Sashe 15
A Babban Gida Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
_Not edited_
﷽
Shi fa har ga Allah bai ma San da zamanta ba sai da ta ɗan bige ƙafarsa garin zuba gurasar a plate tukun ya San da mutum kusa da shi, a hankali ya mayar da dubansa ga wurin da ƙafarsa take, mamaki fal cikin ransa ganin mutum, mutum ɗin ma yarinyar da ta gama raina sa, a fuska ɗaure ya kalleta sai dai ita ba ta san da hakan ba sakamakon yadda ta maida hankalin ta ga zoɓon da take zuba masa.
Tashin hankali Wai ba a sa masa date! Zahrah ba mugun ƙoƙari ta yi ba, bayan ta kammala sai ta ja gefe tare da tsugunnawa gabansa sai Kuma ta kama kunnuwanta biyu.
“I'm sorry Yaya, ka yafe min, I don't meant to hurt you, please ka Yi haƙuri ba zan maimaita ba.”
Ko ɗagowa yayi ya kalle ta bata samu ba talkless of ta sa ran zai amsa, hakan ya sa guiwarta yin sanyi.
“Yaya ga gurasar I prepare it to you myself, don Allah ka ci kada ka kwana da yunwa, I won't forgive myself if you didn't eat, don Allah Yaya.....”
Hannu ya ɗaga mata alamar ya isa sannan ya nuna mata ƙofa da hannunsa.
“Out of my sight!”
Ai da sauri har tana harɗewa ta bar parlourn sai bedroom ɗinta. Duk Wannan ban haƙuri da take bashi yana jinta, and temper da ya hau ya sauƙo musamman yadda ta iya lanƙwasa harshe ta bashi haƙuri. Shi a da yana da wani stereotype game da mata that Suna da girman Kai but karo na farko kenan da yayi proving kan shi wrong.
Abun da ya fu burge shi da yarinyar bai Wuce yadda yadda nuna concern ɗinta kansa ba, he really appreciated it Amma cikin ransa fa, ganin tunanin babu yadda zai Kai shi yasa ya ja tsaki tare da furta Bismillah sannan ya fara cin gurasar yana lumshe idanuwa, cikin ransa ya furta “This sister is unique”
Bai Kai ga kammala ci ba yaji muryar su Hajjaty, idanuwa ya zaro sai Kuma ya gyara Zama ya ci gaba da cin gurasar sa hankali kwance. Ko da suka dawo babu Wanda yayi wa ɗan'uwansa magana sai Yaya Khalil da ɗan banza tsokalarsa ya ce
“Man wa ya kawo maka gurasa kuma?”
Ya ƙarasa yana ƙura Masa ido, gogan naka bai ce komai ba ya ci gaba da Kora zoɓo abun sa. Sauran jama'a babu wadda yace uffan game da hakan.
Alhaji Baba ne ya miƙe don ya Wuce ɗakinsa ya kwanta, Sallama ya Musu sannan ya nufi bedroom ɗinsa, Nan Yaya Sadauki ya bi bayansa ya rage iya Hajjaty ce Sai Yaya Khalil.
Hajjaty ta kalli Yaya Khalil ɗin tace
“Ni Halilu wa ya kawowa Sadauki abinci Nan?”
“Ina ga Zahrah ce fa”
“Zahrah kuma?”
“E Hajjaty, ni fa akwai abun da nake hasasowa and Ina fatan ya tabbata, you people will be Happy with it.”
“To Allah ya tabbatar da alkhairi.”
“Amin” ya and.
A ɓangaren Yaya Sadauki da Kansa ya kaɗewa Alhaji Baba shimfiɗa kana ya taimaka Masa ya zauna bakin gadon Shi kuma ya Nemi waje ya zauna kan carpet din dake shimfiɗe a bedroom ɗin.
Ganin hakan yasa Alhahi Baba fahimtar cewa da abun da yake so.
“Ya dai Sadaukin Abatcha? Akwai damuwa ne?”
“A'ah Alhaji Baba, it's all about that case.” ya faɗa cikin ƙunar rai.
