Sashe 42
Sultan Merah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ranar da kyar barci ya d'auke ta ga tunanin halin sultan ga kawaicin yasmeen da bata gidan.
Washe gari suna kitchen tare da Afiya kamar ko yaushe, ta fito daga kitchen d'auke da kaya xata nufi dinning tajiyo qamshin turaren sa, muryar sa taji yana fad'in ki jira ni yanxu xan iso, ya tsinke wayar yana kallon hidaya itama shi take kallo kamar baxata gaida shi ba sai kuma ta gaida shi tana d'auke kanta, bai amsa ba yayi shigewar sa kitchen ta bisa da kallo tana fad'in a fili kamar na kwarai bayan baa san abinda yake aikatawa a boye ba, sarai ya ji ta kuma ya san dashi take sai ya juya ya d'an dube ta yana d'auke kansa bayan ya qarasa ciki,
Mami xan fita yanxu amira ta kirani mota ta tsaya masu a hanya xanje na duba na gani.
Tace shi fu'ad fa?
Yace kin manta baya gari yaje auren abokin sa Kaduna.
Tace haka ne amma ka tsaya kayi breakfast tukunna tunda an kammala, ya fito yana fad'in jirana take fa a hanya idan na dawo xanci tunda ba jimawa xan yi ba, yasa kai ya bar falon.
Wacece ke jiran sa a hanya ta tambayi kanta tana bin sa da kallo har ya bar falon, haka kawai taji sam xuciyar ta ba dad'i wanda ta rasa dalilin haka, falon ta bari taje tayi wanka idanun ta akan clock fiye da minti talatin bai dawo ba, wurin wacece yaje haka?
Fitar mera gidan bada jimawa ba ya dawo, suna falo xaune su biyu, ya xauna yana fad'in mami kin ganni sai yanxu duk na gaji Haneefa tace a gaida ki.
Tace ina kuma ka had'u da ita yaushe ta dawo qasar,
Ya tashi yana fad'in can na same ta tare da su amira,
Tace breakfast d'in fa?
Yace am ok naci a gurin mummy, yayi shigewar sa.
Sam ta kasa sukuni wacece hanifa ma da tun d'axu yake gurin ta sai yanxu yake dawowa.
Kamar daga sama Afiya taji tana tambayar mamee wacece hanifa?
Daughter wata friend d'ita ce kusan sa'annin juna kuke ma amma xata girme ku keda yasmeen kad'an ba anan suke xaune ba ita da iyayen ta suna Cameron,
Hidaya ta jinjina kai tana tabe baki Afiya kuwa kallon ta take ganin damuwa a fuskarta ko kishin sultan take, murmushi tayi tana qara kallon ta tana cewa ke hidaya haka kika ga anayi miji ya dawo baxaki masa sannu da xuwa ba kuma ki ta xama batare da kin bisa kin masa ya gajiya ba, haka kika ga ina yi da nawa mijin.
Hidaya tayi shiru kuma batada niyar tashi, Afiya ta tashi tana fad'in sai ki ta xama kina barin mijin ki cikin kadaice a hakan xai kyallo wata dake nuna masa kulawa ya fara son ta har kiji anan maganar aure Ma kina xaune sake da baki.
Haka kawai taji hankalin ta is tashi karfa mgnr ta xama gaske, ta turo baki tana barin falon kamar baxata je d'akin na sa ba saw kuma ta shiga da sallama ciki ciki kamar bata so.
Jin muryarta ya saka shi juyowa daga wayar da yake, yana kammalawa kallo d'aya yayi mata ya d'auke kansa daga gare ta, kamar bata so tace barka da dawowa, bai amsa ba amma ya kafe ta da idanunta, kamar baxai yi magana ba sai kuma ya matso daf da ita yana fad'in har yanxu xuciyata ta daina xargin cewa tun farko ba sona kike ba, ta d'ago tana kallon sa sai kuma ta juyar da kanta gefe tana yatsina fuska batare da tayi magana ba, shima tabe bakin sa yayi ya juya abinsa, ta fice da sauri.
