Sashe 32
A Babban Gida Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Suna Isa gate ɗin garden ɗin Nasreen ta ja ta tsaya, juyowar da Zahrah ta yi ta ga babu Nasreen, a ɗan fusace ta dawo baya tace “Malama ya za ki tsaya?”
Ƙasa-ƙasa take maganar gudun kada ya jiyo tace “Kin ga Zahrah ki rufa min asiri ki je ki kai masa, kin ga duk cikinsu Ni kaɗai na rako ki” ta idasa cikin sigar ban tausayi. Zahrah ba ta ce komai ba ta ƙarasa ciki, daidai wani ɗan building flat ta gefe wanda bai fiye girma ba ta tsaya, door bell ta Danna, few seconds sai ga Yaya Sadauki ya fito, murmushi Zahrah tayi tace
“Yaya ga shi” sannan ta miƙa masa.
“Thank You, You can go....” ko rufe baki bai yi ba two of his friends da suka biyo bayansa don ganin amarya coz su a tunaninsu amaryar ce. Bangaje shi ɗaya yayi ɗayan kuma ya ja Yaya Sadaukin baya saying “Ya! Mallam ban wuri na ga amaryar”
Wata muguwar harara ya Banka masa sannan ya aika guntuwar wa Zahrah, tuni ta yi disappearing a wurin.
Ganin ta tafi yasa ya dawo kan su rai ɓace yace “Why Are You people behaving unnaturally? Eh?”
Dariya suka saka suna kallonsa ganin yadda ya wani haɗe girar sama da ƙasa.
Ɗaya daga cikinsu ne ya kalli ɗan'uwansa yace
“Prince ka ga yadda Man yake wani huci don Allah kamar wani mayunwancin zaki, Allah ya ba ka haƙuri, ka san ba lallai muna nan za a kai ta ba shiyasa.”
Wanda aka kira da Prince murmushi kawai yayi yace
“Rabu da shi kawai, wallahi don dai an riga an kusa ɗaurawa da ba abun da zai hana nima na hau layin manema Detective”
Dukan wasa Detective Hamad ya Kai wa Prince yana faɗin
“Ba ka da kirki Prince, to da sanin Allah, shiyasa bai yi wa jaki ƙaho ba, Ni dai Man I'm sorry!” ya faɗa yana haɗe hannu biyu, ɗaga idon da yayi yaga babu Ya Sadauki ba alamun sa, tuni ya yi ciki saboda yadda ya ji su Prince na yaba Lilyn sa.
Ko da suka shigo ciki haka ƙememe yace ba zai ba su abincin ba, da ƙyar Yaya Khalil ya tausasa shi har yayi hakuri ya basu, suna gama ci aka hau hira wanda shi ba wani magana yake ba, iyaka yayi murmushi ne ko kuma ya kaɗa kai.
*A GURGUJE*
Ranar Laraba aka yi family and friends day, abun so ma sha Allah, Aunty Mabruka an Sha kyau kamar ka sace ka gudu. An ci an sha kuma an zubar da Naira, wanda bai je wannan biki ba ya yi missing gaskiya. Can na hango su Maman Tajuddeen riƙe da Taj ɗin ta sai muzurai take alamun dai ita ma kishi take da Aunty Mabruka, ga su nan dai jama'a cikin shiga ta alfarma kamar ba a san da talauci ba.
Team Zahrah ma dai cire kishi aka yi gefe aka gwangwaje, komai dai ya yi kyau kamar yadda aka tsara.
Ana daf da kammala shagalin kwatsam sai ga wata mata fuskarta rufe da baƙin ƙyalle, ta cikin mutane ta kutsa har ta kai ta wurin da aka tanada domin amarya. Ta kuwa ci Sa'a that time Babu kowa a wurin, bridesmaids duk sun ja gefe nasu uzururrukan.
“Ke!” ta ƙira sunan amaryar a hankali, kamar daga sama Aunty Mabruka taji ana kiran sunanta, tana juyawa taci karo da matar da ba za ta iya tantance wace ce ba, wata ƴar ƙaramar wuƙa ta zaro wacce ke zuba sheƙi ta nuna mata sai kuma ta mayar da ita.
“Kin ga wannan wuƙar, ina miji rantsuwa da wanda ya yi ki, In kika bari aka ɗaura auren ki da wannan mutumin, ba shakka kin kawo kan ki ne ga halaka, za ki fuskanci uƙubobi iri-iri, ke da kan ki za ki yi da-na-sanin bari a yi auren a lokacin da ba zan bar ki ba sai dai gawarki, In kin ƙi ji kuma, ba kya ƙi gani ba.”
