Sashe 25
A Babban Gida Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cike da son gulma tace
“Kayan na waye” Zahrah ta amsa mata da “Na Nasreen ne Hajjaty tace ta bani”
“Na gode Allah” ta faɗa a ranta a zahiri kuma tace
“Hala ba ki da kaya da yawa ne har sai sun baki?” duk da maganar ta ba ta haushi amma sai ta dake don tana buƙatar ƙara fahimtar matar. Dariya tayi tana faɗin
“E wallahi Hajjaty ta ce dai za ta sa a ɗinko min amma na karɓo waɗannan ɗin.”
An zo wajen, Mami ta murmusa tana faɗin
“Kin ga ki ɗauke Ni kamar Maman ki Zahrah, kina da buƙatar abu ba za ki samu Ni ba?” shaye da mamaki Zahrah ke kallonta tana kuma tunawa in dai ba mantawa ta yi ba first contact ɗin ta da matar nan a part ɗin Mommah kallon tsanatake mata amma da yake mata iyayen kaidi ne ji abinda take faɗi.
Zahrah na da wayo duk da ƙarancin shekarunta amma kuma in ta sa abu gaba sai ta yi. Saboda haka ita ma sai ta sunkuyar da kai kasa tana faɗin.
“Na gode Mami, Allah ya ƙara girma.”
Murmushin cin nasara Mami tayi tana amsawa Zahrah da “Amin”
Daidai lokacin kuma suka iso part ɗin Hajjatyn. Daga nan kuma Mani tayi shiru bata ƙara cewa komai ba.
Ko da suka shiga direct bedroom ɗin ta ta wuce ta ajiye kayan sannan ta fito don ganin sauran scene ɗin Mami.
Ganin Yaya Sadauki bai dawo ba yasa ta koma kusan Mami ta Zauna fuskarta sake.
Sai da Mami ta juya taga babu kowa tukun tace
“Saura kuma naga ba kya zuwa wurin nawa.”
Kan ta ƙasa ta amsa da “Zan zo In Sha Allah Mami.”
Daga haka hirar ta tsaya saboda fitowar Hajjaty.
Nan suka gaisa cike da girmamawa kamar ba Mami ba, Hajjaty dai mamakin ta bai ɓuya ba ganin abun da bata saba ba. Zahrah kuwa ƙimis tayi ta ƙi ba su wuri, tana so a yi kai gabanta, she wants to feel that she's one of them.
*Afwan My esteem people, Kuna ta jiran update ban yi ba sakamakon ayyuka da suka sha kaina. I'm sorry ga shi nan na yi muku, a taimaka a taya Ni sharing tare da reacting.*
*Na gode da ƙaunarku gare Ni and I appreciated it, thank you so much, love you irin sosai ɗin nan.*
[12/31/2024, 2:31 PM] Diamond Bhatool: https://whatsapp.com/channel/0029VanUFkw5kg7G2ci16o2X
*🏡A BABBAN GIDA🏡*
*TAKUN ƘARSHE*
*©Diamond Bhatool*
*💎💍ELITE DIAMOND WRITERS💍💎*
_Where diamonds shine, words ignite_
_Wattpad: @diamond_bhatool_
_Arewabooks: @diamondbhatool3_
Please follow
*PAGE* 1️⃣9️⃣
﷽
“Hajjaty dama na yi dahuwar kaji ne kuma na ga kina so shi ne nace bari na kawo miki.”
Mami ta faɗa tana miƙewa tsaye tare da miƙewa Hajjaty food flask ɗin har da rusinawa kamar ta Allah.
“To madallah, sannu da ƙoƙari Baraka, Allah ya saka.”
Mami ta amsa da “Amin”.
Hajjaty na shirin ficewa Mami ta dakatar da ita “A'a Hajjaty wurin ki fa nazo.”
“To bari na kai abun nan kitchen.”
“Hajjaty ai ga Zahrah ki ba ta kawai, ke Zahrah karɓi ki kai, Babba ba ya aiki in da yaro kusa kin ji?”
