokacin da kalaman Daddy na 'karshe suka doki kunnenta ta daina fahimtar komai, nan duniyar tafara juya mata, kafin kace me ita ma ta sulale 'kasa sumammiya.
Wa'danda suka zubda 'kwalla su godewa Allah atleast sun rage wani kashi na tarin damuwarsu, har wannan lokaci ko 'digon 'kwalla ba ta zubo daga idanuwansa ba, ra'da'din da yake ji ba zai misaltu ba saboda duk duniya babu wanda ya sha'ku da shi sama da shi, tun ba su da hankali suke tare har zuwa wannan lokaci amma mutuwa ta yi musu yankan 'kauna, a rikice ya nufi Hajjaty da idonsa ya fara kaiwa gare ta kafin ya juyo 'daya 'bangaren da Zahrah da kuma Nainarh ke yashe 'kasa, Ransu na shirin barin gangar jikinsu.
Alhaji Babba da kuma Papa wannan mutuwa ta kaf 'daya ta bugi zukatansu haka nan Abba da saura kawunnan mamacin, ba 'karamar dauriya Daddy yayi ba saboda ya kwantar musu da hankali don ba lallai a samu wanda ya kai shi jin ra'da'din rasa nagartaccen 'dan nasa ba. Ganin yadda wasu suka fara fita hayyacinsu yasa ya 'daga waya ya 'kira aka turo ambulance don tafiya da Hajjaty, Nainarh da kuma Zahrah wa'danda suke sume, bayan an wuce da su asibiti ne kowannensu ya koma 'bangarensa don gobe da sassafe suke sa ran wucewa takamaimai wurin da za a samu pieces na jirgin la'alla ko za a samu gawarsa, in ba a samu ba kuma sai a yi masa salatul ga'ib.
Tabbas wannan rana ta shiga tarihin wannan ahali musamman da suka tafka babban rashi wanda kai tsaye za mu iya 'kiransa da 'kaddararsu, shikenan fa ya tafi, babu wanda zai kuma kallonsa a wannan gida na duniya, Allah sarki rayuwa. Amma duk da haka ana sa masa ran dacewa ne saboda shaidar da ya samu. Mutuwarsa in sha Allah hutu ce, ba ya shiga ha'k'kin kowa, ba ya zaluntar kowa kuma tsakaninsa da mahallincinsa ma ana kyautata zaton kyakkyawar mu'amala ce, ya gama aikin alkhairi, da azumi a bakinsa wannan abu ya afka masa.
Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, ubangiji ya ji'kan Yaya Sadauki yasa aljanna ce makomarsa. Tabbas kowanne mai rai sai ya 'dan'dana mutuwa, ina wa'danda suka shagala da duniya? Kuna ganin irin wannan mutuwa bagtatan kuwa?, ga dai Yaya Sadaukin nan da safiyar Allah kakanninsa sun gana da shi, haka kuma Zahrah da take da rabo, ya yi wa matarsa sallama lafiya lau yanzu ga shi ana labarin mutuwarsa, ya zama tarihi kuma.
Ya kamata mu 'kara kyautata ala'karmu da mahalicci haka nan kuma da mutane, muna tuna mutuwa, muke sanya ta a agenda namu, mu sa a ranmu in mun wayi gari lafiya ba lallai mu yammace da ran mu ba, haka nan in mun kai yammaci mu sa a ranmu ba lallai mu kasance raye ba safiya ta gaba. Wannan zai 'kara sa mu 'kara kusantuwa ga mahaliccinmu. Allah yasa mu dace, wa'danda suka riga mu gidan gaskiya tun daga kan al'ummar farko zuwa yanzu muna ro'kom ubangiji ya musu rahama, idan tamu mutuwar ta zo ubangiji ya sa mu cika da imani.
Kafin 9:00pm tuni mutuwar ta zaga kowanne sa'ko na ahalin kama daga na cikin gida da wa'danda ke nesa da gidan, mutuwar da ta ratsa zukatan mutane da dama yayin da ta zama sulhu ga wasu, ta kuma zama abun farin ciki a zukatan wasu sai dai su ma kada su manta ba tabbata za su yi a doron duniyar ba.
