← Book details A Babban Gida Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 29 OF 46

Sashe 29

A Babban Gida Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ƙarfe 6:30am na safe yayi parking motarsa a harabar makeken asibitin saboda saurin da yake yi ya dubo Lilynsa. Masu kula da asibitin suka tsayar da shi har sai da ya mayar da motarsa wurin da aka tanada domin parking. Yana gamawa ya fito da basket ɗin daga booth ya nufi cikin asibitin. Ko da ya isa reception Nan ya sanar da su wurin patient ɗin sa ya zo, da ƙyar suka bar shi ya shiga saboda irin yadda ya musu kwarjini.

Lokacin da ya shiga ya tarar da Zahrah kwance sai dai da alama ba bacci take ba amma idanuwanta a lumshe suke, alamar buɗe ƙofar yasa ta ɗan buɗe idonta don ganin waye. Cikin rashin Sa'a suka haɗa ido da Yaya Sadauki wanda ya sakar mata wani kyakkyawan murmushi da sai da ji zuciyarta ta buga.

Kujerara ya ja ya zauna yana bin ta da kallo ba tare da ya ce mata komai ba, ita ma sai ta mayar da idanuwanta ta kulle. Can dai yayi murmushi ya ce
“Jira kike na fara miki magana ko Lily?”
Bakin ta ta ɗan turo gaba tace
“To ai Ni ce ba Ni da lafiya kai za ka gaida ni”
Mamaki da al'ajabi suka cika shi jin zancenta sai ya danganta hakan da larurar ta.
“Is alright good morning Lily, ya jikin ki?”
Baki ture ta amsa da “Da sauƙi”
Murmushi yayi ganin dai yau tabbas da rigima ta tashi
“Ok speedy recovery dear, an jima za mu koma gida, kin shirya?”

*React please and help me share this update please.*
*I'm alerting you with my precious 2025 story Ruɗin Zamani which I'll be starting May be tomorrow or day after tomorrow, sai dai paid book ne, amma In na samu reactions daga gare ku zan mayar da shi free, soyayyar ku kaɗai nake buƙata.*

[1/12, 11:52 AM] Diamond Bhatool:
https://whatsapp.com/channel/0029VanUFkw5kg7G2ci16o2X

*🏡A BABBAN GIDA🏡*
*TAKUN ƘARSHE*
*©Diamond Bhatool*

*💎💍ELITE DIAMOND WRITERS💍💎*
_Where diamonds shine, words ignite_

_Wattpad: @diamond_bhatool_
_Arewabooks: @diamondbhatool3_
Please follow

*PAGE* 2️⃣2️⃣

                                  ﷽

Yamutsa fuska tayi tace “Uhm” daga haka kowa yayi shiru, nashi ɓangaren yana tunanin why is Lilyn Yaya so quite nata ɓangaren tana ƙoƙarin koyawa zuciyarta cire soyayyar sa da ta shige shi ba zata.

Abincin ya fara fitarwa sannan ya ɗaura a bedside locker, bayan ya zuba mata papper soup ɗin da Hajjaty ta yi mata ya ce “O Yah Lily tashi, hope kin yi salla ma”
Kai ta gyaɗa masa
“Ok tashi ki ci abinci” da sauri ta miƙe saboda yunwar da take ji. Kaɗan taci daga nan ta sha fruits ɗin da ya ke miƙa mata. Sai da tayi nak tukun tayi ƙoƙarin komawa ta kwanta.
“No Lily, Bari abincin ya gama shiga kada ki ce za ki kwanta kin ji?”

Ba a daɗe ba aka yi discharge nata, bayan ya gama settling komai da taimakon sa suka fice sai Abatcha estate. Daga nan kuma ya damƙa ta hannun Hajjaty saboda yana son a haɗa lefen bikin sa ta hannun Mommy Nasiba wacce take matsayin ya ga Mommah.