Daren yau ma ya kasance su biyu kad'ai ne a gidan su yasmeen sun qi dawowa, ta gaji da xaman kadaici sai take jin gidan baya mata dad'i, da kyar ta tashi ta bar falon bayan tayi wa Afiya good night wanka tayi ta shirya cikin doguwar riga iya gwiwa ta hau gadon bayan tayi addu'a ta kwanta tare da light off na d'akin.
Lumshe idanuwan ta tayi cike da tunanin ko wane hali baffa yake ciki yanxu da tana da waya da ta kira taji muryar sa, da ta nemi yasmeen sun yi hira duk da basu tare, sai taji tana son riqa waya a yanxu ko yaya ne saboda sanin muhimmancin ta, ta jima tana tunanin kafin barci mai nauyi yayi awon gaba da ita.
Can cikin barci taji kamar mutum cikin jikinta yana taba ta, a firgice ta tashi xata kurma ihu yayi saurin riqo ta yana fad'in,
Xaki min tonon asiri ne cikin wannan daren, cikin bacin rai tace amma me kake yi anan har kaxo ka kwanta a saman gado.
Ya tashi ya kunna makunnin fitilar d'akin yana fad'in sauko, kallon sa tayi fuskar sa babu alamar wasa, a sanyaye ta sauko daga saman gadon tana kallon sa, hanyar waje ya nuna mata yace muje d'aki na.
Ta langabar da kanta tana fad'in me xanje yi, nifa barci nake ji ka kyale ni.
Yace kika sake bud'e baki kika min magana sai kin gane kuren ki, kuma kada kixo ki gani ya fita daga d'akin, qaramin tsaki taja a hankali batare da ta bari ya ji ba tabi bayan sa tana qunquni kome xan masa a wannan daren da baxai bari har gobe ba.
Suna shiga d'akin kai tsaye toilet ya nufa ya barta gurin, ta gaji da tsayuwa ta xauna tana tunxure baki, jin motsin fitowar sa yasa ta juya tana kallon wurin, yana tsaye da d'aure da towel iya qugunsa ga qarami a hannunsa yana tsane gashin kansa, kallon shi take cikin mamaki komai nasa na manyan maza ne tun daga faffadan qirjinsa, ya qaraso cikin d'akin qofar ya rufe da key yana kallon ta, xo ki taimaka min na shirya.
Hankalin ta ya tashi, ta yamutsa fuska kamar xatayi kuka Dan Allah kayi haquri ka barni na tafi ni barci nake ji.
Yace ai anan ma barci xakiyi, daga yau har na bar gidan nan tare xamu riqa kwanciya kuma duk ranar da baki xo ba ko... amma ki gwada ko sau d'aya ki gani, cikin fad'uwar gaba take kallon sa tana fad'in barci tare xamu riqa yi saboda me, da can tare muka saba kwanciya ne, ta tashi tana fad'in ni baxan kwanta da kai d'aki d'aya ba, ya fisgota tare da maida ta saman gadon yana nuna ta, xan nuna maki nafi ki taurin kai da kafuwa kuwa, ya juya ya cigaba da abinda yake, tana xaune tana kallon ikon Allah ya shafa wannan ya goga wannan sai kace wata mace, lokacin da yaxo saka kaya ganin babu kunya a gabanta xai saka yasa tayi saurin rumtse idanu tana innalillah, ko da ya gama ya rage hasken d'akin ya kwanta yana nuna mata kusa dashi, xo nan ki kwanta.
