Sashe 22
A Babban Gida Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“You look so beautiful Lilyn Yaya.”
“And you look more handsome than...” Bata ƙarasa ba ganin an wangale musu gate ɗin school ɗin. Ba su wani daɗe ba ya kammala duk wasu matakai na ganin ta zama cikakkiyar ɗaliba, a lokacin kuma ta amshi uniform da littattafai, daga nan aka wuce da ita Form 3...same class da su Zakiyya. Ihun murna suka saki ganin Zahrah suna kuma mamakin ba zatar da tayi musu. Nan suka yi introducing Bata ma sauran ƴan ajin, daga nan fa Zahrah ta ɗame kamar ba baƙuwar ba, har ta yi abokin wai shi Nu'aym, shi ne kuma class rep ɗin su.
Ko da lokacin tashi ya yi ta fito za su tafi da su Nasreen ta hango sayyarar Yayan ta, da sauri ta juya za ta wuce.
Nainarh ta dakatar da ita
“Where do you think you're going, an Zo ɗaukarmu fa.” pointing motar Yaya Sadaukin tayi sa hannu, nan Nainarh ta zaro ido waje tana mamaki, In ba ƙarya tayi ba wannan motar da Yaya Sadauki yau ya fita da ita ne. Bata aune ba ta ga Zahrah har ta kai ga wurin motar, babu yadda ta iya ta nufi motar Baban Salaha. Ko da su Nasreen suka tambaye ta ina Zahrah sai tace musu ai ta tafi. Basu matsa mata da tambaya ba ganin yanayin fuskarta da haka suka wuce gida.
Can wajen Zahrah tana shiga ya ja motar.
“Yaya shi ne ka baro aikinka ka zo, ai da zan koma da su Nainarh.” shiru ya mata bai ce komai ba can kuma yace
“Na san da motar can ɗin ai nazo, kullum kuma Ni zan kai ki na maida ki, don't say anything again....” shiru babu wanda yayi magana har suka isa. Yana daidaita parking ta fito, wannan karon kuma a idon Mami wacce motarta ke shirin barin estate ɗin.
Ko da Yaya Sadauki ya shigo Zahrah ta zo ta tambaye shi ko za ta masa girki? Yace mata a'a zai ci wancan ɗin shima and ta shirya in zai fita zai kawo mata uniform na Tahfiz wacce take cikin estate ɗin.
A islamiyyar suka haɗu, nan suka tusa ta gaba da tambayar waye ya mayar da ita gida, shiru tayi musu, da ta gaji kuma tace musu ai motar su Nu'aym ne, ba tare da sun yarda ba suka ƙyale ta amma suka ce mata kada ta ƙara bin wata motar in ba haka ba sai sun faɗawa Alhaji Babba.
Bayan sun keɓe da Nainarh ne ta kawo zancen ta kuma yi mata jan ido kan ta san waye ne a motar.
“Ya Allah, Sis Nainarh Yaya Sadauki ne fa ba kowa ba, kinga Dama shi ya kawo Ni, ya riga ya gan Ni, In na wuce na bi ku ba zai ji daɗi ba.”
“Then meyasa kika ɓoye min da farko? Ko kina tunanin ba zan so na ganki da shi ba? Ke ma ƴar'uwarsa ce ai.”
“Ba haka ba ne Nainarh...”
“Don't say anything Zahrah, kawai dai na baki amanar Yaya na, don na ga ke ta musamman ce gare shi, ki kasance da Yaya kina ɗebe masa kewa ko damuwoyinsa za su gusa. Nan ta bata labari kamar yadda Nasreen ta bata. Ita dai Zahrah mamaki take, ko me suka ɗauke ta da ta kasance da shi?
Bayan an tashi daga islamiyyar a gajiye ta koma, amma duk da haka she prepare dinner for him. Lokacin da ta shiga wurin Alhaji Baba ne taji ana zancen aure, amma bata fahimci na waye ba. Ko da ta dawo sai ta ji ta rasa sukuni amma haka ta daure, a yau kam ba su yi wata hira ba da Yayan ta, tana gama serving nasa ta wuce ba tare da ita ta yi dinner ɗin ba.