“I believe in you Sadauki, bayan tafiyar ka na Yi bincike and it's found that akwai wadda ya haɗa wannan Abu, a matsayinka na jami'in tsaro da bincike ina roƙon ka da ka faɗaɗa binciken don na ƙosa da ire-iren abubuwan nan.”
Tun da Alhaji Baba ya fara bayani zuciyar Yaya Sadauki tayi sanyi ƙalau, tsoro da fargaban da yake ji all disappeared. Cikin ransa yana faɗin “It's now the game will be started.”
Murmushi ya yi yana faɗin
“Alhamdulillah, na ji daɗin bayyanar gaskiya, Allah ya tsare gaba.”
“Sai dai Sadauki akwai wani hukunci da na yanke game da hakan, Dole za ka auri Mabruka in ba Haka ba ba zamu taɓa gano miyagun cikin familyn nan ba.”
“What? Alhaji Baba aure fa ka ce?”
“Eh Sadauki, aure dai na ce, auren Mabruka dai ƴar'uwarka, ko da Haka ba ta faru tsananin ku ba a tunani na in nace ka aure ta zaka yi babu jayayya but now da aka kawo wannan batun ko cikin family none of your brothers will marry her get my point Sadauki. Yanzu ba mu da wani evidence da za mu wanke ta da Kai kanka idon mutane, but I'm hoping that we'll get one soon.” ya ƙarasa a raunane.
His heart is beating faster to extent that yana ji kamar zata fasa chest ɗinsa ne ta for. He's speechless and soft, ko da was baya jin cewa zai iya ƙetare umarnin Alhaji Baba ba coz he's his everything, he's more than a Granny but someone qualified to be called a Father.
Abu na gaba kuma shi ne matsawar ya amince da wannan haɗin zai cutar da rayuwarsa da Kuma ta baiwar Allahr da Bata ji ba Bata gani ba, sannan shi a tsarin rayuwarsa ma babu saki bare ya ce in gaskiya ta bayyana zai sallame ta, hakan zai Zama babban cin fuska ga Hajiya Babba wacce ta ɗauke sa tamkar ɗanta Khalil.
Nooo ba zai ƙi amincewa da umarnin Alhaji Baba ba ko Dan samarwa Mabruka ƴancin ta Amma ya ɗau alwashi in ya binciko ko uban waye ke da sa hannu sai ya ɗanɗani kwatankwacin ɗacin da ya ji.
“Ka Yi shiru Sadauki, ya ka gani?”
Da ƙyar ya furta “Babu komai Allah yasa hakan shi ne mafi alkairi”
Murmushinsa irin na manyan mutane yayi sannan ya ce
“Allah yayi maka albarka Sadauki, Allah ya baka iyalan da za su Yi maka biyayya kamar yadda kake Yi Mana.”
Can ƙasan maƙoshi ya amsa da
“Amin”
Shiru ɗakin kamar babu kowa tsawon wasu daƙiƙu, cike da ƙarfin Hali tare da son ɓoye damuwarsa ya ce
“Alhaji about that girl ...ehm your granddaughter.” daga haka yayi shiru. Alhaji Baba yayi murmushi sannan yayi gyaran murya.
“Tun dawowar ta nake famar nemanka ba na samunka and it's about her issue....dama Ina son ka taimaka min ne after telling you how it happened.”
Nan ya bashi full labarin Madina tun tana a tare da su zuwa ɓacewarta.
Ransa ɓace ya ce
“Why Alhaji? Why ba za a ɗau mataki kan wannan mugun mutumin da ya cutar da Momy Madina ba? Wallahi sai ya San ya taɓo jinin Abatcha. Wallahi ba Dan ƙyale shi ba Kuma sai ya fito da ita ko ma Ina ya Kai ta!.”
“Halinku ɗaya da Mahaifinka, zafin nama da ɗaukar zafi, wannan ba maslaha bace, mu fara Nemo ta kafin mu koma Kansa.”
Wata zazzafar iska ya fesar.
“Ka je kun gaisa da mutanen gidan ne?”