Daga haka matar ta fara shigewa kafin kace me? Babu alamar ta babu alamar ta taɓa wanzuwa a wurin. Hankalin Aunty Mabruka ne ya tashi kamar za ta yi hauka, tuni idanuwanta suka fara zubar da ƙwalla, Thank God lokacin an kammala shagalin, ai kuwa ta samu ta faki idanuwan jama'a ta fice daga hall ɗin don samar wa kanta mafita.
Ba tsaya ba ta fara takawa da sauri da sauri kasancewar babu nisa daga hall ɗin zuwa apartment ɗin su tana tafe tana waiwayawa kamar munafuka, bata ji horn ɗin da yake mata ba har ya kusa buge ta Allah ya bashi ikon taka brake, a fusace ya fito don ganin waye sai dai abun da ya gani Yasa ya ɗan zaro idanuwansa waje. Da sauri ya Sadauki ya isa gareta tare da ɗaga ta tsaye don lokacin ta riga ta saddaƙar shikenan ta mutu.
“From where are you Mabruka?, Ina za ki je da gudu haka?”
Bata ce masa uffan ba sai ma lafewa da tayi a jikinsa tana sakin wani irin kuka mai raunana zuciyar mai sauraron sa, bai yi ƙoƙarin janye ta daga jikinsa ba kuma bai hana ta kukan ba tsawon mintuna biyar kafin tayi shiru tana sauƙe ajiyar zuciya. Hannunta ya ja bai tsaya ko ina ba sai front seat, ya bude mata ta shiga shima ya zagaya ya shiga, bai tada motar ba sai da ya dube ta tsawon wasu sakanni yana nazartar ta, can kuma ya kau da kansa gefe yace
“Daga ina kike?”
Cikin rawar murya tace “Daga can nake..ehm hall ɗin da ake event ɗin.”
Kansa gefe yace “An gama ne?”
“A'a” ta bashi amsa tana jijjiga kanta
“Then why are you out, baki son bikin ne?”
Shiru tayi ba ta ce masa komai ba.
“Ki bani amsa”
Kai ta jijjiga masa alamar a'a
A ɗan hasale yace “Ba a min magana da ka”
Da sauri tace “I'm sorry”
Shiru yayi ba kuma shi da alamar tayar da motar ga shi maghrib ta kusa
“Then why are you out?”
Kuka ta fashe masa da shi tana jijjiga kai, bai san lokacin da ya janyo ta jikinsa yana tapping bayanta ba har ta Yi shiru tana sauƙe ajiyar zuciya akai akai.
Gently in his melodious voice yace
“Tell me, Ko Mommah ta je wurin ne?”
“A'a” ta bashi amsa
“Ok tell me why are so frightened kika fito ba ki jira an mayar da ke ba, sai kace ba amarya ba.”
Kokawar da take da zuciyarta akan ta sanar da shi ko akasin haka ta kawo karshe. Zuciyar ta ta bata goyon baya ɗari bisa ɗari kan ta faɗa masa, atleast he'll know something to do, probably he might confront the issue and resolve it, ko kuma a fasa auren gaba-daya.”
Nan ta buɗe baki ta sanar da shi abunda ya faru. Ɓacin ransa ya ɓoye don ya ma samfo waye ya aikata hakan, ba kowa bace face Mommah, kuma ko za ta mutu auren nan babu fashi.
Lallashin ta yayi cikin kalmomi marasa yawa, and he encouraged her to be brave, nothing bad will happen in Sha Allah. Daga haka ya ja motar, daidai bakin flat ɗin su yayi parking, sai da ya tabbatar ya gana shigar ta ya sauke wani gauron numfashi sannan ya ja motar.
Can wurin event lokaci ɗaya aka nemi amarya aka rasa, duk neman duniyar nan an yi ba ta wurin, hakan yasa aka ƙira gida aka sanar nan ake ce musu ai ta koma ba ta jin daɗi ne. Nan aka fara jigilar mayar da kowa gida.
*Mommah*
Cikin kwana ɗayan da ta yi a gidansu ta galabaita, ta saba kwana kan makeken gado ta juya yadda taso wai yau ita ce kan gayar tabarma, a can gidan mijinta ta kan manta da wata halitta ta sauro amma daren nan haka sauro suka hana ta rintsawa, da ta juya nan sai wannan ya mall mata. Da safe fuskar nan Tata ta kumbura suntum saboda rashin samun bacci, ko ina na jikinta ban da ciwo babu abun da yake yi, maimakon ta risina sai ma ƙara zafi da tayi, alwashin ta sha ma kanta tabbas aka yi auren nan sai ta hana su zaman auren nan.