Sosai ABATCHA ESTATE ya zama tamkar ma'kabarta, kowanne sashe shiru yake kowa na 'kara jimamin mutuwar yana hawaye irin na yankan 'kauna, ba iya ahalin gidan ba hatta ma'aikatan gidan sun matu'kar razana da mutuwar Yaya Sadauki, sun yi kuka tamkar wa'danda suka rasa wane sashe na jikinsu, kai dole ma su yi kukan don kuwa ba lallai Marigayi ya mu'amalance ka ba ka ji 'kaunarsa cikin ranka ba, yana da salon mutuntawa da iya mu'amala. Saboda yanayin Alhaji Baba yasa Daddy ya zauna a tare da shi, Yaya Khalil da kuma Hajiya Babba suka wuce asibitin don zama kusa da marasa lafiyan, sai a lokacin ne Humairah ta koma, a nan kuma Hajiya Babba ta san da cewa Mabrukan ma ashe tana nan.
Duk wanda ya farfa'do cikinsu da zarar ya tuna da event 'din da ya faru sai ya koma, haka dai wannan dare ya kasance ga wa'dannan mutane uku, sai dai kuma wa'danda ke jinyar sosai zukatansu suka fi raunana, gwanda Hajiya Babba ta zubarda hawaye, Yaya Khalil kam ba a magana illa iyaka dai idanuwansa sun sauya daga wa'dannan fararen zuwa jajaye kamar gauta ga kuma yadda suke masa zafi kamar ana hura wuta a ciki, zafin da suke masa kuma in za a kwatanta shi da wadda zuciyarsa ke yi ba a magana, jijiyoyin kansa sun fito ru'du-ru'du. A hakan idan Hajiya ta gama kukanta sai kuma ta hau masa nasiha. Addu'a kuwa daren ranar ya sha ta daga masoyansa.
Wannan dare dai ya yawaita tsayi tamkar an dakatar da tafiyar lokaci haka suke gani ko dan saboda kashi 98% nasu ba su rintsa bane, sahur na azumin washegari ya gagara har alfijr ya keto. Bayan sallar asuba kai tsaye iyaye mazan banda Daddy da ke tare da Alhaji Baba suka fice daga gidan don nemo gawarsa shima a masa sutura a mi'ka shi gidansa na gaskiya. Allah ya masa rahama.
Washegari da safe su Aunty Madina suka diro, su Yaya Haidar da Yaya Junaid tare da ahalinsu su ma suna hanyarsu ta zuwa tunda sa'kon ya kai gare su, sai dai ba su wani 'daga hankali akai ba saboda ba su yadda da zancen mutuwar tasa ba.
"Mu shiga ciki"
Babu musu suka bi bayansa kowa ya koma, a matu'kar tsorace kowa yake ta yadda za ka fahimci hakan parlourn ya koma kamar wani graveyard ko sautin numfarfashinsu ba a ji yayin da kowa idanuwansa ke 'kasa.
Cike da dakiya Daddy ya yi sallama, bayan sun amsa ya fara jawabi.
"Kamar yadda muka sani duk abunda ya faru da bawa mu'kaddari ne daga mahaliccinsa, ita 'kaddara kan zowa kowa ta fuskoki mabanbanta, kada mu mance duk abunda ya faru da bawa to a rubuce yake cikin zanen rayuwarsa, babu yadda kuma bawa zai yi ya tsallake abunda ubangiji ya gindaya a kansa."
Shiru yayi yayin da zuciyarsa ke wani irin bugu, cike da danne emotions nasa ya bu'de baki zi ci gaba, ku kiyasta cewa ku ne a wannan mataki kuke jiran jin me Daddy zai fa'da, kamar haka su ma mutanen da ke zaune a parlourn suka shiga hali irin na ru'du musamman wa'danda ba su san me yake faruwa ba.
"Ubaniji shi ke da ikon busa mana numfashi haka kuma yana da damar ya tsayar da shi a lokacin da yaso saboda cikar wa'adin numfashin da ya rubuta za mu yi tsawon rayuwarmu! Ubangiji kan 'dauki ran wani daga cikin mutane ba don ba ya son sa ba, kamar yadda ya 'dauke ran habibinsa kuma shugabanmu Annabi muhammad, zai iya 'daukar kowa duk kuwa yadda mutane ke tsananin sonsa, ko da kuwa duk duniya za su sadaukar da numfashin su saboda wannan rai 'daya, ubangiji ba zai dakatar da 'kudurinsa ba."
Shiru ya kuma yi, i zuwa wannan lokaci hankalin duk wani mazaunin parlourn ya kai ga 'kololuwar tashi yayin da masu raunin cikinsu suke share hawaye saboda zukatansu ba za su iya 'daukar wannan al'amari ba.