Kamar ya tsala ihu ya ce
“Sai da safe tukun”
Nan fa Alhaji Baba ya fara mass faɗa Wai meyasa ba zai shiga ya gaida Mahaifiyarsa ba ko da ba zai duba kowa ba?
“Bana son irin Haka Sadauki, ba irin rainon da Rukayya tayi maka ba, yanzu ba sai gobe ba ka tabbatar ka shiga wurin Sughrah ka Kuma Bata haƙuri ka ji ko?”
Kai ya gyaɗa kamar zai Yi kuka ya ce
“To”
“Mu kwana Lafiya ni zan kwanta.”
“Allah ya Bamu alkairi”
Daga Haka ya fice zuciyarsa na ƙuna. Ba tare da ya je ɓangaren Mommah ba ya Wuce bedroom ɗinsa da ke part ɗin Hajiya Babba, ba Wai ya ƙi bin umarnin Alhaji Baba ba ne, sai dai baya son a Yi ba daidai ba musamman da yake sama, ya Kuma riga ya San halin birkitacciyar Mahaifiyarsa shiyasa kawai ya zaɓi ya huta Idan ya so da safe ya shiga.
Yana shiga yayi wanka sannan ya ɗauro alwala don yin shafa'i da witri kamar yadda yadda Saba coz yana jin yau ba lallai ya iya tashi don ya riga ya faka damuwar jama'a a gefe, in ya tashi daga baccin ya saɓa ko ya ɗuura ta a baya.
*Zahrah's POV*
Da sauri ta bar parlourn sai Kuma bedroom ɗinta. Kan bed ta faɗa tana maida numfashi
“Ya Allah! Allah dai yasa ya ci abincin kada ya kwana da yunwa.” she said so openly sai Kuma ta yamutsa fuska
“To Ina ruwa na da shi in ya ci in bai ci ba?”
“Kin manta kin ce Zaki taimaka wurin dawo da rayuwarsa daidai, it's part of your job.”
“Yea Haka ne! Amma meyasa nake jin sa mutum na musamman a rayuwata?”
“Saboda shi ɗin ɗan'uwanki ne.”
Kamar mahaukaciya Haka take ta surutu ita ɗaya. Kamar an ce ta nutsu sai ta tura bankinta gaba tare da cakumo blanket ɗin dake shimfiɗe kan bed ɗin saying
“Ke Zahrah relax! Relax! Relax please.”
Lokaci ɗaya ta kwashe da dariya
“Wallahi yau na Zama mahaukaciyar gaske, please lemme control myself!”
Sai Kuma ta Fara juyi kan bed ɗin. Tunawa da Bata Yi salla ba yasa ta diro da sauri ta nufi toilet, sai da tayi wanka tukun ta ɗauro alwala, bayan ta yi salla ta haye bed don ta fara tsara ta Ina zata Fara.
Ganin kamar an toshe brain ɗinta yasa ta yanke shawarar gobe sa zanta da Nasreen kawai. A Haka dai har bacci ya ɗauke ta.
*Devil Klans’ POV, 1:13 Midnight, in an unknown dark area full of long canopies and trees.*
Guguwa ce Mai ƙarfin gaske ta tashi kamar duniyar zata kife lokaci ɗaya Kuma ta ɗauke yayin da wani irin duhu ya mamaye farfajiyar wajen tsawon wani lokaci Kuma sai ga Haske yana bayyana kaɗan kaɗan har ya gama mamaye wurin.
Halittun Nan na kwanakin baya da za su Kai goma Sha biyar suka bayyana shugabansu kuma na zaune ƙafarsa ɗaya kan ɗaya. A yau dai Kam na gama tabbatarwa da Kai na waɗannam matsafa ne ko Kuma cultists waɗanda ke amfani da jinin mutane da wasu dabbobin Suna shayar da baƙaƙen shaiɗanu don Samar ma kanunsu da wani ƙarfin iko na sihiri, ɗaukaka ko Kuma dukiya.
A yau ma kamar ibada sai da suka gabatar da karatun dalasimansu da suke cewa addu'a kafin su Fara tattaunawa kan abun da ya Tara su.