Kai Zahrah ta ɗaga daga nan ta wuce kitchen kamar yadda Mami ta so. Tana ajiyewa ta juyo da sauri. Isowar ta ya yi daidai da lokacin da Hajjaty ta yi magana.
“Ban gane ba Baraka”
Ƙasa-ƙasa Mami ta Yi maganar ya yadda Zahrah ba ta iya jin komai. Kamar za ta fasa ihu haka ta koma Bedroom ɗin ta tana cije baki.
Shigowarsa kenan ya ci karo da fuskar Mami a tare da Hajjaty kuma, nan ya fara tambayar kansa ko me ya kawo ta? Har ya yi nufin juyawa wata zuciyar ta hana shi, gyaran murya ya yi wacce ta yi indicating presence na shi.
Kama wata tsohuwar munafuka Mami ta fara zaro idanuwa.
“A'a Aliyu ne?” ta faɗa tana washe baki. Ba tare da ya kalle ta ba yace “Good afternoon”
Bai jira amsawarta ba ya wuce zuwa Bedroom ɗin Hajjaty tunda abokin hirar tasa ba ya nan. Cikin ransa har yanzu ganin matar nan ya buge shi, ko wanne munafurcin take ƙullawa oho mata.
Da hararar Zahrah ta raka Mami da za ta fita daga nan kuma ta ƙarasa wurin Hajjaty tana faɗin
“Hajjaty dama Mamin su Ya Faruq tana shigowa nan? Ko gaisuwa ban taɓa ganin ta shigo ta miki ba”
Murmushi irin na manya Hajjaty ta yi kana ta ce
“Zahra'u ashe kema kin iya sa ido ban sani ba?,”
A shagwaɓe Zahrah tace
“Ba wani nan Hajjaty, ai dole na sa ido kan duk wani mai zuwa tun da dai noma I belonged to the place.”
“Za ki yi bayani ai, kin ga shiga ciki ki kira Yayanku ya zo ya yi lunch.”
“Yaya kuma? Ya shigo ne?”
“Ban sani ba, kar ki cika Ni da surutu, wuce ki je”
Daga haka Zahrah ta wuce tana tura baki wai Hajjaty ta nata faɗa, lokacin da ta shiga ba ta yi sallama ba ganin yana kwance kamar bacci yake, murmushi tayi tare da juyawa, taku ɗaya biyu ya dakatar da ita
Juyowa tayi tana kame kame
“Dama ba bacci kake ba Yaya? E Hajjaty ce tace ka fito ka ci abinci”
“Ok wait for me”
Tare suka yi lunch ɗin su daga nan ya mata sallar zai wuce office ɗinsa.
Tun bayan tafiyarsa Zahrah ke tariyowa abun da ya faru da ita a daren jiya, gani take kamar mafarki tayi amma tunawa da alwashin matar da ta kira kanta da Black-devil yasa ta ƙara tabbatarwa kanta a zahiri abun ya faru.
Tunaninta a yanzu ya ta'allaka ne ga don gano wacece wannan Black Devil Kuma meme ne ƙudirin ta ga ahalin nan, amma me? She need someone that'll support her.
A da ta yi tunanin Nasreen sai kuma ta fasa, haka ta yi ta ɗaura mutanen da ta
sani kan mizanin amma babu wadda ta ga ya cancanci wannan matsayi na sa rayuwarsa a kasada musamman da ta gano abun Black-devil na da alaƙa da Cultism.
“No!” ta faɗa a zahiri “I won't put any one's life in danger, I'll support myself ko da zan mutu sai na gano wace ce ita!”
“Amma ai a'a buƙatar wani ya san al'amarin nan, amma za a gaskata Ni kuwa? If yes waye zai yadda da Ni?”
Zuciyarta ta na ta amsa da “Yaya Sadauki”
Idanuwa ta zaro kamar dai tana gabansa ta maimaita sunansa da zuciyarta ta ambata. Cike da karfafa mata guiwa zuciyarta tace
“Yes Zahrah! Yaya Sadauki ne kaɗai zai iya yadda da ke ka ya zamo garkuwarki har ki cimma nasara a muradun ki, ina tabbatar miki he'll be there for you kamar yadda yake faɗa.”
