Sashe 44
A Babban Gida Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da misalin 'karfe tara na safe aka fito da gawarsa zuwa parlourn Hajjaty saboda mutane sun riga sun taru za a masa salla. Ko da aka ce Hajjaty ta masa addu'a cike da 'karfin hali ta matso kusa da gawar tasa da ke 'kamshin turare ba tare da ta bu'de fuskar ba ta ha'da hannayenta tana masa addu'a, bayan ta kammala Alhaji Baba ya dubi Mommah yace ita ma in za ta kalle shi to, da sauri ta 'karaso gaban gawar ta tsugunna hawaye na zuba daga idanuwanta ta ha'de nata hannayen ta fara jera masa addu'o'i. Ko da ta gama aka 'daga gawar da niyyar ficewa da ita don a sallace ta kwatsam Zahrah da ke 'dakinta ta fito da gudu ta zube 'kasa tare da ri'ke 'kafar Papa da ke ri'ke da makarar tana fa'din
"Ku yi wa Allah ku yi wa manzon tsira ku ajiye min Yaya na, wallahi bai mutu ba, da ransa kada ku bisne shi. Papa ka duba ka ga Yaya ya ce min zai zo min da dadda'dan labari amma kuce ya rasu? Wallahi Yaya na bai mutu ba, Yaya ka duba Lilynka ce fa" ta fa'da tana sakin wani irin murmushi
"Ka tashi daga makarar nan ba wurin zamanka bane, Yaya ka bar wannan wasan da Lily..."
Fahimtar ba ta cikin hayyacinta yasa su Aunty Na'eemah da su Mimie suka ri'ke ta su kuma su Daddy suka fice da gawar, da 'kyar suka tisa ta gaba ta yadda ta koma bedroom nata wasu irin zafafan hawaye na zuba a idanuwanta.
Nan aka wuce da Yaya Sadauki aka masa sallah sannan aka raka shi makwancinsa.
Tsawon wannan kwanaki biyu na rasuwar Yaya Sadauki, akwai mata da kuma 'ya'yan da ban ga giftawarsu ba cikin ahalin bare a yi tunanin za a yi zaman jimami a tare da su. Bayan kwana uku kuma Alhaji Baba yace kowa ya kama nasa wurin, a ci gaba da yi wa Yaya Sadauki addu'ar Allah yasa ya dace. Babu wanda ya tsallake wannan umarni na Alhaji Baba duk aka watse, Aunty Madina da mijinta da kuma sirkanta suka koma, Yaya Junaid ma ya koma haka Yaya Haidar.
'Bangaren Hajjaty ya rage daga ita sai Alhaji Baba sai kuma Zahrah wacce har yau ba ta farfa'do ba, magana ma ba ta 'kara yi ba tun lokacin da aka fice da gawar Yaya Sadauki. Nainarh wacce yanzu suke kwana tare da Zahrah ta yi iyakar iyawarta wurin ta sa Zahrah ta mance da Yaya amma abun ya fasaya, hakan yasa Hajiya Babba tace daga ita har Nainarh su tattaro su dawo part 'dinta idan ya so Ra'ees ya zauna tare da Hajjatyn.Da haka Zahrah tattara ta koma can 'din ba don ta so hakan ba.
Haka dai rayuwar taci gaba da tafiya, rashin wani ba zai sa a rasa wani ba, kowa da dalilin da ya sa ubangiji ya busa masa rai. Sati da guda da wannan rashi su Zahrah suka fara shirye-shiryen rubuta JAMB nasu, saboda haka suka koma makaranta kamar dai da amma Zahrah har yanzu ta kasa komawa daidai, gaba 'daya ta rame kamar ba Zahrah ba kuma har yau 'din ta kasa amincewa da cewa Yayanta ya rasu, gani take kamar wata rana zai dawo gare ta.