﷽
Shi fa har ga Allah bai ma San da zamanta ba sai da ta ɗan bige ƙafarsa garin zuba gurasar a plate tukun ya San da mutum kusa da shi, a hankali ya mayar da dubansa ga wurin da ƙafarsa take, mamaki fal cikin ransa ganin mutum, mutum ɗin ma yarinyar da ta gama raina sa, a fuska ɗaure ya kalleta sai dai ita ba ta san da hakan ba sakamakon yadda ta maida hankalin ta ga zoɓon da take zuba masa.
Tashin hankali Wai ba a sa masa date! Zahrah ba mugun ƙoƙari ta yi ba, bayan ta kammala sai ta ja gefe tare da tsugunnawa gabansa sai Kuma ta kama kunnuwanta biyu.
“I'm sorry Yaya, ka yafe min, I don't meant to hurt you, please ka Yi haƙuri ba zan maimaita ba.”
Ko ɗagowa yayi ya kalle ta bata samu ba talkless of ta sa ran zai amsa, hakan ya sa guiwarta yin sanyi.
“Yaya ga gurasar I prepare it to you myself, don Allah ka ci kada ka kwana da yunwa, I won't forgive myself if you didn't eat, don Allah Yaya.....”
Hannu ya ɗaga mata alamar ya isa sannan ya nuna mata ƙofa da hannunsa.
“Out of my sight!”
Ai da sauri har tana harɗewa ta bar parlourn sai bedroom ɗinta. Duk Wannan ban haƙuri da take bashi yana jinta, and temper da ya hau ya sauƙo musamman yadda ta iya lanƙwasa harshe ta bashi haƙuri. Shi a da yana da wani stereotype game da mata that Suna da girman Kai but karo na farko kenan da yayi proving kan shi wrong.
Abun da ya fu burge shi da yarinyar bai Wuce yadda yadda nuna concern ɗinta kansa ba, he really appreciated it Amma cikin ransa fa, ganin tunanin babu yadda zai Kai shi yasa ya ja tsaki tare da furta Bismillah sannan ya fara cin gurasar yana lumshe idanuwa, cikin ransa ya furta “This sister is unique”
Bai Kai ga kammala ci ba yaji muryar su Hajjaty, idanuwa ya zaro sai Kuma ya gyara Zama ya ci gaba da cin gurasar sa hankali kwance. Ko da suka dawo babu Wanda yayi wa ɗan'uwansa magana sai Yaya Khalil da ɗan banza tsokalarsa ya ce
“Man wa ya kawo maka gurasa kuma?”
Ya ƙarasa yana ƙura Masa ido, gogan naka bai ce komai ba ya ci gaba da Kora zoɓo abun sa. Sauran jama'a babu wadda yace uffan game da hakan.
Alhaji Baba ne ya miƙe don ya Wuce ɗakinsa ya kwanta, Sallama ya Musu sannan ya nufi bedroom ɗinsa, Nan Yaya Sadauki ya bi bayansa ya rage iya Hajjaty ce Sai Yaya Khalil.
Hajjaty ta kalli Yaya Khalil ɗin tace
“Ni Halilu wa ya kawowa Sadauki abinci Nan?”
“Ina ga Zahrah ce fa”
“Zahrah kuma?”
“E Hajjaty, ni fa akwai abun da nake hasasowa and Ina fatan ya tabbata, you people will be Happy with it.”
“To Allah ya tabbatar da alkhairi.”
“Amin” ya and.
A ɓangaren Yaya Sadauki da Kansa ya kaɗewa Alhaji Baba shimfiɗa kana ya taimaka Masa ya zauna bakin gadon Shi kuma ya Nemi waje ya zauna kan carpet din dake shimfiɗe a bedroom ɗin.
Ganin hakan yasa Alhahi Baba fahimtar cewa da abun da yake so.
“Ya dai Sadaukin Abatcha? Akwai damuwa ne?”
“A'ah Alhaji Baba, it's all about that case.” ya faɗa cikin ƙunar rai.