*Washegari*
Kamar yadda ya faɗa ɗin shi ne ya kai ta school da kansa, haka kuma ya ɗauko ta. A hanyarsu ta dawowa ya kawo mata zancen aurensa. Dim ƙirjin ta ya buga, amma sai ta masa Allah sanya alkairi duk da bata ji daɗin zancen ba, amma ta ta'allaƙa hakan ne da sanin ba son auren yake yi ba saboda ta san mata ba sa gabanta.
A sukwane ta ƙarasa yinin ranar, ko a islamiyya sisters ɗin ta babu tambayar da basu mata ba amma tace babu abinda ke damunta kawai gajiya ce. Bata fasa masa hidima ba tayi masa dinner. Bayan ta yi sallah ta ɗan kwanta kan sallayar ta da niyyar ba zata ma fita waje ba coz ji take kamar ta rausa kuka haka take ji idan ta tuna da maganar. (Yarinya don't know that she's in love....).
Tsawon sati guda tana bin motar gida gudun kada su haɗu, In an tashi ma da wuri take kaɗe ma su Zakiyya hankali su wuce, cikin satin nan ba ƙaramar rama ta yi ba, and bata Zama a parlour ma gudun kada su haɗu da kowa, she's always fund of isolating herself saboda ta fi jin daɗin hakan, duk yadda ƴan uwanta suka matsa mata da tambaya ko uffan ba ta cewa sai ma ta basu waje.
Ɓangaren Yaya Sadauki kwana biyu in ya zo sai Hajjaty tace masa Zahrah ta bi su Nasreen saboda kada ta makara, a rana ta uku ya bar mata sallahun lallai lallai ta jira shi da safe gobe coz zaman part ɗin Hajjaty ma daina shi tayi ta koma Part ɗin Hajiya Babba.
Babu wadda ya fahimci dalilin Zahrah na sauyawarta daga yadda take zuwa Silent Zahrah. Allah sarki Yaya Sadauki ya fi kowa damuwa da rashin ganinta, ta riga ta sabarwa zuciyarsa da rayuwa da shi and yanzu take gudunsa, ya Yi tunanin har ya gaji kan me ya mata amma ya kasa fahimtar komai. Lokacin ya fara fahimtar cewa ita ɗin ƙarfin guiwarsa ce, dole ta dawo gare shi don cikar burinsa da ya ɗauri aniyar cimma su.
Alhamdulillah ya fara aiki kan neman Mama, an kama kawu wanda ke hauka tuburan daga ƙarshe dai aka sake shi ganin ba information ɗin da za a samu wurinsa. Baba Amarya da ɗiyarta Bibalo Are no where to be found. Yadda yadda so abun ya zo masa sai yake ƙoƙarin ba shi wahala and supporter ɗinsa ta guje shi, ba shi da wata maslaha da ta wuce ya dawo da ita gare shi.
Yau juma'a kuwa ya ƙuduri aniyar sanya ta a idonsa ya kuma tanadi tambayoyin sa da zai mata, dole ta amsa masa su kuma in ba haka ba.....