A matu'kar wahale ta dawo daga school saboda yadda azumi ya fara bata wahala coz sai a yau 'din ne ta fara. A part 'din Hajjaty ta yada zango saboda tana bu'katar hutu, can kuma in ta koma ba za su barta ta rintsa ba don ita ka'dai tasan yadda take ji a jikinta. Wayarta da ba ta iya rabuwa da ita a halin yanzu ta jefa gefe kana ta baje kan bed nata.
Ko da lokacin shan ruwa yayi Zahrah ta koma wurin 'yan'uwanta, bayan an sha ruwa suka gabatar da sallarsu ta maghrib daga nan kuma suka mi'ke don zuwa sannu da shan ruwa ga sauran jama'ar ahalin kamar yadda suka tsara, sai da suka ziyarci kowanne part na gidan, idan akwai squad member nasu sai su ha'du su 'kara gaba, bayan sun zaga ko'ina na gidan suka nufi part 'din Hajjaty. Tun daga door step gaban Zahrah ya buga har sai da ta 'dan dakata. Nainarh ta kalleta tace
"Ya dai Zahrah" kanta ta kawar gefe ba tare da ta ce komai ba ta fara 'ko'karin shigewa, hakan yasa ita ma Nainarh ta bi bayanta suka shige.
Wasu ba'ki ne guda hu'du a zaune a parlourn tare da Hajjaty sai dai ba ka oya gane su wane ne saboda yanayin hasken 'dakin...dim light ne shiyasa. Cike da girmamawa suka 'karasa suna gaida ba'kin sai dai kamar yadda suka shigo ashe cikin ba'kin akwai wacce ba ta gaida Hajjaty ba, still dai ba kuma ta amsa gaisuwar su Zahrah ba a wannan karon. Ra'ees ne da 'dan banzan rigimarsa ya taho da gudu ya kunna light sannan ya yo gurin Hajjaty.
ko da aka kunna hasken abun da Zahrah ta fara cin karo da shi ya matu'kar sa bugun zuciyarta 'kara tsananta bugu, kamar a mafarki! Saboda ta farfa'do daga sumar tsayen da tayi ta murza idanuwanta da hannunta don 'kara confirming abun da idonta ya gani, gaskiya ba daidai ya nuna mata ba wannan karon ma hakan yasa Zahrah ta fara marin fuskarta tana fa'din "Farka farka Zahrah"
Tana 'kara bu'de idanuwanta dai same abu haka take gani.
_Hajjaty_ tun da haske ya gama gauraye parlourn ta kai dubanta ga ba'kin, idan har mai karatu ya san ru'du, to Hajjaty ta shiga wani irin hali na ru'du, waye take gani haka gabanta?
"Nooo that could not be her, ba ita bace" tayi reassuring kanta.
Ihun da Zahrah ta buga tana nufar 'daya daga cikin ba'kin tana ihu tana fa'din
"Mamah na!" Sai kuma ta 'kara hugging nata tightly kamar za a 'kwace ta daga gareta. Wannan ihu da Zahrah tayi shi ya dawo da Hajjaty daga duniyar tunani, tabbas ba gizo Madina take mata ba,'diyarta ce yau ta dawo gareta, nan hawaye suka fara wanke fuskar Hajjaty, Zahrah ce ta raba jikinta da na Mamah ba tare da hawayen fuskarta sun daina zuba ba.
"Mamah yau kam kin dawo..." bata ida fa'din abunda za ta ce ba taga Hajjaty rungume da Mamar dukkansu sai kuka suke. Babu wanda yayi 'ko'karin raba su haka aka bar su suna kukansu, they deserve to cry, kusan shekaru ashirin yanzu rabonsu da juna, dole kuwa su koka.
Nasreen, Nainah, Rumaysa, Zakiyya da yanzu sun fahimci cewa Mamah ce ta dawo yasa suma suka fara zubar da 'kwallar farin ciki tare da dawowa suka rungume Zahrah a tare. Inna, Asma'u da kuma Balkisu wa'danda su suka rako Mama su ma mamaki ya gama cika su musamman yadda suka ga Mama da Hajjaty na kukan farin ciki, hakan ya 'kara tabbatar musu da cewa ba 'karamar soyayya da sha'kuwa bace tsakaninsu.