“I believe in you Sadauki, bayan tafiyar ka na Yi bincike and it's found that akwai wadda ya haɗa wannan Abu, a matsayinka na jami'in tsaro da bincike ina roƙon ka da ka faɗaɗa binciken don na ƙosa da ire-iren abubuwan nan.”
Tun da Alhaji Baba ya fara bayani zuciyar Yaya Sadauki tayi sanyi ƙalau, tsoro da fargaban da yake ji all disappeared. Cikin ransa yana faɗin “It's now the game will be started.”
Murmushi ya yi yana faɗin
“Alhamdulillah, na ji daɗin bayyanar gaskiya, Allah ya tsare gaba.”
“Sai dai Sadauki akwai wani hukunci da na yanke game da hakan, Dole za ka auri Mabruka in ba Haka ba ba zamu taɓa gano miyagun cikin familyn nan ba.”
“What? Alhaji Baba aure fa ka ce?”
“Eh Sadauki, aure dai na ce, auren Mabruka dai ƴar'uwarka, ko da Haka ba ta faru tsananin ku ba a tunani na in nace ka aure ta zaka yi babu jayayya but now da aka kawo wannan batun ko cikin family none of your brothers will marry her get my point Sadauki. Yanzu ba mu da wani evidence da za mu wanke ta da Kai kanka idon mutane, but I'm hoping that we'll get one soon.” ya ƙarasa a raunane.
His heart is beating faster to extent that yana ji kamar zata fasa chest ɗinsa ne ta for. He's speechless and soft, ko da was baya jin cewa zai iya ƙetare umarnin Alhaji Baba ba coz he's his everything, he's more than a Granny but someone qualified to be called a Father.
Abu na gaba kuma shi ne matsawar ya amince da wannan haɗin zai cutar da rayuwarsa da Kuma ta baiwar Allahr da Bata ji ba Bata gani ba, sannan shi a tsarin rayuwarsa ma babu saki bare ya ce in gaskiya ta bayyana zai sallame ta, hakan zai Zama babban cin fuska ga Hajiya Babba wacce ta ɗauke sa tamkar ɗanta Khalil.
Nooo ba zai ƙi amincewa da umarnin Alhaji Baba ba ko Dan samarwa Mabruka ƴancin ta Amma ya ɗau alwashi in ya binciko ko uban waye ke da sa hannu sai ya ɗanɗani kwatankwacin ɗacin da ya ji.
“Ka Yi shiru Sadauki, ya ka gani?”
Da ƙyar ya furta “Babu komai Allah yasa hakan shi ne mafi alkairi”
Murmushinsa irin na manyan mutane yayi sannan ya ce
“Allah yayi maka albarka Sadauki, Allah ya baka iyalan da za su Yi maka biyayya kamar yadda kake Yi Mana.”
Can ƙasan maƙoshi ya amsa da
“Amin”
Shiru ɗakin kamar babu kowa tsawon wasu daƙiƙu, cike da ƙarfin Hali tare da son ɓoye damuwarsa ya ce
“Alhaji about that girl ...ehm your granddaughter.” daga haka yayi shiru. Alhaji Baba yayi murmushi sannan yayi gyaran murya.
“Tun dawowar ta nake famar nemanka ba na samunka and it's about her issue....dama Ina son ka taimaka min ne after telling you how it happened.”
Nan ya bashi full labarin Madina tun tana a tare da su zuwa ɓacewarta.
Ransa ɓace ya ce
“Why Alhaji? Why ba za a ɗau mataki kan wannan mugun mutumin da ya cutar da Momy Madina ba? Wallahi sai ya San ya taɓo jinin Abatcha. Wallahi ba Dan ƙyale shi ba Kuma sai ya fito da ita ko ma Ina ya Kai ta!.”
“Halinku ɗaya da Mahaifinka, zafin nama da ɗaukar zafi, wannan ba maslaha bace, mu fara Nemo ta kafin mu koma Kansa.”
Wata zazzafar iska ya fesar.
“Ka je kun gaisa da mutanen gidan ne?”