Safe kanta ta yi jin shawarar da zuciyarta ke ba ta, kan ta ta gyaɗa alamar na'am sai kuma ta fesar da wata zazzafar iska.
“Feel free Zahrah! Calm and relax”
Nan ta ja numfashi ta fesar.
“Yes! Zan mishi magana” ta faɗa a bayyane. Ganin dai tunanin nan ba barinta zai yi na ga shi kuma ƙwaƙwalwarta na shirin fashewa saboda tunani yasa ta miƙe ta nufi parlour tare da kunna kallo, this is her first time to sit in the parlourn da niyyar kallo. Ko da ta kunna na ba fahimtar komai take ba coz her mind was taken away.
Da yamma Alhaji Baba ya dawo dama ya je wurin makoki mara abokinsa da ya rasu yau ɗin. Ko da ya huta ya a Hajjaty a ƙara yawan dinner without telling her the exact reason.
*BAUCHIN YAKUBU, ƘARAMAR HUKUMAR TORO*
Alhamdulillah za a ce, sauƙi ya fara samuwa ga matar da Inna ke kula da ita tare da ƴan jikokin ta. Yau ma kamar kullum zaune suke su uku, Asma'u, Inna sai kuma Maras lafiyar da ke bin su da ido suna hira, yanayin yadda yake kallon su zai tabbatar maka da cewa ba abinda take fahimta a ciki sai dai kuma suna sanya ta cikin hirar saboda ita a yadda Inna fahimci ciwon Amina (Sunan da suka laƙana mata.) Bai wuce gushewar tunanin ta da kuma hankali ba wanda ke da alaƙa da sihiri ko sammu.
Balkisu tace
“Inna har yau dai Malam Sufin bai zo ba, ina tausayawa Baba Amina wallahi, gaskiya Inna me zai hana mu ku ta can ɗin la'alla shi ba shi da lokacin zuwa, ko ya kika ce Asma'u?”
“E wallahi Inna, gobe mu shirya kawai muje can ɗin.” kalaman su sun taɓa zuciyar Inna, hakn ya sa ta yanke shawarar zuwa ganin Malam Sufin ɗin tare da Amina.
Washegari kuwa suka niƙi hanya sai Tafawaɓalewa don kai Amina wurin Mallam Sufi ko Allah zai sa a dace kamar kowa ita ma ta rayu cikin farin cikin.
*GRA, BAUCHI*
Cikin jerin gwanon gidajen da suka amsa sunan gida motar ta fito, bayan fitar ta free man ya rufe ƙatoton gare ɗin hakan ya sa ban samu damar kutsa kai cikin ba sai na bi motar don ganin ina za ta.
Unguwar Zango ta nufa kai tsaye, dai-dai wani gida wanda in ban manta ba gidan Idrisu ne!
Wane ne wannan kuma? Kafafuwansa ya ziro don fitowa, kamar wani basarake haka yake taku yayin da fuskar sa ke sanye da face mask Amma tsaro da yanayin jikinsa uwa uba kuma yanayin dressing ɗinsa zai tabbatar wa mai karatu da cikar izzarsa, da gani ka matashin ba zai wuce shekara 29-30 ba.
Takawa ya ci gaba da yi har isa daidai kofar gidan da ke sanye da kwaɗo. Tsaki ya ja tare da ƙara nazartar kwaɗon wadda alamun an jima da maƙala sa ta bayyana saboda yadda yake cijewa ga kuma tsatsar da ke jiki.
“Ya Allah!” ya furta yana dafe kansa tare da addu'ar Allah yasa dai ba tashi suka yi ba. Nan ya ga wani mutumin da sauri ya ƙarasa gunsa yana faɗin
“Am sannu da rana Malam.”
“Yauwa sannu ɗan saurayi”
“Baba don Allah tambaya nake” ɗan tsohon ya amsa da “Allah ya sa na sani.”