Bayan an share mintuna goma da wasu sakannin ana kuka suka raba jikinsu koma na duban kowa. Hajjaty tana hawaye tace "Madina yau ke kika dawo? Farin cikin da na rasa tsawon shekarun nan yau ya dawo! Alhamdulillah" sai kuma ta sau'ka ta zube 'kasa tayi sujjada, itama Mamah sai ta bi bayan Hajjaty tayi sujjadar, sosai sauran mutanen suka bi su da murmushi da kuma tausayawa. Hajjaty da ta tashi ta dubi Hajjaty tace "Maza 'diyata tashi ki shiga ki yi wanka kafin a sanarwa Alhaji Baba da zuwanki ko?"
"Ke Zahrah kai ta bedroom 'dina,ba'kin kuma ki kai su naki kafin Laraba ta gyara musu wurin kwanansu" Kallon ba'kin tayi tace "Ku samu ku watsa ruwa sai ku ci abinci, Allah yasa dai ba da azumin kuka zo ba"
Murmushi Inna tayi tana kallo Hajjaty tana kuma yaba kirki da sau'kin kan Hajjaty tace "A'a ai da yake tafiyar mai tsayi ce shiyasa bamu 'dau azumin ba"
"Masha Allah, ku bi Zahrah ta 'karasa daku ko?" Hajjaty ta fa'da tana 'kwala kiran Laraba, ko da ta zo ta fa'da mata dalilin kiran sai ta wuce dining don taga me ya rage tunda ba a yi girki da su ba, an sha ruwa kuma in ta ce laraba tayi ita ma ta san ta gaji.
*MOMMAH*
Sosai wasu 'dabi'unta suka sauya sakamakon yadda rashin 'danta ya ta'ba ta, wannan hali na izza da kuma nuna isa duk babu shi, babu wannan rashin girmama manyan...haka dai duk ta koma ga ubangijinta, Sallah take tana addu'a babu dare ba rana ko Allah zai sa Daddy ya mayar da ita gidanta don nadama kam ta riga ta yi ta. A yau kuma ta kuduri aniyar tabbatar da maganar Hajjanta game da 'kawayenta wa'danda suka juya mata baya lokaci guda, kayan takaicin shine duk cikinsu babu waccetaga wulgwarta a rasuwar Yaya Sadauki, ta kuma 'kullace su za ta ji dalilinsu na 'kin ko da yi mata ta'aziyya ne.
Wannan kenan!
*React and Share please*
*For those who share, jazakumullahu khairan, Allah bar ni da ku masu 'kamshin humra.*
[1/23, 3:05 PM] Diamond Bhatool:
*🏡A BABBAN GIDA🏡*
*TAKUN ƘARSHE*
*©Diamond Bhatool*
*💎💍ELITE DIAMOND WRITERS💍💎*
_Where diamonds shine, words ignite_
_Wattpad: @diamond_bhatool_
_Arewabooks: @diamondbhatool3_
Please follow
*PAGE* 3️⃣3️⃣
﷽
Tabbas cikin wannan family babu wanda suke having good time fiye da Ammie, amma wai ace har a mata rasuwa ba za ta iya kira ko a waya ta mata ta'aziyya ba? Meye amfanin abotar. A matu'kar raunane ta wuce part 'dinta na da tana share 'kwalla tare da fatan Allah yasa wata rana tana da rabon sake rayuwa ciki. A haka har ta iso part 'din Ammie. Da sallama ta shiga ciki amma bakinta kusan biyar tukun Ammie ta amsa, sarai ta gane muryar Mommah amma ta share, sai da ta shafe kusan mintuna biyar tukun ta aiko Afifa ta shigo da ita.