*Allah sarki little Zahrah Kuma Lilyn yayanta an zurma tun kafin a je ko ina, anya kuwa za ta samu cikar burin ta a yadda ta sanya damuwa cikin ranta? Kai jama'a....team Zahrah kuna ina? Yau reactions ɗin ku kamata yayi ya zo da emojin 😥 nan. Ni dai ina taya Yaya Sadauki murnar samun mace wayayya kamar Barrister Mabruka. Ko ba komai za mu yi anko, ke kuma Zahrah ki kashe kanki tunda baki da hankali....Ina team Rumana? Ku ma an doka ku, haka team Kausar ku ma ana shiri.*
*Ko wanne shiri su Mami ke yi, sun ma san me ake ciki kuwa?*
*Allah Sarki Rayuwa, Allah ya kawo ma kowa sauƙi.*
*Kada a mance for any inquiries ga number ta +2347061707238, ƙofar gyara a buɗe take.*
*Please react and share fisabilillah.*
# LilynYaya
# YayanLily
# Kausar
# Rumana
[12/29, 9:56 PM] Diamond Bhatool:
https://whatsapp.com/channel/0029VanUFkw5kg7G2ci16o2X
*🏡A BABBAN GIDA🏡*
*TAKUN ƘARSHE*
*©Diamond Bhatool*
*💎💍ELITE DIAMOND WRITERS💍💎*
_Where diamonds shine, words ignite_
_Wattpad: @diamond_bhatool_
_Arewabooks: @diamondbhatool3_
Please follow
*PAGE* 1️⃣7️⃣
﷽
*ZAHRAH*
Baiwar Allah daren juma'a dai bacci gagararta yayi, ta rasa ina zata jefa kanta, ga shi yanzu magana ma wahala take bata bare a zo gandun hira, Nasreen ma ta yi ta gaji, har kuka sai da ta yi wa Zahrah amma ƙyam ta ƙeƙashe idanun ta. A haka har bacci ya ɗauke Nasreen ɗin.
Haka ta yi ta jera sallolints har dare ya tsala, cikin daren ta fara jin ihu sama-sama, a hankali kuma ihun ke ƙaruwa har ya kai ga ya fara damun kunnuwanta. A hankali ta miƙe tare da switching bulb Amma ba abun da ta gani, siɗaf-siɗaf ta buɗe ƙofa ta fice parlourn tana waige-waige kamar tsohuwar munafuka.
Still dai babu kowa a parlourn amma ihun nan didn't disappear. Cike da tsoro ta nufi entrance door ɗin ta buɗe ta a hankali bakinta ɗauke da addu'ar neman kariya a wurin ubangiji. Hararbar gidan ma dai babu kowa, sannan har wa lokacin nan tana jin ihun kamar a cikin kunnenta.
Ba ta gushe ba tana mai ambaton sunan Ubangiji a haka ta fara takawa tana kewaya ko'ina but nothing to be found. Da ta gaji da zagayawar kuma kunnenta ya ƙi ya daina jiyo ihun kawai ta yanke shawarar fita waje ta duba.
Duk irin tsoron da take ji haka ta kawar da shi ta murɗa lock ɗin jikin ƙofar a hankali, Allahn da ya so ta kuma ƙofar ba ta yi ƙara ba, ajiyar zuciya ta sauke tana mai ƙara ninka addu'o'in tsari bisa harshen ta. A haka ta fice ba tare da takalmi ba tana tafe tana waiwaye.
Kamar wacce aka ce wa tsaya sai ta tsaya cak da tafiyar tana mai lashe kunne don gano direction ɗin da sautin ke fitowa wanda a yanzu ya sauya amo i zuwa wani irin abu maras daɗin ji ko sauraro.
Wurin da take tsammanin daga nan sautin ke fitowa ta nufa har lokacin zuciyarta ba ta daina lugude ba amma ambaton sunam Ubangiji da take yi yasa take jin ƙarfin tunkarar wurin wanda fili ne tarwal sai kuma bishiyoyi da ciyayi masu tsayi da suka gama cike wurin.
Dakatawa ta yi tana zaro ido saboda hango wasu mutane da tayi daga nesa, mamaki sai da ya so kashe ta, ko su waye ne? Ta faɗa cikin zuciyarta. Cike da ƙarfin hali ta fara takawa cikin sanɗa har ta kusa isa ga mutanen sai kuma ta kwanta cikin ciyayin da suka fara bushewa ai kuwa wani sauti ya ɗan bayyana. Nan ta rufe bakinta da tafin hannunta tana roƙon Allah yasa ba su ji ta ba, sai dai kash sun riga sun ji.