Babbar magana, su Mommah an saba da samun ruwa ko yaushe sai da ta shiga wanka ta tarar ashe babu ruwa ko ɗiso, haka ta fito ranta ɓace, Hajja ta tarar a parlourn amma ko kallo ba ta samu ba, gaida ta tayi ta amsa kamar dai jiya daga haka ta ɗauke kanta. Cikin ta ne ya ba da sautin ƙulululuu, nan ta tuna rabin ta da abinci tun jiya da safe. Kamar za ta yi kuka ta ƙira sunan Hajja.
“Hajja” kallo ɗaya Hajja ta mata ta ɗauke kanta
“Ina abinci na?”
Wani kallo da Hajja ta aika mata sai da ƴaƴan hanjin cikinta suka motsa
“Dama nauyin ciyar da ke a wuya na yake Sughrah?, Ba dai ke kin isa da kan ki ba? Sai ki yi zaman gidan idan daɗi ne da shi aka ce miki, ga fili ga mai doki.”
Daga haka Hajja ta miƙe ta bar parlourn ranta na ƙuna.
Baki sake Mommah ke kallon ta, “ko meye na ɗaukan zafin rai?” Ta tambayi kanta. Daga haka ta kyaɓe baki ta wuce zuwa ɓangaren Yaya Kabir, bayan sun gaisa da Aunty Rahina sai ta rasa mai zata ce mata, ga shi yunwa take ji ga kuma izza ta hana ta faɗin abun da ya kawo ta, sarai ita ma Aunty Rahina ta fahimta amma sai ta kafse ta ci gaba da wankin kayan yaran da take yi.
“Don Allah nace ba” Mommah ta faɗa ranta na ƙuna tare da kawar da kanta gefe.
“Idan akwai abinci ki bani”
“Babu” shi ne kaɗai amsar da ta samu daga gareta. Daga haka Aunty Rahina ta ci gaba da wankin ta. Ran Mommah ina ya yi dubu to yau ya ɓaci, haka ta fice a hasale, ta shiga ƙofar Yaya Sa'ad, gwanda Aunty Rahina ta amsa mata, Aunty Maryama ko kallonta bata yi ba har ya gaji da tsayuwa ta fito don kanta.
Ƙasa-ƙasa take maganar gudun kada ya jiyo tace “Kin ga Zahrah ki rufa min asiri ki je ki kai masa, kin ga duk cikinsu Ni kaɗai na rako ki” ta idasa cikin sigar ban tausayi. Zahrah ba ta ce komai ba ta ƙarasa ciki, daidai wani ɗan building flat ta gefe wanda bai fiye girma ba ta tsaya, door bell ta Danna, few seconds sai ga Yaya Sadauki ya fito, murmushi Zahrah tayi tace
“Yaya ga shi” sannan ta miƙa masa.
“Thank You, You can go....” ko rufe baki bai yi ba two of his friends da suka biyo bayansa don ganin amarya coz su a tunaninsu amaryar ce. Bangaje shi ɗaya yayi ɗayan kuma ya ja Yaya Sadaukin baya saying “Ya! Mallam ban wuri na ga amaryar”
Wata muguwar harara ya Banka masa sannan ya aika guntuwar wa Zahrah, tuni ta yi disappearing a wurin.
Ganin ta tafi yasa ya dawo kan su rai ɓace yace “Why Are You people behaving unnaturally? Eh?”
Dariya suka saka suna kallonsa ganin yadda ya wani haɗe girar sama da ƙasa.
Ɗaya daga cikinsu ne ya kalli ɗan'uwansa yace
“Prince ka ga yadda Man yake wani huci don Allah kamar wani mayunwancin zaki, Allah ya ba ka haƙuri, ka san ba lallai muna nan za a kai ta ba shiyasa.”
Wanda aka kira da Prince murmushi kawai yayi yace
“Rabu da shi kawai, wallahi don dai an riga an kusa ɗaurawa da ba abun da zai hana nima na hau layin manema Detective”
Dukan wasa Detective Hamad ya Kai wa Prince yana faɗin
“Ba ka da kirki Prince, to da sanin Allah, shiyasa bai yi wa jaki ƙaho ba, Ni dai Man I'm sorry!” ya faɗa yana haɗe hannu biyu, ɗaga idon da yayi yaga babu Ya Sadauki ba alamun sa, tuni ya yi ciki saboda yadda ya ji su Prince na yaba Lilyn sa.