A dadda'kile suka gaisa don kuwa nunawa tayi kamar ba ta san Mommah ba, tarin mamaki da al'ajabi suka cika Mommah duk takaicin kanta ya kama ta. A da idan ta zo wurinta takan ka'da yaran 'dakunan su tukun ta fuskanci Mommah, amma a yau sai ta ha'de girar sama da 'kasa ta 'daura 'kafarta 'daya kan 'daya. Gauron numfashi Mommah ta sau'ke kana ta fara magana.
"Ku yi wa Allah ku yi wa manzon tsira ku ajiye min Yaya na, wallahi bai mutu ba, da ransa kada ku bisne shi. Papa ka duba ka ga Yaya ya ce min zai zo min da dadda'dan labari amma kuce ya rasu? Wallahi Yaya na bai mutu ba, Yaya ka duba Lilynka ce fa" ta fa'da tana sakin wani irin murmushi
"Ka tashi daga makarar nan ba wurin zamanka bane, Yaya ka bar wannan wasan da Lily..."
Fahimtar ba ta cikin hayyacinta yasa su Aunty Na'eemah da su Mimie suka ri'ke ta su kuma su Daddy suka fice da gawar, da 'kyar suka tisa ta gaba ta yadda ta koma bedroom nata wasu irin zafafan hawaye na zuba a idanuwanta.
Nan aka wuce da Yaya Sadauki aka masa sallah sannan aka raka shi makwancinsa.
Tsawon wannan kwanaki biyu na rasuwar Yaya Sadauki, akwai mata da kuma 'ya'yan da ban ga giftawarsu ba cikin ahalin bare a yi tunanin za a yi zaman jimami a tare da su. Bayan kwana uku kuma Alhaji Baba yace kowa ya kama nasa wurin, a ci gaba da yi wa Yaya Sadauki addu'ar Allah yasa ya dace. Babu wanda ya tsallake wannan umarni na Alhaji Baba duk aka watse, Aunty Madina da mijinta da kuma sirkanta suka koma, Yaya Junaid ma ya koma haka Yaya Haidar.
'Bangaren Hajjaty ya rage daga ita sai Alhaji Baba sai kuma Zahrah wacce har yau ba ta farfa'do ba, magana ma ba ta 'kara yi ba tun lokacin da aka fice da gawar Yaya Sadauki. Nainarh wacce yanzu suke kwana tare da Zahrah ta yi iyakar iyawarta wurin ta sa Zahrah ta mance da Yaya amma abun ya fasaya, hakan yasa Hajiya Babba tace daga ita har Nainarh su tattaro su dawo part 'dinta idan ya so Ra'ees ya zauna tare da Hajjatyn.Da haka Zahrah tattara ta koma can 'din ba don ta so hakan ba.
Haka dai rayuwar taci gaba da tafiya, rashin wani ba zai sa a rasa wani ba, kowa da dalilin da ya sa ubangiji ya busa masa rai. Sati da guda da wannan rashi su Zahrah suka fara shirye-shiryen rubuta JAMB nasu, saboda haka suka koma makaranta kamar dai da amma Zahrah har yanzu ta kasa komawa daidai, gaba 'daya ta rame kamar ba Zahrah ba kuma har yau 'din ta kasa amincewa da cewa Yayanta ya rasu, gani take kamar wata rana zai dawo gare ta.
A matu'kar wahale ta dawo daga school saboda yadda azumi ya fara bata wahala coz sai a yau 'din ne ta fara. A part 'din Hajjaty ta yada zango saboda tana bu'katar hutu, can kuma in ta koma ba za su barta ta rintsa ba don ita ka'dai tasan yadda take ji a jikinta. Wayarta da ba ta iya rabuwa da ita a halin yanzu ta jefa gefe kana ta baje kan bed nata.