Ba shi ya dawo ba sai da yamma, ko da ya shigo bai tarar da kowa ba, direct bedroom ɗinta ya nufa and luckily yana nocking yaji ta bashi amsa da “Come in”
A kwance ya tarar da ita, ganin shi ne sai ta turo baki gaba, sarai ya ganta amma sai ya sake kamar bai ga ba. Sai da ya zauna gefen Bed ɗin yace
“In kina tura min bakin nan Lilyn Yaya zan yanke shi”
Kamar bata ji ba ta ƙara tura bakin wanda hakan ya shagaltar da shi ga kallonta ba tare da kifta ido ba na tsawon minti guda da wasu sakanni. Kallon nasa da taga ya yi yawa yasa ta langwaɓe kai tana faɗin
“Ni ka bar kallo na Yaya”
Kansa ya kawar gefe ya haɗe fuskar nan sannan yace
“Wa ya ce miki kallon ki nake, ina duba yanayin jikin ki ne ko akwai progress, ba wannan ba ba na son Wasa Lily, ki faɗa min gaskiya me yake damunku, wace damuwa kike da ita da take shirin jefa ki ga wani yanayi na daban?”

Shiru tayi tare da mayar da kallonta ƙasa, a ɗan kausashe yace
“Kin ga Lily, bana son Shirun Nan, don't let me repeat myself”
Fuska a shagwaɓe tace
“Yaya babu komai fa”
Hararar da ya banko mata yasa ta mayar da hankalinta.
“Eh ah ah Yaya ba komai da gaske nake nima kawai zazzaɓi nake”

“Will You shut up?” ya dakatar da ita
“Idan ba ki faɗa min ba wallahi sai na lahira ya fi ki jin daɗi, Ni sa'an ki ne?”
Jiki na rawa tuni hawaye suka wanke mata fuska, ta ya ma za ta iya ce masa soyayyar sa ce take shirin hallaka ta?, That's impossible.

Ganin hawaye a fuskarta ga kuma yadda ta tsorata yasa yace
“Is ok, daina kukan tunda ban dake ki ba, faɗa min me ke damun ki”
“Mama ce har yanzu ba ta dawo ba, kuma ina so na kalle ta.”
Nan ya fara lallashin ta yana ce mata Mama ta kusa dawowa in Sha Allah. Daga nan yace ta faɗi me take so zai siyo mata. Daga haka ya fice.

*Ina Mommah?*

Mommah dai har yanzu tana kan bakar ta na a fasa wannan aure wanda tuni har an fara shirye-shiryen sa. Ya ma za a yi a yi mata haka? Nan da nan ta tada hauka bisa zigin Aminanta, Daddy har tsoron shigowa gidan yake saboda bai san tsiyar da zai tarar ba. Abun nata har ya wuce nan ta kan shiga har sashrn Hajiya Babba ta mata tijara daga nan kuma ta nufi sashen Hajjaty nan ma ta sauƙe kwandon tsiyarta.

*A week later*

Cikin satin nan Zahrah ta koma makaranta sannan ta mayar da hankalinta ga karatun ta, ba wai don ta daina son Yaya Sadauki ba Amma a halin yanzu tana iya ɓoye feelings ɗin ta a game da shi yayin da kusancin su kuma ya Karu, kulawar da yake bata ta ninku.

A yau talata Zahrah, Nasreen, Zakiyya, Nainarh da kuma Rumaysa suka je amso ɗinkinsu daga wurin tailor. Sun ci Sa'a kuwa ɗinki ya kammala. Duk an ɗinka, ankon Dinner, Yini da kuma Family and friends day duk an gama. Nan ƴan matan suka biya tailor daga nan suka dawo gida.

Suna dawowa suka tarar an kawo lefen Aunty Mabruka. Bayan sun ajiye kayan su a Bedroom ɗin Zahrah suka dawo parlourn. Mommy Nasiba ce da kuma wasu yayyen Mommah suka kawo. Kaya ne na kuzo mu gani wanda duk idon da yayi tozali da su sai ya tabbatar Naira ta sha wahala. Su Mimie, Aunty Amarya da sauran matan gidan sai yaba kayan suke yayin da Mamie da Ammie ke jin zukatan su kamar su yi bunga musamman da suka ga kayan, kowaccen su cikin ranta tana faɗin da yanzu fa na ɗiyarta wannan dukiya da aka narka.

