Sashe 30
A Babban Gida Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A harzuƙe Momma tace
“Ni Kake cewa mahaukaciya ko Umar? Wallahi za ka san ba ni da hankali, bari ku ga haukar, tattara kuɗin ɗa na zanyi na yi idan ya so ku da kuka nace sai ya yi auren kwa haɗa masa lefen.” nan ta kai hannun ta kan akwatunan tana faɗin
“Habiba ku zo ku taya Ni mu kwashe”
Sai a lokacin su Ammie suka fito don da a maƙale suke.
“Wallahi Sughrah kika kuskura kika taɓa abu anan zan ɓata miki rai.”
Dariyar takaico tayi tana mai kallon Daddy da fuskarsa ke ɗaure
“Wane ɓacin rai ne ban gani ba a wurin ka tunda Gashi yanzu ina gani kai da iyayenka masu gadarar tsiya kuna shirin nuna min iyaka kan ɗana.”
A harzuƙe wannan karen ma Mommy Nasiba ta Yo kanta sai dai Daddy ya dakatar da ita. Murya a kausashe yace
“Sughrah ki koma ɓangaren ki”
Tsoro ta ji kawai sai ta juya tana burga ta bar parlourn, muƙarrabanta suka bi bayanta.
Nan dai aka tattara kaya aka shiga da su ɗakin Alhaji Baba, Hajjaty sai haƙuri take ba wa su Mommy Nasiba, su ma suna bata haƙuri don ko ba komai yau ƴar'uwarsu ta sa sun ji kunya kuma ta ɓata wayonta.
Duk abun da yake faruwa Yaya Sadauki bai sani ba saboda yana can kan aikin neman Mama. Wuraren Isha ya dawo. Har aka yi sallah ya wuce da su Alhaji Baba babu wanda ya ba shi labarin abun da ya faru yau. Bayan ya yi Dinner ya nufi part ɗin su don ya huta.
A parlour ya ci karo da Daddy bayan sun gaisa yana shirin Hayewa sama ya dakatar da shi. Tsawon wasu mintuna suka kwashe suna magana ƙasa-ƙasa can dai yaya Sadauki ya wuce DADDY kuma ya ciro wayarsa ya kira Ya Junaid Wanda ke Abu Dhabi da zama tare da matarsa. Shi ma sun jima suna waya kafin nan ya yanke, nan ya wuce Bedroom ɗin Mommahn.
Bai tsaya ɓata lokaci ba ya kira sunanta sai tayi kamar ba ta san da wanzuwarsa ba, sarai kuma ya san ta ji ɗin tunda idonta biyu. Bulb ya kunna ai kuwa ta Zabura ta miƙe daga kan Bed ɗin
“Mallam ya za ka kunna min haske ina bacci”
Murmushin takaici ya saki yace
“Ba wani dogon zance ko rigima nazo ba, ba kuma shawara ko suggestion na bayar ba, umarni nake baki da...”
Shewa tayi tace
“Dama ta Nan ka fi kauri ai, sai iya ba da umarni kamar kai ka haifi mutum, Ni zan kwanta, idan ka gama ka kashe min bulb.”
Zata haye Bed yace
“Na ba ki yau zuwa gobe ki tattara kayan ki na sawa ki bar min gida, ban yadda ki ɗauki komai ba bayan kayan sawar ki sai ki tafi tunda ba ki daraja kowa a gidan.”
Duk da cewa jikinta yayi sanyi amma da ta tuna karatun da ta sha sai tace
“To sai me in na tafin, ta fi nono fari ai. Kuma wallahi ku tabbatar kun dakatar da bikin da kuke shirin yi ba izini na.”
Bai tsaya jin me zata ce ba ya wuce Bedroom ɗinsa Rai a ɓace.
Washegari kuwa da sassafe Daddy da zai fita ya shiga ya ƙara nanata mata cewa Kada ya dawo ya tarar da ita. Bata damu ba ta fara tattara kayanta sannan ta yi shirin ficewa, ATM card ɗin ta tayi wa neman duniyar nan amma bata gani ba, haka keys ɗin motarta babu alamun su nan jikin ta ya bata cewa Daddy ne ya ɗauke.