Kamar ya tsala ihu ya ce
“Sai da safe tukun”
Nan fa Alhaji Baba ya fara mass faɗa Wai meyasa ba zai shiga ya gaida Mahaifiyarsa ba ko da ba zai duba kowa ba?
“Bana son irin Haka Sadauki, ba irin rainon da Rukayya tayi maka ba, yanzu ba sai gobe ba ka tabbatar ka shiga wurin Sughrah ka Kuma Bata haƙuri ka ji ko?”
Kai ya gyaɗa kamar zai Yi kuka ya ce
“To”
“Mu kwana Lafiya ni zan kwanta.”
“Allah ya Bamu alkairi”
Daga Haka ya fice zuciyarsa na ƙuna. Ba tare da ya je ɓangaren Mommah ba ya Wuce bedroom ɗinsa da ke part ɗin Hajiya Babba, ba Wai ya ƙi bin umarnin Alhaji Baba ba ne, sai dai baya son a Yi ba daidai ba musamman da yake sama, ya Kuma riga ya San halin birkitacciyar Mahaifiyarsa shiyasa kawai ya zaɓi ya huta Idan ya so da safe ya shiga.
Yana shiga yayi wanka sannan ya ɗauro alwala don yin shafa'i da witri kamar yadda yadda Saba coz yana jin yau ba lallai ya iya tashi don ya riga ya faka damuwar jama'a a gefe, in ya tashi daga baccin ya saɓa ko ya ɗuura ta a baya.
*Zahrah's POV*
Da sauri ta bar parlourn sai Kuma bedroom ɗinta. Kan bed ta faɗa tana maida numfashi
“Ya Allah! Allah dai yasa ya ci abincin kada ya kwana da yunwa.” she said so openly sai Kuma ta yamutsa fuska
“To Ina ruwa na da shi in ya ci in bai ci ba?”
“Kin manta kin ce Zaki taimaka wurin dawo da rayuwarsa daidai, it's part of your job.”
“Yea Haka ne! Amma meyasa nake jin sa mutum na musamman a rayuwata?”
“Saboda shi ɗin ɗan'uwanki ne.”
Kamar mahaukaciya Haka take ta surutu ita ɗaya. Kamar an ce ta nutsu sai ta tura bankinta gaba tare da cakumo blanket ɗin dake shimfiɗe kan bed ɗin saying
“Ke Zahrah relax! Relax! Relax please.”
Lokaci ɗaya ta kwashe da dariya
“Wallahi yau na Zama mahaukaciyar gaske, please lemme control myself!”
Sai Kuma ta Fara juyi kan bed ɗin. Tunawa da Bata Yi salla ba yasa ta diro da sauri ta nufi toilet, sai da tayi wanka tukun ta ɗauro alwala, bayan ta yi salla ta haye bed don ta fara tsara ta Ina zata Fara.
Ganin kamar an toshe brain ɗinta yasa ta yanke shawarar gobe sa zanta da Nasreen kawai. A Haka dai har bacci ya ɗauke ta.
*Devil Klans’ POV, 1:13 Midnight, in an unknown dark area full of long canopies and trees.*
Guguwa ce Mai ƙarfin gaske ta tashi kamar duniyar zata kife lokaci ɗaya Kuma ta ɗauke yayin da wani irin duhu ya mamaye farfajiyar wajen tsawon wani lokaci Kuma sai ga Haske yana bayyana kaɗan kaɗan har ya gama mamaye wurin.
Halittun Nan na kwanakin baya da za su Kai goma Sha biyar suka bayyana shugabansu kuma na zaune ƙafarsa ɗaya kan ɗaya. A yau dai Kam na gama tabbatarwa da Kai na waɗannam matsafa ne ko Kuma cultists waɗanda ke amfani da jinin mutane da wasu dabbobin Suna shayar da baƙaƙen shaiɗanu don Samar ma kanunsu da wani ƙarfin iko na sihiri, ɗaukaka ko Kuma dukiya.
A yau ma kamar ibada sai da suka gabatar da karatun dalasimansu da suke cewa addu'a kafin su Fara tattaunawa kan abun da ya Tara su.