Sashe 46
A Babban Gida Part 1 Complete Hausa Novel · about 2 min read
Sai da aka idar da sallar maghrib Alhaji Baba yakawo musu zancen dawowar Mamah, a lokacin dukkansu suka 'dunguma wai za su je su ganta sai kace wasu yariya, murmushi irin na manya Alhaji Baba yayi yace
"Kul! Ban ji ba ban yadda ba, kwa bari gari ya waye dai ko?" Kansu 'kasa suna murmushi suka ce to shikenan.
Da misalin 'karfe 7:00am sai ga Daddy ya zo, idan baku mance ba Daddy na matu'kar 'kaunar 'yar'uwar tasa sai dai zuwansa har su Hajjaty babu wanda ya tashi, hakan yasa ya wuce office nasa ba tare da sun ha'dun ba, sosai yake jin da'di da bayyanarta, kuma ta bayyana a lokacin da ake bu'katarta ne, suna cikin jimamin rashin Yaya Sadauki kuma sai ga ta, Allah ya 'dauke ya kawo kenan.
Haka sauran 'yan'uwan nata duk suka fice wuraren ayyukansu ba tare da sun sa ta a idanuwansu ba. Ba su kuwa suka tashi ba sai wuraren 10am coz babu laifi sun sha gajiyar hanya, abuja to bauchi a cikin mota ai dole a jijjiga. Bayan an gaisa da juna, Zahrah ta ja Asma'u da Balkisu cikin sauran 'yan'uwanta su ma suka ja gefe suna hira, tun ba sa magana har suka saki baki suka fara.
Su Mamah ma hirarsu suke yi da Inna da kuma Hajjaty, Yaya Khalil ne ya shigo gaisuwar safe, yana 'karasowayaci karo da Mamah, shaye da mamaki yake kallonta, can dai yace "Ina yini Mommy Madina"
"Lafiya lau" ta amsa masa fuska sake.
Hajjaty ce ta 'dan ha'de rai tace
"Ban gane ba Halilu, yau saboda ka ga uwarka shine ka manta da zamana har sai da ka gaishe ta? A hakan ma mu da alama ba za ka gaishe mu ba"
kunya ce ta kama Yaya Khalil yace
"Haba Hajjaty kya tsaya dai in gama da sabon hannu, ke kam ai....."
Hannun da ta mi'ko kamar za ta kwa'de shi ne yasa yaja baya yana dariya, gaba'dayansu suka saki dariyar suma, gaishe da Hajjaty da Inna yayi kana ya wuce corridorn da zai sada shi da 'bangaren tsoho mai ran 'karfe. Bayan sun gaisa da Alhaji Baba haka ya sako shi gaba wai sai ya fito sun yi hira da 'yarsa don ga can Hajjaty ta ma'kale ta kamar ita ka'dai ta haife ta, sosai Alhaji ya dara jin shiriritar Yaya Khalil, daga nan suka fito tare, Yaya Khalil yayi wa Mamah Sallama daga nan ya wuce office shima.
*React and Share Lillah, for those who share, Alkhairin ubangiji ya kai ku.*
"Kul! Ban ji ba ban yadda ba, kwa bari gari ya waye dai ko?" Kansu 'kasa suna murmushi suka ce to shikenan.
Da misalin 'karfe 7:00am sai ga Daddy ya zo, idan baku mance ba Daddy na matu'kar 'kaunar 'yar'uwar tasa sai dai zuwansa har su Hajjaty babu wanda ya tashi, hakan yasa ya wuce office nasa ba tare da sun ha'dun ba, sosai yake jin da'di da bayyanarta, kuma ta bayyana a lokacin da ake bu'katarta ne, suna cikin jimamin rashin Yaya Sadauki kuma sai ga ta, Allah ya 'dauke ya kawo kenan.
Haka sauran 'yan'uwan nata duk suka fice wuraren ayyukansu ba tare da sun sa ta a idanuwansu ba. Ba su kuwa suka tashi ba sai wuraren 10am coz babu laifi sun sha gajiyar hanya, abuja to bauchi a cikin mota ai dole a jijjiga. Bayan an gaisa da juna, Zahrah ta ja Asma'u da Balkisu cikin sauran 'yan'uwanta su ma suka ja gefe suna hira, tun ba sa magana har suka saki baki suka fara.
Su Mamah ma hirarsu suke yi da Inna da kuma Hajjaty, Yaya Khalil ne ya shigo gaisuwar safe, yana 'karasowayaci karo da Mamah, shaye da mamaki yake kallonta, can dai yace "Ina yini Mommy Madina"
"Lafiya lau" ta amsa masa fuska sake.
Hajjaty ce ta 'dan ha'de rai tace
"Ban gane ba Halilu, yau saboda ka ga uwarka shine ka manta da zamana har sai da ka gaishe ta? A hakan ma mu da alama ba za ka gaishe mu ba"
kunya ce ta kama Yaya Khalil yace
"Haba Hajjaty kya tsaya dai in gama da sabon hannu, ke kam ai....."
Hannun da ta mi'ko kamar za ta kwa'de shi ne yasa yaja baya yana dariya, gaba'dayansu suka saki dariyar suma, gaishe da Hajjaty da Inna yayi kana ya wuce corridorn da zai sada shi da 'bangaren tsoho mai ran 'karfe. Bayan sun gaisa da Alhaji Baba haka ya sako shi gaba wai sai ya fito sun yi hira da 'yarsa don ga can Hajjaty ta ma'kale ta kamar ita ka'dai ta haife ta, sosai Alhaji ya dara jin shiriritar Yaya Khalil, daga nan suka fito tare, Yaya Khalil yayi wa Mamah Sallama daga nan ya wuce office shima.
*React and Share Lillah, for those who share, Alkhairin ubangiji ya kai ku.*