Wayarta ta ɗaga ta kira Number su Mamie cewa tana son ganinsu, ba jimawa kuwa ta suka zo, nan ta labarta musu halin da take ciki, sa yake su ƴan duniya ne suka ƙara ɗaura ta layin kada ta kuskura ta bari ayi auren nan tun da yanzu ya ce ta bar masa gida. Da wannan shawara suka wuce, Mommah kuma tayi amanna da ita.
Ba tare da ta damu ba kuwa ta haɗa ta fice, ko ta kan auta Ra'ees bata bi ba ta fice, daidaita ta hau bata tsaya ko ina ba sai gidansu.
Nan ta biya mai a daidaita kudinsa da sauran cash ɗin da ya rage mata. A bakin gate ta tsaya tana ƙarewa gidan kallo, babu laifi gida ne mai kyau sai dai kana gani za ka fahimci cewa masu gidan tsoffin masu kuɗi ne. Ko a mafarki ba ta jin za ta iya zaman gidan amma a haka ta daure ta jefa ƙafarta ciki.
*Ina buƙatar reactions ɗinku sosai my esteem people, don girman Allah na ci albarkacin Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallama a yi min share zuwa wasu groups ɗin. Thanks You so much, Diamond Bhatool taku ce🦋💞!*
[1/13, 9:42 AM] Diamond Bhatool:
https://vm.tiktok.com/ZMkaSGVu8/
*Please follow my Tiktok handle*
https://whatsapp.com/channel/0029VanUFkw5kg7G2ci16o2X
*🏡A BABBAN GIDA🏡*
*TAKUN ƘARSHE*
*©Diamond Bhatool*
*💎💍ELITE DIAMOND WRITERS💍💎*
_Where diamonds shine, words ignite_
_Wattpad: @diamond_bhatool_
_Arewabooks: @diamondbhatool3_
Please follow
*PAGE* 2️⃣3️⃣
﷽
Mahaifin Mommah ya daɗe da rasuwa, mahaifiyarta ce kawai a gidan sai kuma yayyenta maza uku da matansu tare da yaransu da suke zaune gidan.
Tun daga hanyar da zata sada ka da mai flt ɗin ta ci karo da ruwa kwalale a ƙasa, ɗage rigarta tayi tana yamutsa fuska kamar ta taka kashi. A main parlourn ta tarar da mahaifiyarta Hajja wacce ke zaune tana kallon SunnahTV. Sallama tayi ciki-ciki Hajja ta amsa tana aika mata wani mummunan kallo na za ki sani don tuni su Mommy Nasiba suka sanar da ita abun da ya faru.
Da yake ma can ba zuwa take ba tunda taga mijinta mai hali ne dama kuma can akwai ji da kai su Hajiya Sughrah sai ta janye ƙafafunta, sai ta share shekara bata ziyarci mahaifiyarta ba, amma su Yaya Sadauki suna zuwa duk juma'a su gaida Hajja.
Gaida Hajja Mommah tayi, ba tare da Hajja ta ɗago ba ta amsa daga haka bata ce komai ba sai da aka gama karatun tukun ta kashe TV ta juyo ta fuskanci Mommah fuska ɗaure.
“Ba dai zaman gidan kika zaɓa ba Sughrah? Madalla da ke! Ga can ɗaki sai ki zo ki gyara ki zauna tunda ba za ki taɓa yin hankali ba. Ai Umar ya kyauta ma da ya dawo dake, shashasha kawai.”
Kamar Mommah za ta saka kuka haka ta tashi ta nufi ɗakin da Hajja ta nuna mata, subhanallah! Sai da ta dafe ƙirji ganin yanayin ɗakin, ƙura ce cike da ɗakin ga kuma yana kamar an shekara goma ba a buɗe ba, abun da ya fi ɗaga mata hankali ko labule babu ga shi ko fanka babu a ɗakin. Kamar za ta yi kuka haka ta naɗe gyalenta ta ɗaure saman rigarta da kwalinta sannan ta fara shara, tsabar an dade ba a haɗu ba sai da idonta ya raina fata har shaƙewa numfashin ta yake. Da ƙyar ta gama ta nufi toilet ɗin ta fara share ƙurar da ke ciki. Ko da ta kunna ruwa tap ɗin ba ya zuwa, kamar za ta yi kuka ta fito ta tambayi Hajja. Amsar da Hajja ta bata ne ta sa gabanta bugawa.