Ko da suka shigo ciki haka ƙememe yace ba zai ba su abincin ba, da ƙyar Yaya Khalil ya tausasa shi har yayi hakuri ya basu, suna gama ci aka hau hira wanda shi ba wani magana yake ba, iyaka yayi murmushi ne ko kuma ya kaɗa kai.
*A GURGUJE*
Ranar Laraba aka yi family and friends day, abun so ma sha Allah, Aunty Mabruka an Sha kyau kamar ka sace ka gudu. An ci an sha kuma an zubar da Naira, wanda bai je wannan biki ba ya yi missing gaskiya. Can na hango su Maman Tajuddeen riƙe da Taj ɗin ta sai muzurai take alamun dai ita ma kishi take da Aunty Mabruka, ga su nan dai jama'a cikin shiga ta alfarma kamar ba a san da talauci ba.
Team Zahrah ma dai cire kishi aka yi gefe aka gwangwaje, komai dai ya yi kyau kamar yadda aka tsara.
Ana daf da kammala shagalin kwatsam sai ga wata mata fuskarta rufe da baƙin ƙyalle, ta cikin mutane ta kutsa har ta kai ta wurin da aka tanada domin amarya. Ta kuwa ci Sa'a that time Babu kowa a wurin, bridesmaids duk sun ja gefe nasu uzururrukan.
“Ke!” ta ƙira sunan amaryar a hankali, kamar daga sama Aunty Mabruka taji ana kiran sunanta, tana juyawa taci karo da matar da ba za ta iya tantance wace ce ba, wata ƴar ƙaramar wuƙa ta zaro wacce ke zuba sheƙi ta nuna mata sai kuma ta mayar da ita.
“Kin ga wannan wuƙar, ina miji rantsuwa da wanda ya yi ki, In kika bari aka ɗaura auren ki da wannan mutumin, ba shakka kin kawo kan ki ne ga halaka, za ki fuskanci uƙubobi iri-iri, ke da kan ki za ki yi da-na-sanin bari a yi auren a lokacin da ba zan bar ki ba sai dai gawarki, In kin ƙi ji kuma, ba kya ƙi gani ba.”
Daga haka matar ta fara shigewa kafin kace me? Babu alamar ta babu alamar ta taɓa wanzuwa a wurin. Hankalin Aunty Mabruka ne ya tashi kamar za ta yi hauka, tuni idanuwanta suka fara zubar da ƙwalla, Thank God lokacin an kammala shagalin, ai kuwa ta samu ta faki idanuwan jama'a ta fice daga hall ɗin don samar wa kanta mafita.
Ba tsaya ba ta fara takawa da sauri da sauri kasancewar babu nisa daga hall ɗin zuwa apartment ɗin su tana tafe tana waiwayawa kamar munafuka, bata ji horn ɗin da yake mata ba har ya kusa buge ta Allah ya bashi ikon taka brake, a fusace ya fito don ganin waye sai dai abun da ya gani Yasa ya ɗan zaro idanuwansa waje. Da sauri ya Sadauki ya isa gareta tare da ɗaga ta tsaye don lokacin ta riga ta saddaƙar shikenan ta mutu.
“From where are you Mabruka?, Ina za ki je da gudu haka?”
Bata ce masa uffan ba sai ma lafewa da tayi a jikinsa tana sakin wani irin kuka mai raunana zuciyar mai sauraron sa, bai yi ƙoƙarin janye ta daga jikinsa ba kuma bai hana ta kukan ba tsawon mintuna biyar kafin tayi shiru tana sauƙe ajiyar zuciya. Hannunta ya ja bai tsaya ko ina ba sai front seat, ya bude mata ta shiga shima ya zagaya ya shiga, bai tada motar ba sai da ya dube ta tsawon wasu sakanni yana nazartar ta, can kuma ya kau da kansa gefe yace
“Daga ina kike?”
Cikin rawar murya tace “Daga can nake..ehm hall ɗin da ake event ɗin.”
Kansa gefe yace “An gama ne?”
“A'a” ta bashi amsa tana jijjiga kanta
“Then why are you out, baki son bikin ne?”
Shiru tayi ba ta ce masa komai ba.
“Ki bani amsa”
Kai ta jijjiga masa alamar a'a
A ɗan hasale yace “Ba a min magana da ka”
Da sauri tace “I'm sorry”
Shiru yayi ba kuma shi da alamar tayar da motar ga shi maghrib ta kusa
“Then why are you out?”