“Kayan na waye” Zahrah ta amsa mata da “Na Nasreen ne Hajjaty tace ta bani”
“Na gode Allah” ta faɗa a ranta a zahiri kuma tace
“Hala ba ki da kaya da yawa ne har sai sun baki?” duk da maganar ta ba ta haushi amma sai ta dake don tana buƙatar ƙara fahimtar matar. Dariya tayi tana faɗin
“E wallahi Hajjaty ta ce dai za ta sa a ɗinko min amma na karɓo waɗannan ɗin.”
An zo wajen, Mami ta murmusa tana faɗin
“Kin ga ki ɗauke Ni kamar Maman ki Zahrah, kina da buƙatar abu ba za ki samu Ni ba?” shaye da mamaki Zahrah ke kallonta tana kuma tunawa in dai ba mantawa ta yi ba first contact ɗin ta da matar nan a part ɗin Mommah kallon tsanatake mata amma da yake mata iyayen kaidi ne ji abinda take faɗi.
Zahrah na da wayo duk da ƙarancin shekarunta amma kuma in ta sa abu gaba sai ta yi. Saboda haka ita ma sai ta sunkuyar da kai kasa tana faɗin.
“Na gode Mami, Allah ya ƙara girma.”
Murmushin cin nasara Mami tayi tana amsawa Zahrah da “Amin”
Daidai lokacin kuma suka iso part ɗin Hajjatyn. Daga nan kuma Mani tayi shiru bata ƙara cewa komai ba.
Ko da suka shiga direct bedroom ɗin ta ta wuce ta ajiye kayan sannan ta fito don ganin sauran scene ɗin Mami.
Ganin Yaya Sadauki bai dawo ba yasa ta koma kusan Mami ta Zauna fuskarta sake.
Sai da Mami ta juya taga babu kowa tukun tace
“Saura kuma naga ba kya zuwa wurin nawa.”
Kan ta ƙasa ta amsa da “Zan zo In Sha Allah Mami.”
Daga haka hirar ta tsaya saboda fitowar Hajjaty.
Nan suka gaisa cike da girmamawa kamar ba Mami ba, Hajjaty dai mamakin ta bai ɓuya ba ganin abun da bata saba ba. Zahrah kuwa ƙimis tayi ta ƙi ba su wuri, tana so a yi kai gabanta, she wants to feel that she's one of them.
*Afwan My esteem people, Kuna ta jiran update ban yi ba sakamakon ayyuka da suka sha kaina. I'm sorry ga shi nan na yi muku, a taimaka a taya Ni sharing tare da reacting.*
*Na gode da ƙaunarku gare Ni and I appreciated it, thank you so much, love you irin sosai ɗin nan.*
[12/31/2024, 2:31 PM] Diamond Bhatool: https://whatsapp.com/channel/0029VanUFkw5kg7G2ci16o2X
*🏡A BABBAN GIDA🏡*
*TAKUN ƘARSHE*
*©Diamond Bhatool*
*💎💍ELITE DIAMOND WRITERS💍💎*
_Where diamonds shine, words ignite_
_Wattpad: @diamond_bhatool_
_Arewabooks: @diamondbhatool3_
Please follow
*PAGE* 1️⃣9️⃣
﷽
“Hajjaty dama na yi dahuwar kaji ne kuma na ga kina so shi ne nace bari na kawo miki.”
Mami ta faɗa tana miƙewa tsaye tare da miƙewa Hajjaty food flask ɗin har da rusinawa kamar ta Allah.
“To madallah, sannu da ƙoƙari Baraka, Allah ya saka.”
Mami ta amsa da “Amin”.
Hajjaty na shirin ficewa Mami ta dakatar da ita “A'a Hajjaty wurin ki fa nazo.”
“To bari na kai abun nan kitchen.”
“Hajjaty ai ga Zahrah ki ba ta kawai, ke Zahrah karɓi ki kai, Babba ba ya aiki in da yaro kusa kin ji?”