“Ki tambayi su Rahina la'alla su ba ki, idan babu kuma sai ki fita waje ki ɗebo. Babu yadda ta iya haka ta nufi sashen babban yayansu Alhaji Kabir. Kallon arziƙi bata samu ba saboda dama sun tanadi wulaƙancin da za su mata musamman da ya kasance umarnin Hajja ne. Kamar wacce lakar ta ta saki ta ƙaraso. Ba tare da ta gaishe da Aunty Rahina ba tace
“Ki ɗan san min ruwa zan wanke bayi”
Hararar ta Aunty Rahina tayi tace
“ki ɗauki plastic ɗaya daga haka kar ki dawo saboda wuta ta ɓaci ba lallai mu samu ruwan ba.”
Babu yadda ta iya ta buɗe randar ta fara zuba ruwan a plastic ɗin sai dai kafin ta gama tuni ta gaji saboda a gidan ta iyakaci ba da umarni ne. Ƙasa ɗaukar ruwan tayi ta juyo tana kallon Aunty Rahina.
“Don Allah ki taimaka ki miƙa min wallahi na kasa”
Abun mamaki wai yau Sughrah ce ke haɗa ta da Allah? Kamar ba zata ɗauka ba sai kuma ta ɗauka mata ta kai mata. Mommah tace “Na gode”
Daga haka ta wanke bayin sai yamutsa fuska take..
Bayan ta gama ta shimfida tabarma a sabon ɗakinta ta zauna, nan ta jera kaya sannan ta kira Ammie take sanar da ita ta iso, bayan ta gama mata karatu ta fara laluɓen Numbern Yaya Sadauki coz akwai abubuwan da za ta buƙata amma Numbern ba ya shiga. Duk abun da Mommah take yi a kan idon Hajjja ne, jijjiga kai kawai ta yi tana mata fatan shiriya.
*Yaya Sadauki*
Aka ce biki ya yi biki, zaune yake shi da Ya Khalil sai kuma wasu friends ɗin su da Ya Khalil ɗin ya gayyato waɗanda suka iso safiyar yau. Ban da tsokanarsa babu abun da suke shi kuma mutumin ya tsuke fuska kamar a filin daga. Kamar wanda aka tsikara ya ciro wayarsa, Mommah ce ta fara faɗo masa a rai amma sai ya sauya fuska yana yamutsa ta, Numbern Hajjaty ya lalaɓo ya dannawa Kira, cikin Sa'a kuwa wayar na hannunta. Suna gaisawa ya miƙe zai fice sai tsiya suke masa ba tare da sun san wane irin ware zai yi ba. Tambayar Hajjatyn yayi ko Zahrah na nan, tace “Gaskiya to bari dai na duba,sun dai ce za su karɓo ɗinkin su ita da su Nasreen” jim yayi kafin yace
“Don Allah ki duba min ita Hajjaty.”
Katse kiran Hajjaty tayi taje dubo Zahrah.
Yana zaune ba tare da ya ce da su komai ba wayarsa ta yi ringing.
“A'a ta ƙira fa! Wannan kuwa za ta bar mu da abokin?” Ya Salim ya faɗa yana ɗage masa gira. Ba tare da ya ɗaga kiran ba har ya katse ya dubi Ya Salim yayi murmushin takaici kana ya miƙe, kiran Hajjaty ya bi, bayan ta ɗaga tace masa “Ga Zahra'un”
Jin shiru ba a yi magana ba yasa Zahrah faɗin
“Hi! Who's on the line?”
Gyaran murya yayi, lokacin ta fahimci waye ne.