Kuka ta fashe masa da shi tana jijjiga kai, bai san lokacin da ya janyo ta jikinsa yana tapping bayanta ba har ta Yi shiru tana sauƙe ajiyar zuciya akai akai.
Gently in his melodious voice yace
“Tell me, Ko Mommah ta je wurin ne?”
“A'a” ta bashi amsa
“Ok tell me why are so frightened kika fito ba ki jira an mayar da ke ba, sai kace ba amarya ba.”
Kokawar da take da zuciyarta akan ta sanar da shi ko akasin haka ta kawo karshe. Zuciyar ta ta bata goyon baya ɗari bisa ɗari kan ta faɗa masa, atleast he'll know something to do, probably he might confront the issue and resolve it, ko kuma a fasa auren gaba-daya.”
Nan ta buɗe baki ta sanar da shi abunda ya faru. Ɓacin ransa ya ɓoye don ya ma samfo waye ya aikata hakan, ba kowa bace face Mommah, kuma ko za ta mutu auren nan babu fashi.
Lallashin ta yayi cikin kalmomi marasa yawa, and he encouraged her to be brave, nothing bad will happen in Sha Allah. Daga haka ya ja motar, daidai bakin flat ɗin su yayi parking, sai da ya tabbatar ya gana shigar ta ya sauke wani gauron numfashi sannan ya ja motar.
Can wurin event lokaci ɗaya aka nemi amarya aka rasa, duk neman duniyar nan an yi ba ta wurin, hakan yasa aka ƙira gida aka sanar nan ake ce musu ai ta koma ba ta jin daɗi ne. Nan aka fara jigilar mayar da kowa gida.
*Mommah*
Cikin kwana ɗayan da ta yi a gidansu ta galabaita, ta saba kwana kan makeken gado ta juya yadda taso wai yau ita ce kan gayar tabarma, a can gidan mijinta ta kan manta da wata halitta ta sauro amma daren nan haka sauro suka hana ta rintsawa, da ta juya nan sai wannan ya mall mata. Da safe fuskar nan Tata ta kumbura suntum saboda rashin samun bacci, ko ina na jikinta ban da ciwo babu abun da yake yi, maimakon ta risina sai ma ƙara zafi da tayi, alwashin ta sha ma kanta tabbas aka yi auren nan sai ta hana su zaman auren nan.
Babbar magana, su Mommah an saba da samun ruwa ko yaushe sai da ta shiga wanka ta tarar ashe babu ruwa ko ɗiso, haka ta fito ranta ɓace, Hajja ta tarar a parlourn amma ko kallo ba ta samu ba, gaida ta tayi ta amsa kamar dai jiya daga haka ta ɗauke kanta. Cikin ta ne ya ba da sautin ƙulululuu, nan ta tuna rabin ta da abinci tun jiya da safe. Kamar za ta yi kuka ta ƙira sunan Hajja.
“Hajja” kallo ɗaya Hajja ta mata ta ɗauke kanta
“Ina abinci na?”
Wani kallo da Hajja ta aika mata sai da ƴaƴan hanjin cikinta suka motsa
“Dama nauyin ciyar da ke a wuya na yake Sughrah?, Ba dai ke kin isa da kan ki ba? Sai ki yi zaman gidan idan daɗi ne da shi aka ce miki, ga fili ga mai doki.”
Daga haka Hajja ta miƙe ta bar parlourn ranta na ƙuna.
Baki sake Mommah ke kallon ta, “ko meye na ɗaukan zafin rai?” Ta tambayi kanta. Daga haka ta kyaɓe baki ta wuce zuwa ɓangaren Yaya Kabir, bayan sun gaisa da Aunty Rahina sai ta rasa mai zata ce mata, ga shi yunwa take ji ga kuma izza ta hana ta faɗin abun da ya kawo ta, sarai ita ma Aunty Rahina ta fahimta amma sai ta kafse ta ci gaba da wankin kayan yaran da take yi.
“Don Allah nace ba” Mommah ta faɗa ranta na ƙuna tare da kawar da kanta gefe.
“Idan akwai abinci ki bani”
“Babu” shi ne kaɗai amsar da ta samu daga gareta. Daga haka Aunty Rahina ta ci gaba da wankin ta. Ran Mommah ina ya yi dubu to yau ya ɓaci, haka ta fice a hasale, ta shiga ƙofar Yaya Sa'ad, gwanda Aunty Rahina ta amsa mata, Aunty Maryama ko kallonta bata yi ba har ya gaji da tsayuwa ta fito don kanta.