Ko da lokacin shan ruwa yayi Zahrah ta koma wurin 'yan'uwanta, bayan an sha ruwa suka gabatar da sallarsu ta maghrib daga nan kuma suka mi'ke don zuwa sannu da shan ruwa ga sauran jama'ar ahalin kamar yadda suka tsara, sai da suka ziyarci kowanne part na gidan, idan akwai squad member nasu sai su ha'du su 'kara gaba, bayan sun zaga ko'ina na gidan suka nufi part 'din Hajjaty. Tun daga door step gaban Zahrah ya buga har sai da ta 'dan dakata. Nainarh ta kalleta tace
"Ya dai Zahrah" kanta ta kawar gefe ba tare da ta ce komai ba ta fara 'ko'karin shigewa, hakan yasa ita ma Nainarh ta bi bayanta suka shige.
Wasu ba'ki ne guda hu'du a zaune a parlourn tare da Hajjaty sai dai ba ka oya gane su wane ne saboda yanayin hasken 'dakin...dim light ne shiyasa. Cike da girmamawa suka 'karasa suna gaida ba'kin sai dai kamar yadda suka shigo ashe cikin ba'kin akwai wacce ba ta gaida Hajjaty ba, still dai ba kuma ta amsa gaisuwar su Zahrah ba a wannan karon. Ra'ees ne da 'dan banzan rigimarsa ya taho da gudu ya kunna light sannan ya yo gurin Hajjaty.
ko da aka kunna hasken abun da Zahrah ta fara cin karo da shi ya matu'kar sa bugun zuciyarta 'kara tsananta bugu, kamar a mafarki! Saboda ta farfa'do daga sumar tsayen da tayi ta murza idanuwanta da hannunta don 'kara confirming abun da idonta ya gani, gaskiya ba daidai ya nuna mata ba wannan karon ma hakan yasa Zahrah ta fara marin fuskarta tana fa'din "Farka farka Zahrah"
Tana 'kara bu'de idanuwanta dai same abu haka take gani.
_Hajjaty_ tun da haske ya gama gauraye parlourn ta kai dubanta ga ba'kin, idan har mai karatu ya san ru'du, to Hajjaty ta shiga wani irin hali na ru'du, waye take gani haka gabanta?
"Nooo that could not be her, ba ita bace" tayi reassuring kanta.
Ihun da Zahrah ta buga tana nufar 'daya daga cikin ba'kin tana ihu tana fa'din
"Mamah na!" Sai kuma ta 'kara hugging nata tightly kamar za a 'kwace ta daga gareta. Wannan ihu da Zahrah tayi shi ya dawo da Hajjaty daga duniyar tunani, tabbas ba gizo Madina take mata ba,'diyarta ce yau ta dawo gareta, nan hawaye suka fara wanke fuskar Hajjaty, Zahrah ce ta raba jikinta da na Mamah ba tare da hawayen fuskarta sun daina zuba ba.
"Mamah yau kam kin dawo..." bata ida fa'din abunda za ta ce ba taga Hajjaty rungume da Mamar dukkansu sai kuka suke. Babu wanda yayi 'ko'karin raba su haka aka bar su suna kukansu, they deserve to cry, kusan shekaru ashirin yanzu rabonsu da juna, dole kuwa su koka.
Nasreen, Nainah, Rumaysa, Zakiyya da yanzu sun fahimci cewa Mamah ce ta dawo yasa suma suka fara zubar da 'kwallar farin ciki tare da dawowa suka rungume Zahrah a tare. Inna, Asma'u da kuma Balkisu wa'danda su suka rako Mama su ma mamaki ya gama cika su musamman yadda suka ga Mama da Hajjaty na kukan farin ciki, hakan ya 'kara tabbatar musu da cewa ba 'karamar soyayya da sha'kuwa bace tsakaninsu.