*React and share please*
[1/22, 4:40 PM] Diamond Bhatool:
*🏡A BABBAN GIDA🏡*
*TAKUN ƘARSHE*
*©Diamond Bhatool*
*💎💍ELITE DIAMOND WRITERS💍💎*
_Where diamonds shine, words ignite_
_Wattpad: @diamond_bhatool_
_Arewabooks: @diamondbhatool3_
Please follow
*PAGE* 3️⃣1️⃣
﷽
Shi kansa Daddy a wannan ga'bar jarumtarsa ta kusa gushewa, muryarsa na rawa ya ci gaba da magana.
"Na san kun 'kosa ku ji meyasa nake wannan dogon sharhi, ina so ku dubi maganganu na ku musu kyakkyawar fahimta, ku yi imani da 'kaddara mai kyau ko akasin haka, ku amshe ta hannu biyu kada ku yiwa ubangiji butulci."
Hajjaty da zuwa yanzu jikinta ke karkarwa ga yadda zuciyarta ta yanke tace
"Muna sauraronka Umar, ka fa'da mana me yake faruwa."
Murmushin da na kasa fahimtar na meye Daddy yayi, shi ka'dai yasan yadda zuciyarsa ke yi. Daurewa yayi yace.
"Tabbas mun yi babban rashi cikin wannan family, mun tafka rashi wanda in mun kar'ba da hannu biyu hala ubangiji ya kawo mana kwatankwanci."
"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'una" gaba'daya parlourn ya 'dau salallami, wa'danda ba sa kuka ma tuni sun fara saboda yadda sa'kon rashi ya bugi zuciyarsutun kafin su ji wanene ma ya Rasu.
Shima Daddy sai da ya faki idanuwansu ya share 'kwallar da ta zubo masa.
"Ubangijin da ya ba mu Sadauki yau ya 'dauki abunsa sakamakon ha'darin jirgin sama da ya afku, a halin yanzu babu abunda yake bu'kata daga gare mu matsayin masoyansa face addu'a, babu shakka kowanne mai rai mamaci ne."
Yana gama rufe bakinsa Hajjaty ta sulale 'kasa sumammiya, Alhaji Baba kam hawaye ne kawai ke sintiri daga idanuwansa. Shikenan! Shikenan ya rasa jikansa mafi soyuwa gare shi?
Zahrah kuwa tun lokacin da kalaman Daddy na 'karshe suka doki kunnenta ta daina fahimtar komai, nan duniyar tafara juya mata, kafin kace me ita ma ta sulale 'kasa sumammiya.
Wa'danda suka zubda 'kwalla su godewa Allah atleast sun rage wani kashi na tarin damuwarsu, har wannan lokaci ko 'digon 'kwalla ba ta zubo daga idanuwansa ba, ra'da'din da yake ji ba zai misaltu ba saboda duk duniya babu wanda ya sha'ku da shi sama da shi, tun ba su da hankali suke tare har zuwa wannan lokaci amma mutuwa ta yi musu yankan 'kauna, a rikice ya nufi Hajjaty da idonsa ya fara kaiwa gare ta kafin ya juyo 'daya 'bangaren da Zahrah da kuma Nainarh ke yashe 'kasa, Ransu na shirin barin gangar jikinsu.
Alhaji Babba da kuma Papa wannan mutuwa ta kaf 'daya ta bugi zukatansu haka nan Abba da saura kawunnan mamacin, ba 'karamar dauriya Daddy yayi ba saboda ya kwantar musu da hankali don ba lallai a samu wanda ya kai shi jin ra'da'din rasa nagartaccen 'dan nasa ba. Ganin yadda wasu suka fara fita hayyacinsu yasa ya 'daga waya ya 'kira aka turo ambulance don tafiya da Hajjaty, Nainarh da kuma Zahrah wa'danda suke sume, bayan an wuce da su asibiti ne kowannensu ya koma 'bangarensa don gobe da sassafe suke sa ran wucewa takamaimai wurin da za a samu pieces na jirgin la'alla ko za a samu gawarsa, in ba a samu ba kuma sai a yi masa salatul ga'ib.
Tabbas wannan rana ta shiga tarihin wannan ahali musamman da suka tafka babban rashi wanda kai tsaye za mu iya 'kiransa da 'kaddararsu, shikenan fa ya tafi, babu wanda zai kuma kallonsa a wannan gida na duniya, Allah sarki rayuwa. Amma duk da haka ana sa masa ran dacewa ne saboda shaidar da ya samu. Mutuwarsa in sha Allah hutu ce, ba ya shiga ha'k'kin kowa, ba ya zaluntar kowa kuma tsakaninsa da mahallincinsa ma ana kyautata zaton kyakkyawar mu'amala ce, ya gama aikin alkhairi, da azumi a bakinsa wannan abu ya afka masa.
Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, ubangiji ya ji'kan Yaya Sadauki yasa aljanna ce makomarsa. Tabbas kowanne mai rai sai ya 'dan'dana mutuwa, ina wa'danda suka shagala da duniya? Kuna ganin irin wannan mutuwa bagtatan kuwa?, ga dai Yaya Sadaukin nan da safiyar Allah kakanninsa sun gana da shi, haka kuma Zahrah da take da rabo, ya yi wa matarsa sallama lafiya lau yanzu ga shi ana labarin mutuwarsa, ya zama tarihi kuma.
Ya kamata mu 'kara kyautata ala'karmu da mahalicci haka nan kuma da mutane, muna tuna mutuwa, muke sanya ta a agenda namu, mu sa a ranmu in mun wayi gari lafiya ba lallai mu yammace da ran mu ba, haka nan in mun kai yammaci mu sa a ranmu ba lallai mu kasance raye ba safiya ta gaba. Wannan zai 'kara sa mu 'kara kusantuwa ga mahaliccinmu. Allah yasa mu dace, wa'danda suka riga mu gidan gaskiya tun daga kan al'ummar farko zuwa yanzu muna ro'kom ubangiji ya musu rahama, idan tamu mutuwar ta zo ubangiji ya sa mu cika da imani.
Kafin 9:00pm tuni mutuwar ta zaga kowanne sa'ko na ahalin kama daga na cikin gida da wa'danda ke nesa da gidan, mutuwar da ta ratsa zukatan mutane da dama yayin da ta zama sulhu ga wasu, ta kuma zama abun farin ciki a zukatan wasu sai dai su ma kada su manta ba tabbata za su yi a doron duniyar ba.
Sosai ABATCHA ESTATE ya zama tamkar ma'kabarta, kowanne sashe shiru yake kowa na 'kara jimamin mutuwar yana hawaye irin na yankan 'kauna, ba iya ahalin gidan ba hatta ma'aikatan gidan sun matu'kar razana da mutuwar Yaya Sadauki, sun yi kuka tamkar wa'danda suka rasa wane sashe na jikinsu, kai dole ma su yi kukan don kuwa ba lallai Marigayi ya mu'amalance ka ba ka ji 'kaunarsa cikin ranka ba, yana da salon mutuntawa da iya mu'amala. Saboda yanayin Alhaji Baba yasa Daddy ya zauna a tare da shi, Yaya Khalil da kuma Hajiya Babba suka wuce asibitin don zama kusa da marasa lafiyan, sai a lokacin ne Humairah ta koma, a nan kuma Hajiya Babba ta san da cewa Mabrukan ma ashe tana nan.
Duk wanda ya farfa'do cikinsu da zarar ya tuna da event 'din da ya faru sai ya koma, haka dai wannan dare ya kasance ga wa'dannan mutane uku, sai dai kuma wa'danda ke jinyar sosai zukatansu suka fi raunana, gwanda Hajiya Babba ta zubarda hawaye, Yaya Khalil kam ba a magana illa iyaka dai idanuwansa sun sauya daga wa'dannan fararen zuwa jajaye kamar gauta ga kuma yadda suke masa zafi kamar ana hura wuta a ciki, zafin da suke masa kuma in za a kwatanta shi da wadda zuciyarsa ke yi ba a magana, jijiyoyin kansa sun fito ru'du-ru'du. A hakan idan Hajiya ta gama kukanta sai kuma ta hau masa nasiha. Addu'a kuwa daren ranar ya sha ta daga masoyansa.
Wannan dare dai ya yawaita tsayi tamkar an dakatar da tafiyar lokaci haka suke gani ko dan saboda kashi 98% nasu ba su rintsa bane, sahur na azumin washegari ya gagara har alfijr ya keto. Bayan sallar asuba kai tsaye iyaye mazan banda Daddy da ke tare da Alhaji Baba suka fice daga gidan don nemo gawarsa shima a masa sutura a mi'ka shi gidansa na gaskiya. Allah ya masa rahama.
Washegari da safe su Aunty Madina suka diro, su Yaya Haidar da Yaya Junaid tare da ahalinsu su ma suna hanyarsu ta zuwa tunda sa'kon ya kai gare su, sai dai ba su wani 'daga hankali akai ba saboda ba su yadda da zancen mutuwar tasa ba.