“And you look more handsome than...” Bata ƙarasa ba ganin an wangale musu gate ɗin school ɗin. Ba su wani daɗe ba ya kammala duk wasu matakai na ganin ta zama cikakkiyar ɗaliba, a lokacin kuma ta amshi uniform da littattafai, daga nan aka wuce da ita Form 3...same class da su Zakiyya. Ihun murna suka saki ganin Zahrah suna kuma mamakin ba zatar da tayi musu. Nan suka yi introducing Bata ma sauran ƴan ajin, daga nan fa Zahrah ta ɗame kamar ba baƙuwar ba, har ta yi abokin wai shi Nu'aym, shi ne kuma class rep ɗin su.
Ko da lokacin tashi ya yi ta fito za su tafi da su Nasreen ta hango sayyarar Yayan ta, da sauri ta juya za ta wuce.
Nainarh ta dakatar da ita
“Where do you think you're going, an Zo ɗaukarmu fa.” pointing motar Yaya Sadaukin tayi sa hannu, nan Nainarh ta zaro ido waje tana mamaki, In ba ƙarya tayi ba wannan motar da Yaya Sadauki yau ya fita da ita ne. Bata aune ba ta ga Zahrah har ta kai ga wurin motar, babu yadda ta iya ta nufi motar Baban Salaha. Ko da su Nasreen suka tambaye ta ina Zahrah sai tace musu ai ta tafi. Basu matsa mata da tambaya ba ganin yanayin fuskarta da haka suka wuce gida.
Can wajen Zahrah tana shiga ya ja motar.
“Yaya shi ne ka baro aikinka ka zo, ai da zan koma da su Nainarh.” shiru ya mata bai ce komai ba can kuma yace
“Na san da motar can ɗin ai nazo, kullum kuma Ni zan kai ki na maida ki, don't say anything again....” shiru babu wanda yayi magana har suka isa. Yana daidaita parking ta fito, wannan karon kuma a idon Mami wacce motarta ke shirin barin estate ɗin.
Ko da Yaya Sadauki ya shigo Zahrah ta zo ta tambaye shi ko za ta masa girki? Yace mata a'a zai ci wancan ɗin shima and ta shirya in zai fita zai kawo mata uniform na Tahfiz wacce take cikin estate ɗin.
A islamiyyar suka haɗu, nan suka tusa ta gaba da tambayar waye ya mayar da ita gida, shiru tayi musu, da ta gaji kuma tace musu ai motar su Nu'aym ne, ba tare da sun yarda ba suka ƙyale ta amma suka ce mata kada ta ƙara bin wata motar in ba haka ba sai sun faɗawa Alhaji Babba.
Bayan sun keɓe da Nainarh ne ta kawo zancen ta kuma yi mata jan ido kan ta san waye ne a motar.
“Ya Allah, Sis Nainarh Yaya Sadauki ne fa ba kowa ba, kinga Dama shi ya kawo Ni, ya riga ya gan Ni, In na wuce na bi ku ba zai ji daɗi ba.”
“Then meyasa kika ɓoye min da farko? Ko kina tunanin ba zan so na ganki da shi ba? Ke ma ƴar'uwarsa ce ai.”
“Ba haka ba ne Nainarh...”
“Don't say anything Zahrah, kawai dai na baki amanar Yaya na, don na ga ke ta musamman ce gare shi, ki kasance da Yaya kina ɗebe masa kewa ko damuwoyinsa za su gusa. Nan ta bata labari kamar yadda Nasreen ta bata. Ita dai Zahrah mamaki take, ko me suka ɗauke ta da ta kasance da shi?
Bayan an tashi daga islamiyyar a gajiye ta koma, amma duk da haka she prepare dinner for him. Lokacin da ta shiga wurin Alhaji Baba ne taji ana zancen aure, amma bata fahimci na waye ba. Ko da ta dawo sai ta ji ta rasa sukuni amma haka ta daure, a yau kam ba su yi wata hira ba da Yayan ta, tana gama serving nasa ta wuce ba tare da ita ta yi dinner ɗin ba.