Basu bari an gama gani ba suka ɗunguma don kai report ga uwar ango, ai kuwa suka ɗaura ta kan layi, ba a jima ba sai ga ta ta shigo parlourn Hajjaty gadan-gadan, biye da ita kuma Ammie da Mamie ne. Tana isa ta ja burki ganin Yayyenta da ƙannenta a parlourn musamman da ta ga akwatunan da ke Baje a parlourn.

Kamar wacce aka hankaɗa ta nufi cikin parlourn sai ka ce mai taɓin hankali.
Sai da ta isa tsakiyar ta nuno Mommy Nasiba da yatsa
“Ashe har da ku ake cin amana ta Yaya? Ke ma har da ku?” ta fara nuna su ɗaya bayan ɗaya.
“Na rantse da Allah ba a isa an mun cin kashin nan ba, har ku ba zan bar ku ba, kuma ku kwashi kayanku don wallahi auren nan ba za a yi shi ba ko zan bar gidan nan.”

Galala Mommy Nasiba ke kallon Ƙanwar Tata musamman in ta tuna dama ba ta da kirki can da amma bata yi tsammanin rashin ɗa'arta ta kai haka ba.
“Haba Sughrah! Ashe ba ki da hankali ke?”

A gadarance Mommah ta rufe ido tace
“E ba Ni da shi, akan haka wallahi ko da me za a ƙira Ni ba zan ja da baya ba, ku kuma ɗaya bayan ɗaya sai na yi maganinku.”

“Haba Sughrah! Meye kike haka kamar marar ilimi?” Hajjaty ta faɗa tana tsare Mommah da ido.

“Ki ƙira Ni da marar ilimin kai tsaye Hajjaty, ai dama can ba so na kike yi ba, har zan ce ba na son haɗin auren amma a ƙi saboda Ni ba Ni da ƴanci? Tukunna ma wai akwai wanda ya haifa min ɗan ne?”
Ba shiri taji an ɗauke ta da mari, ba kowa bace sai Mommy Nasiba.

“Idan kina cin ƙasa ki kiyayi ta shuri! Hajjaty ai ba sa'ar yin ki bane In kin mana mun yi shiru ba zan zuba ido ki ɓata tarbiyyar gidan mu gaba na ba, shashasha kawai”

“Ni kika mara Yaya?”
“Ƙwarai kuwa Sughrah ke na mara”
“Ni kika mara ko yaya?” ta nuna kanta da yatsa har lokacin hannunta na kan kuncinta.

“Wallahi ba a isa ba, ko duniya za ta kifa sai an fasa auren nan, don me ma zan bar ɗa na ya auri matar da ta hana Ni shan iska a gidan aure na, ta toshe min duk wata kafa da zan sarara, wallahi ba zai auri Mabruka wacce ta gama yawon banza ba kam, never! Ɗa na Ni na haife shi saboda haka babu wanda ya isa yayi min iko da shi.”

“Ai ba ke kaɗai kika haife shi ba kuma ba ke kaɗai kike da iko da shi ba.” Muryar DADDY ta sauƙa a kunnenta. A zabure ta waiwayo sai kuma ta kama kunkumi tace
“Ai duk laifin ka ne Daddynsu, na ce bana so dole sai kun nuna min isa akan cikin da na raina na kuma haife har ya zama mutum?, Wallahi ka ji na rantse Umar wallahi sai an fasa auren nan ko kuma ran kowa ya ɓaci don ba zan bari a yi min cin kashin nan ba.”

Mommy Nasiba ce wannan karon take shirin ƙara saukewa Mommah wani marin taji Daddy yace
“Rabu da ita Hajiya Nasiba, ta gama haukarta babu abun da zai fasaya.”
Chapter 29 · 0% Book details