“Ah Yaya Kai ne?” ba tare da ta jira amsarsa ba tace
“Hajjaty tace za ka yi magana da Ni ”
“Ni Kake cewa mahaukaciya ko Umar? Wallahi za ka san ba ni da hankali, bari ku ga haukar, tattara kuɗin ɗa na zanyi na yi idan ya so ku da kuka nace sai ya yi auren kwa haɗa masa lefen.” nan ta kai hannun ta kan akwatunan tana faɗin
“Habiba ku zo ku taya Ni mu kwashe”
Sai a lokacin su Ammie suka fito don da a maƙale suke.
“Wallahi Sughrah kika kuskura kika taɓa abu anan zan ɓata miki rai.”
Dariyar takaico tayi tana mai kallon Daddy da fuskarsa ke ɗaure
“Wane ɓacin rai ne ban gani ba a wurin ka tunda Gashi yanzu ina gani kai da iyayenka masu gadarar tsiya kuna shirin nuna min iyaka kan ɗana.”
A harzuƙe wannan karen ma Mommy Nasiba ta Yo kanta sai dai Daddy ya dakatar da ita. Murya a kausashe yace
“Sughrah ki koma ɓangaren ki”
Tsoro ta ji kawai sai ta juya tana burga ta bar parlourn, muƙarrabanta suka bi bayanta.
Nan dai aka tattara kaya aka shiga da su ɗakin Alhaji Baba, Hajjaty sai haƙuri take ba wa su Mommy Nasiba, su ma suna bata haƙuri don ko ba komai yau ƴar'uwarsu ta sa sun ji kunya kuma ta ɓata wayonta.
Duk abun da yake faruwa Yaya Sadauki bai sani ba saboda yana can kan aikin neman Mama. Wuraren Isha ya dawo. Har aka yi sallah ya wuce da su Alhaji Baba babu wanda ya ba shi labarin abun da ya faru yau. Bayan ya yi Dinner ya nufi part ɗin su don ya huta.
A parlour ya ci karo da Daddy bayan sun gaisa yana shirin Hayewa sama ya dakatar da shi. Tsawon wasu mintuna suka kwashe suna magana ƙasa-ƙasa can dai yaya Sadauki ya wuce DADDY kuma ya ciro wayarsa ya kira Ya Junaid Wanda ke Abu Dhabi da zama tare da matarsa. Shi ma sun jima suna waya kafin nan ya yanke, nan ya wuce Bedroom ɗin Mommahn.
Bai tsaya ɓata lokaci ba ya kira sunanta sai tayi kamar ba ta san da wanzuwarsa ba, sarai kuma ya san ta ji ɗin tunda idonta biyu. Bulb ya kunna ai kuwa ta Zabura ta miƙe daga kan Bed ɗin
“Mallam ya za ka kunna min haske ina bacci”
Murmushin takaici ya saki yace
“Ba wani dogon zance ko rigima nazo ba, ba kuma shawara ko suggestion na bayar ba, umarni nake baki da...”
Shewa tayi tace
“Dama ta Nan ka fi kauri ai, sai iya ba da umarni kamar kai ka haifi mutum, Ni zan kwanta, idan ka gama ka kashe min bulb.”
Zata haye Bed yace
“Na ba ki yau zuwa gobe ki tattara kayan ki na sawa ki bar min gida, ban yadda ki ɗauki komai ba bayan kayan sawar ki sai ki tafi tunda ba ki daraja kowa a gidan.”
Duk da cewa jikinta yayi sanyi amma da ta tuna karatun da ta sha sai tace
“To sai me in na tafin, ta fi nono fari ai. Kuma wallahi ku tabbatar kun dakatar da bikin da kuke shirin yi ba izini na.”
Bai tsaya jin me zata ce ba ya wuce Bedroom ɗinsa Rai a ɓace.
Washegari kuwa da sassafe Daddy da zai fita ya shiga ya ƙara nanata mata cewa Kada ya dawo ya tarar da ita. Bata damu ba ta fara tattara kayanta sannan ta yi shirin ficewa, ATM card ɗin ta tayi wa neman duniyar nan amma bata gani ba, haka keys ɗin motarta babu alamun su nan jikin ta ya bata cewa Daddy ne ya ɗauke.