*Washegari*
Kamar yadda ya faɗa ɗin shi ne ya kai ta school da kansa, haka kuma ya ɗauko ta. A hanyarsu ta dawowa ya kawo mata zancen aurensa. Dim ƙirjin ta ya buga, amma sai ta masa Allah sanya alkairi duk da bata ji daɗin zancen ba, amma ta ta'allaƙa hakan ne da sanin ba son auren yake yi ba saboda ta san mata ba sa gabanta.
A sukwane ta ƙarasa yinin ranar, ko a islamiyya sisters ɗin ta babu tambayar da basu mata ba amma tace babu abinda ke damunta kawai gajiya ce. Bata fasa masa hidima ba tayi masa dinner. Bayan ta yi sallah ta ɗan kwanta kan sallayar ta da niyyar ba zata ma fita waje ba coz ji take kamar ta rausa kuka haka take ji idan ta tuna da maganar. (Yarinya don't know that she's in love....).
Tsawon sati guda tana bin motar gida gudun kada su haɗu, In an tashi ma da wuri take kaɗe ma su Zakiyya hankali su wuce, cikin satin nan ba ƙaramar rama ta yi ba, and bata Zama a parlour ma gudun kada su haɗu da kowa, she's always fund of isolating herself saboda ta fi jin daɗin hakan, duk yadda ƴan uwanta suka matsa mata da tambaya ko uffan ba ta cewa sai ma ta basu waje.
Ɓangaren Yaya Sadauki kwana biyu in ya zo sai Hajjaty tace masa Zahrah ta bi su Nasreen saboda kada ta makara, a rana ta uku ya bar mata sallahun lallai lallai ta jira shi da safe gobe coz zaman part ɗin Hajjaty ma daina shi tayi ta koma Part ɗin Hajiya Babba.
Babu wadda ya fahimci dalilin Zahrah na sauyawarta daga yadda take zuwa Silent Zahrah. Allah sarki Yaya Sadauki ya fi kowa damuwa da rashin ganinta, ta riga ta sabarwa zuciyarsa da rayuwa da shi and yanzu take gudunsa, ya Yi tunanin har ya gaji kan me ya mata amma ya kasa fahimtar komai. Lokacin ya fara fahimtar cewa ita ɗin ƙarfin guiwarsa ce, dole ta dawo gare shi don cikar burinsa da ya ɗauri aniyar cimma su.
Alhamdulillah ya fara aiki kan neman Mama, an kama kawu wanda ke hauka tuburan daga ƙarshe dai aka sake shi ganin ba information ɗin da za a samu wurinsa. Baba Amarya da ɗiyarta Bibalo Are no where to be found. Yadda yadda so abun ya zo masa sai yake ƙoƙarin ba shi wahala and supporter ɗinsa ta guje shi, ba shi da wata maslaha da ta wuce ya dawo da ita gare shi.
Yau juma'a kuwa ya ƙuduri aniyar sanya ta a idonsa ya kuma tanadi tambayoyin sa da zai mata, dole ta amsa masa su kuma in ba haka ba.....