Bayan an share mintuna goma da wasu sakannin ana kuka suka raba jikinsu koma na duban kowa. Hajjaty tana hawaye tace "Madina yau ke kika dawo? Farin cikin da na rasa tsawon shekarun nan yau ya dawo! Alhamdulillah" sai kuma ta sau'ka ta zube 'kasa tayi sujjada, itama Mamah sai ta bi bayan Hajjaty tayi sujjadar, sosai sauran mutanen suka bi su da murmushi da kuma tausayawa. Hajjaty da ta tashi ta dubi Hajjaty tace "Maza 'diyata tashi ki shiga ki yi wanka kafin a sanarwa Alhaji Baba da zuwanki ko?"
"Ke Zahrah kai ta bedroom 'dina,ba'kin kuma ki kai su naki kafin Laraba ta gyara musu wurin kwanansu" Kallon ba'kin tayi tace "Ku samu ku watsa ruwa sai ku ci abinci, Allah yasa dai ba da azumin kuka zo ba"
Murmushi Inna tayi tana kallo Hajjaty tana kuma yaba kirki da sau'kin kan Hajjaty tace "A'a ai da yake tafiyar mai tsayi ce shiyasa bamu 'dau azumin ba"
"Masha Allah, ku bi Zahrah ta 'karasa daku ko?" Hajjaty ta fa'da tana 'kwala kiran Laraba, ko da ta zo ta fa'da mata dalilin kiran sai ta wuce dining don taga me ya rage tunda ba a yi girki da su ba, an sha ruwa kuma in ta ce laraba tayi ita ma ta san ta gaji.
*MOMMAH*
Sosai wasu 'dabi'unta suka sauya sakamakon yadda rashin 'danta ya ta'ba ta, wannan hali na izza da kuma nuna isa duk babu shi, babu wannan rashin girmama manyan...haka dai duk ta koma ga ubangijinta, Sallah take tana addu'a babu dare ba rana ko Allah zai sa Daddy ya mayar da ita gidanta don nadama kam ta riga ta yi ta. A yau kuma ta kuduri aniyar tabbatar da maganar Hajjanta game da 'kawayenta wa'danda suka juya mata baya lokaci guda, kayan takaicin shine duk cikinsu babu waccetaga wulgwarta a rasuwar Yaya Sadauki, ta kuma 'kullace su za ta ji dalilinsu na 'kin ko da yi mata ta'aziyya ne.
Wannan kenan!
*React and Share please*
*For those who share, jazakumullahu khairan, Allah bar ni da ku masu 'kamshin humra.*
[1/23, 3:05 PM] Diamond Bhatool:
*🏡A BABBAN GIDA🏡*
*TAKUN ƘARSHE*
*©Diamond Bhatool*
*💎💍ELITE DIAMOND WRITERS💍💎*
_Where diamonds shine, words ignite_
_Wattpad: @diamond_bhatool_
_Arewabooks: @diamondbhatool3_
Please follow
*PAGE* 3️⃣3️⃣
﷽
Tabbas cikin wannan family babu wanda suke having good time fiye da Ammie, amma wai ace har a mata rasuwa ba za ta iya kira ko a waya ta mata ta'aziyya ba? Meye amfanin abotar. A matu'kar raunane ta wuce part 'dinta na da tana share 'kwalla tare da fatan Allah yasa wata rana tana da rabon sake rayuwa ciki. A haka har ta iso part 'din Ammie. Da sallama ta shiga ciki amma bakinta kusan biyar tukun Ammie ta amsa, sarai ta gane muryar Mommah amma ta share, sai da ta shafe kusan mintuna biyar tukun ta aiko Afifa ta shigo da ita.
A dadda'kile suka gaisa don kuwa nunawa tayi kamar ba ta san Mommah ba, tarin mamaki da al'ajabi suka cika Mommah duk takaicin kanta ya kama ta. A da idan ta zo wurinta takan ka'da yaran 'dakunan su tukun ta fuskanci Mommah, amma a yau sai ta ha'de girar sama da 'kasa ta 'daura 'kafarta 'daya kan 'daya. Gauron numfashi Mommah ta sau'ke kana ta fara magana.