Kai Zahrah ta ɗaga daga nan ta wuce kitchen kamar yadda Mami ta so. Tana ajiyewa ta juyo da sauri. Isowar ta ya yi daidai da lokacin da Hajjaty ta yi magana.
“Ban gane ba Baraka”
Ƙasa-ƙasa Mami ta Yi maganar ya yadda Zahrah ba ta iya jin komai. Kamar za ta fasa ihu haka ta koma Bedroom ɗin ta tana cije baki.
Shigowarsa kenan ya ci karo da fuskar Mami a tare da Hajjaty kuma, nan ya fara tambayar kansa ko me ya kawo ta? Har ya yi nufin juyawa wata zuciyar ta hana shi, gyaran murya ya yi wacce ta yi indicating presence na shi.
Kama wata tsohuwar munafuka Mami ta fara zaro idanuwa.
“A'a Aliyu ne?” ta faɗa tana washe baki. Ba tare da ya kalle ta ba yace “Good afternoon”
Bai jira amsawarta ba ya wuce zuwa Bedroom ɗin Hajjaty tunda abokin hirar tasa ba ya nan. Cikin ransa har yanzu ganin matar nan ya buge shi, ko wanne munafurcin take ƙullawa oho mata.
Da hararar Zahrah ta raka Mami da za ta fita daga nan kuma ta ƙarasa wurin Hajjaty tana faɗin
“Hajjaty dama Mamin su Ya Faruq tana shigowa nan? Ko gaisuwa ban taɓa ganin ta shigo ta miki ba”
Murmushi irin na manya Hajjaty ta yi kana ta ce
“Zahra'u ashe kema kin iya sa ido ban sani ba?,”
A shagwaɓe Zahrah tace
“Ba wani nan Hajjaty, ai dole na sa ido kan duk wani mai zuwa tun da dai noma I belonged to the place.”
“Za ki yi bayani ai, kin ga shiga ciki ki kira Yayanku ya zo ya yi lunch.”
“Yaya kuma? Ya shigo ne?”
“Ban sani ba, kar ki cika Ni da surutu, wuce ki je”
Daga haka Zahrah ta wuce tana tura baki wai Hajjaty ta nata faɗa, lokacin da ta shiga ba ta yi sallama ba ganin yana kwance kamar bacci yake, murmushi tayi tare da juyawa, taku ɗaya biyu ya dakatar da ita
Juyowa tayi tana kame kame
“Dama ba bacci kake ba Yaya? E Hajjaty ce tace ka fito ka ci abinci”
“Ok wait for me”
Tare suka yi lunch ɗin su daga nan ya mata sallar zai wuce office ɗinsa.
Tun bayan tafiyarsa Zahrah ke tariyowa abun da ya faru da ita a daren jiya, gani take kamar mafarki tayi amma tunawa da alwashin matar da ta kira kanta da Black-devil yasa ta ƙara tabbatarwa kanta a zahiri abun ya faru.
Tunaninta a yanzu ya ta'allaka ne ga don gano wacece wannan Black Devil Kuma meme ne ƙudirin ta ga ahalin nan, amma me? She need someone that'll support her.
A da ta yi tunanin Nasreen sai kuma ta fasa, haka ta yi ta ɗaura mutanen da ta
sani kan mizanin amma babu wadda ta ga ya cancanci wannan matsayi na sa rayuwarsa a kasada musamman da ta gano abun Black-devil na da alaƙa da Cultism.
“No!” ta faɗa a zahiri “I won't put any one's life in danger, I'll support myself ko da zan mutu sai na gano wace ce ita!”
“Amma ai a'a buƙatar wani ya san al'amarin nan, amma za a gaskata Ni kuwa? If yes waye zai yadda da Ni?”
Zuciyarta ta na ta amsa da “Yaya Sadauki”
Idanuwa ta zaro kamar dai tana gabansa ta maimaita sunansa da zuciyarta ta ambata. Cike da karfafa mata guiwa zuciyarta tace
“Yes Zahrah! Yaya Sadauki ne kaɗai zai iya yadda da ke ka ya zamo garkuwarki har ki cimma nasara a muradun ki, ina tabbatar miki he'll be there for you kamar yadda yake faɗa.”