Wayarta ta ɗaga ta kira Number su Mamie cewa tana son ganinsu, ba jimawa kuwa ta suka zo, nan ta labarta musu halin da take ciki, sa yake su ƴan duniya ne suka ƙara ɗaura ta layin kada ta kuskura ta bari ayi auren nan tun da yanzu ya ce ta bar masa gida. Da wannan shawara suka wuce, Mommah kuma tayi amanna da ita.
Ba tare da ta damu ba kuwa ta haɗa ta fice, ko ta kan auta Ra'ees bata bi ba ta fice, daidaita ta hau bata tsaya ko ina ba sai gidansu.
Nan ta biya mai a daidaita kudinsa da sauran cash ɗin da ya rage mata. A bakin gate ta tsaya tana ƙarewa gidan kallo, babu laifi gida ne mai kyau sai dai kana gani za ka fahimci cewa masu gidan tsoffin masu kuɗi ne. Ko a mafarki ba ta jin za ta iya zaman gidan amma a haka ta daure ta jefa ƙafarta ciki.
*Ina buƙatar reactions ɗinku sosai my esteem people, don girman Allah na ci albarkacin Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallama a yi min share zuwa wasu groups ɗin. Thanks You so much, Diamond Bhatool taku ce🦋💞!*
[1/13, 9:42 AM] Diamond Bhatool:
https://vm.tiktok.com/ZMkaSGVu8/
*Please follow my Tiktok handle*
https://whatsapp.com/channel/0029VanUFkw5kg7G2ci16o2X
*🏡A BABBAN GIDA🏡*
*TAKUN ƘARSHE*
*©Diamond Bhatool*
*💎💍ELITE DIAMOND WRITERS💍💎*
_Where diamonds shine, words ignite_
_Wattpad: @diamond_bhatool_
_Arewabooks: @diamondbhatool3_
Please follow
*PAGE* 2️⃣3️⃣
﷽
Mahaifin Mommah ya daɗe da rasuwa, mahaifiyarta ce kawai a gidan sai kuma yayyenta maza uku da matansu tare da yaransu da suke zaune gidan.
Tun daga hanyar da zata sada ka da mai flt ɗin ta ci karo da ruwa kwalale a ƙasa, ɗage rigarta tayi tana yamutsa fuska kamar ta taka kashi. A main parlourn ta tarar da mahaifiyarta Hajja wacce ke zaune tana kallon SunnahTV. Sallama tayi ciki-ciki Hajja ta amsa tana aika mata wani mummunan kallo na za ki sani don tuni su Mommy Nasiba suka sanar da ita abun da ya faru.
Da yake ma can ba zuwa take ba tunda taga mijinta mai hali ne dama kuma can akwai ji da kai su Hajiya Sughrah sai ta janye ƙafafunta, sai ta share shekara bata ziyarci mahaifiyarta ba, amma su Yaya Sadauki suna zuwa duk juma'a su gaida Hajja.
Gaida Hajja Mommah tayi, ba tare da Hajja ta ɗago ba ta amsa daga haka bata ce komai ba sai da aka gama karatun tukun ta kashe TV ta juyo ta fuskanci Mommah fuska ɗaure.
“Ba dai zaman gidan kika zaɓa ba Sughrah? Madalla da ke! Ga can ɗaki sai ki zo ki gyara ki zauna tunda ba za ki taɓa yin hankali ba. Ai Umar ya kyauta ma da ya dawo dake, shashasha kawai.”
Kamar Mommah za ta saka kuka haka ta tashi ta nufi ɗakin da Hajja ta nuna mata, subhanallah! Sai da ta dafe ƙirji ganin yanayin ɗakin, ƙura ce cike da ɗakin ga kuma yana kamar an shekara goma ba a buɗe ba, abun da ya fi ɗaga mata hankali ko labule babu ga shi ko fanka babu a ɗakin. Kamar za ta yi kuka haka ta naɗe gyalenta ta ɗaure saman rigarta da kwalinta sannan ta fara shara, tsabar an dade ba a haɗu ba sai da idonta ya raina fata har shaƙewa numfashin ta yake. Da ƙyar ta gama ta nufi toilet ɗin ta fara share ƙurar da ke ciki. Ko da ta kunna ruwa tap ɗin ba ya zuwa, kamar za ta yi kuka ta fito ta tambayi Hajja. Amsar da Hajja ta bata ne ta sa gabanta bugawa.