*Allah sarki little Zahrah Kuma Lilyn yayanta an zurma tun kafin a je ko ina, anya kuwa za ta samu cikar burin ta a yadda ta sanya damuwa cikin ranta? Kai jama'a....team Zahrah kuna ina? Yau reactions ɗin ku kamata yayi ya zo da emojin 😥 nan. Ni dai ina taya Yaya Sadauki murnar samun mace wayayya kamar Barrister Mabruka. Ko ba komai za mu yi anko, ke kuma Zahrah ki kashe kanki tunda baki da hankali....Ina team Rumana? Ku ma an doka ku, haka team Kausar ku ma ana shiri.*
*Ko wanne shiri su Mami ke yi, sun ma san me ake ciki kuwa?*
*Allah Sarki Rayuwa, Allah ya kawo ma kowa sauƙi.*
*Kada a mance for any inquiries ga number ta +2347061707238, ƙofar gyara a buɗe take.*
*Please react and share fisabilillah.*
# LilynYaya
# YayanLily
# Kausar
# Rumana
[12/29, 9:56 PM] Diamond Bhatool:
https://whatsapp.com/channel/0029VanUFkw5kg7G2ci16o2X
*🏡A BABBAN GIDA🏡*
*TAKUN ƘARSHE*
*©Diamond Bhatool*
*💎💍ELITE DIAMOND WRITERS💍💎*
_Where diamonds shine, words ignite_
_Wattpad: @diamond_bhatool_
_Arewabooks: @diamondbhatool3_
Please follow
*PAGE* 1️⃣7️⃣
﷽
*ZAHRAH*
Baiwar Allah daren juma'a dai bacci gagararta yayi, ta rasa ina zata jefa kanta, ga shi yanzu magana ma wahala take bata bare a zo gandun hira, Nasreen ma ta yi ta gaji, har kuka sai da ta yi wa Zahrah amma ƙyam ta ƙeƙashe idanun ta. A haka har bacci ya ɗauke Nasreen ɗin.
Haka ta yi ta jera sallolints har dare ya tsala, cikin daren ta fara jin ihu sama-sama, a hankali kuma ihun ke ƙaruwa har ya kai ga ya fara damun kunnuwanta. A hankali ta miƙe tare da switching bulb Amma ba abun da ta gani, siɗaf-siɗaf ta buɗe ƙofa ta fice parlourn tana waige-waige kamar tsohuwar munafuka.
Still dai babu kowa a parlourn amma ihun nan didn't disappear. Cike da tsoro ta nufi entrance door ɗin ta buɗe ta a hankali bakinta ɗauke da addu'ar neman kariya a wurin ubangiji. Hararbar gidan ma dai babu kowa, sannan har wa lokacin nan tana jin ihun kamar a cikin kunnenta.
Ba ta gushe ba tana mai ambaton sunan Ubangiji a haka ta fara takawa tana kewaya ko'ina but nothing to be found. Da ta gaji da zagayawar kuma kunnenta ya ƙi ya daina jiyo ihun kawai ta yanke shawarar fita waje ta duba.
Duk irin tsoron da take ji haka ta kawar da shi ta murɗa lock ɗin jikin ƙofar a hankali, Allahn da ya so ta kuma ƙofar ba ta yi ƙara ba, ajiyar zuciya ta sauke tana mai ƙara ninka addu'o'in tsari bisa harshen ta. A haka ta fice ba tare da takalmi ba tana tafe tana waiwaye.
Kamar wacce aka ce wa tsaya sai ta tsaya cak da tafiyar tana mai lashe kunne don gano direction ɗin da sautin ke fitowa wanda a yanzu ya sauya amo i zuwa wani irin abu maras daɗin ji ko sauraro.
Wurin da take tsammanin daga nan sautin ke fitowa ta nufa har lokacin zuciyarta ba ta daina lugude ba amma ambaton sunam Ubangiji da take yi yasa take jin ƙarfin tunkarar wurin wanda fili ne tarwal sai kuma bishiyoyi da ciyayi masu tsayi da suka gama cike wurin.
Dakatawa ta yi tana zaro ido saboda hango wasu mutane da tayi daga nesa, mamaki sai da ya so kashe ta, ko su waye ne? Ta faɗa cikin zuciyarta. Cike da ƙarfin hali ta fara takawa cikin sanɗa har ta kusa isa ga mutanen sai kuma ta kwanta cikin ciyayin da suka fara bushewa ai kuwa wani sauti ya ɗan bayyana. Nan ta rufe bakinta da tafin hannunta tana roƙon Allah yasa ba su ji ta ba, sai dai kash sun riga sun ji.