Safe kanta ta yi jin shawarar da zuciyarta ke ba ta, kan ta ta gyaɗa alamar na'am sai kuma ta fesar da wata zazzafar iska.
“Feel free Zahrah! Calm and relax”
Nan ta ja numfashi ta fesar.
“Yes! Zan mishi magana” ta faɗa a bayyane. Ganin dai tunanin nan ba barinta zai yi na ga shi kuma ƙwaƙwalwarta na shirin fashewa saboda tunani yasa ta miƙe ta nufi parlour tare da kunna kallo, this is her first time to sit in the parlourn da niyyar kallo. Ko da ta kunna na ba fahimtar komai take ba coz her mind was taken away.
Da yamma Alhaji Baba ya dawo dama ya je wurin makoki mara abokinsa da ya rasu yau ɗin. Ko da ya huta ya a Hajjaty a ƙara yawan dinner without telling her the exact reason.
*BAUCHIN YAKUBU, ƘARAMAR HUKUMAR TORO*
Alhamdulillah za a ce, sauƙi ya fara samuwa ga matar da Inna ke kula da ita tare da ƴan jikokin ta. Yau ma kamar kullum zaune suke su uku, Asma'u, Inna sai kuma Maras lafiyar da ke bin su da ido suna hira, yanayin yadda yake kallon su zai tabbatar maka da cewa ba abinda take fahimta a ciki sai dai kuma suna sanya ta cikin hirar saboda ita a yadda Inna fahimci ciwon Amina (Sunan da suka laƙana mata.) Bai wuce gushewar tunanin ta da kuma hankali ba wanda ke da alaƙa da sihiri ko sammu.
Balkisu tace
“Inna har yau dai Malam Sufin bai zo ba, ina tausayawa Baba Amina wallahi, gaskiya Inna me zai hana mu ku ta can ɗin la'alla shi ba shi da lokacin zuwa, ko ya kika ce Asma'u?”
“E wallahi Inna, gobe mu shirya kawai muje can ɗin.” kalaman su sun taɓa zuciyar Inna, hakn ya sa ta yanke shawarar zuwa ganin Malam Sufin ɗin tare da Amina.
Washegari kuwa suka niƙi hanya sai Tafawaɓalewa don kai Amina wurin Mallam Sufi ko Allah zai sa a dace kamar kowa ita ma ta rayu cikin farin cikin.
*GRA, BAUCHI*
Cikin jerin gwanon gidajen da suka amsa sunan gida motar ta fito, bayan fitar ta free man ya rufe ƙatoton gare ɗin hakan ya sa ban samu damar kutsa kai cikin ba sai na bi motar don ganin ina za ta.
Unguwar Zango ta nufa kai tsaye, dai-dai wani gida wanda in ban manta ba gidan Idrisu ne!
Wane ne wannan kuma? Kafafuwansa ya ziro don fitowa, kamar wani basarake haka yake taku yayin da fuskar sa ke sanye da face mask Amma tsaro da yanayin jikinsa uwa uba kuma yanayin dressing ɗinsa zai tabbatar wa mai karatu da cikar izzarsa, da gani ka matashin ba zai wuce shekara 29-30 ba.
Takawa ya ci gaba da yi har isa daidai kofar gidan da ke sanye da kwaɗo. Tsaki ya ja tare da ƙara nazartar kwaɗon wadda alamun an jima da maƙala sa ta bayyana saboda yadda yake cijewa ga kuma tsatsar da ke jiki.
“Ya Allah!” ya furta yana dafe kansa tare da addu'ar Allah yasa dai ba tashi suka yi ba. Nan ya ga wani mutumin da sauri ya ƙarasa gunsa yana faɗin
“Am sannu da rana Malam.”
“Yauwa sannu ɗan saurayi”
“Baba don Allah tambaya nake” ɗan tsohon ya amsa da “Allah ya sa na sani.”