“Ki tambayi su Rahina la'alla su ba ki, idan babu kuma sai ki fita waje ki ɗebo. Babu yadda ta iya haka ta nufi sashen babban yayansu Alhaji Kabir. Kallon arziƙi bata samu ba saboda dama sun tanadi wulaƙancin da za su mata musamman da ya kasance umarnin Hajja ne. Kamar wacce lakar ta ta saki ta ƙaraso. Ba tare da ta gaishe da Aunty Rahina ba tace
“Ki ɗan san min ruwa zan wanke bayi”
Hararar ta Aunty Rahina tayi tace
“ki ɗauki plastic ɗaya daga haka kar ki dawo saboda wuta ta ɓaci ba lallai mu samu ruwan ba.”
Babu yadda ta iya ta buɗe randar ta fara zuba ruwan a plastic ɗin sai dai kafin ta gama tuni ta gaji saboda a gidan ta iyakaci ba da umarni ne. Ƙasa ɗaukar ruwan tayi ta juyo tana kallon Aunty Rahina.
“Don Allah ki taimaka ki miƙa min wallahi na kasa”
Abun mamaki wai yau Sughrah ce ke haɗa ta da Allah? Kamar ba zata ɗauka ba sai kuma ta ɗauka mata ta kai mata. Mommah tace “Na gode”
Daga haka ta wanke bayin sai yamutsa fuska take..
Bayan ta gama ta shimfida tabarma a sabon ɗakinta ta zauna, nan ta jera kaya sannan ta kira Ammie take sanar da ita ta iso, bayan ta gama mata karatu ta fara laluɓen Numbern Yaya Sadauki coz akwai abubuwan da za ta buƙata amma Numbern ba ya shiga. Duk abun da Mommah take yi a kan idon Hajjja ne, jijjiga kai kawai ta yi tana mata fatan shiriya.
*Yaya Sadauki*
Aka ce biki ya yi biki, zaune yake shi da Ya Khalil sai kuma wasu friends ɗin su da Ya Khalil ɗin ya gayyato waɗanda suka iso safiyar yau. Ban da tsokanarsa babu abun da suke shi kuma mutumin ya tsuke fuska kamar a filin daga. Kamar wanda aka tsikara ya ciro wayarsa, Mommah ce ta fara faɗo masa a rai amma sai ya sauya fuska yana yamutsa ta, Numbern Hajjaty ya lalaɓo ya dannawa Kira, cikin Sa'a kuwa wayar na hannunta. Suna gaisawa ya miƙe zai fice sai tsiya suke masa ba tare da sun san wane irin ware zai yi ba. Tambayar Hajjatyn yayi ko Zahrah na nan, tace “Gaskiya to bari dai na duba,sun dai ce za su karɓo ɗinkin su ita da su Nasreen” jim yayi kafin yace
“Don Allah ki duba min ita Hajjaty.”
Katse kiran Hajjaty tayi taje dubo Zahrah.
Yana zaune ba tare da ya ce da su komai ba wayarsa ta yi ringing.
“A'a ta ƙira fa! Wannan kuwa za ta bar mu da abokin?” Ya Salim ya faɗa yana ɗage masa gira. Ba tare da ya ɗaga kiran ba har ya katse ya dubi Ya Salim yayi murmushin takaici kana ya miƙe, kiran Hajjaty ya bi, bayan ta ɗaga tace masa “Ga Zahra'un”
Jin shiru ba a yi magana ba yasa Zahrah faɗin
“Hi! Who's on the line?”
Gyaran murya yayi, lokacin ta fahimci waye ne.
“Ah Yaya Kai ne?” ba tare da ta jira amsarsa ba tace
“Hajjaty tace za ka yi magana da Ni ”