Ta tsura masa ido batare da ta motsa ba, cikin tsawa yace bakya jine? ba shiri jiki na rawa taje kusa da shi amma ta kasa kwanciya sai ruwan hawaye take, fisgota yayi ya kwantar da ita a jikinsa tare da rungume ta sosai yana lumshe idanuwan sa, tsura masa ido tayi har lokacin ta kasa rumtse idanunta saboda tsoro, sultan bai ma san tana yi ba yanayin da suke ciki ya saka barci mai dad'i yayi awon gaba dashi, jin saukar numfashin sa da yanda ya sassauta riqon da yayi mata ya tabbatar mata yayi barci, ta kai fuskarta dai dai wuyansa tana shaqar qamshin jikin sa tuni barci yayi awon gaba da ita.
Tun daga ranar tare suke kwanciya duk da ba abin dake had'asu sosai ta saba da kwanciya tare dashi kuma tana jin dad'in haka, wani lokacin ma idan ya jima bai dawo ba takan je d'aki ta jira sa, sai dai ya dawo ya same ta tayi barci.
Ranar da su yasmeen suka dawo sai wani bata fuska take musamman da dare yayi, yasmeen sai labari take bata soyayyar ta da fu'ad da bata ma so dawowa ba amma hankalin hidaya baya kanta yana gun nata mijin, kwanciya tayi a gadon sai take jin ba dad'i duk da yasmeen na kwance akai amma ganin sa take ya mata kwanciya, ta tashi tana gyara igiyar rigar barcin ta tana yatsina fuska kamar bata so kada yasmeen d'in ta xarge ta, tace yaya sultan ke nema na tun d'axu.
Yasmeen ta dube ta tana fad'in shine baki je ba sai yanxu kin ma raina sa, da yaya fu'ad ne ya kirani tun d'axu baxa ki ganni anan ba, ni wlhy banji dad'in dawowa ba kinga acan sai mu raba dare muna tare muna hira kamar kada mu rabu.
Hidaya ta bud'e idanun ta tana kallon ta like serious sis, ke bakya jin tsoron sa?
Tsoron me?
Yasmeen ta tambaya tana kallon ta cikin mamaki.
Hidaya ta cije yatsa cikin tunani sai kuma ta dube ta tana fad'in qila baya maki irin abinda yaya sultan ke min ne, yanxu tare fa muke kwanciya kullum sai ya wani matse ni a jikinsa a hakan kuma naji na saba baxan iya barci batare da shi ba.
Yasmeen ta gimtse dariyar ta tana fad'in chab garin dad'i na nesa Allah ya kaimu lokacin ni da yaya fu'ad xaki ga love bird, ki cigaba da yiwa yaya sultan wulaqanci kin san namiji da son gata yana son ana kula dashi da shagwaba shi idan bakya masa haka xai je ya nema a gurin wata before you know xaki ji ana maganar xai qara aure.
Hidaya ta bata fuska tana kallon ta amma ni menene bana masa.
Yasmeen ta tabe baki tana fad'in komai ban gani ba, ke da kike nuna masa halin ko in kula ma baki damu dashi ba, abinda yayi maki a baya ya kamata ace kin yafe kin manta ki dawo da soyayyar da kike masa before.
Hidaya tace ni na gayamiki bana son sa, tuntuni na yafe masa amma kinsan me yayi min ranar fa da safe inda wata yaje ko hanifa ne sunan ta ko miye ma na manta.
Washe gari suna kitchen tare da Afiya kamar ko yaushe, ta fito daga kitchen d'auke da kaya xata nufi dinning tajiyo qamshin turaren sa, muryar sa taji yana fad'in ki jira ni yanxu xan iso, ya tsinke wayar yana kallon hidaya itama shi take kallo kamar baxata gaida shi ba sai kuma ta gaida shi tana d'auke kanta, bai amsa ba yayi shigewar sa kitchen ta bisa da kallo tana fad'in a fili kamar na kwarai bayan baa san abinda yake aikatawa a boye ba, sarai ya ji ta kuma ya san dashi take sai ya juya ya d'an dube ta yana d'auke kansa bayan ya qarasa ciki,
Mami xan fita yanxu amira ta kirani mota ta tsaya masu a hanya xanje na duba na gani.
Tace shi fu'ad fa?
Yace kin manta baya gari yaje auren abokin sa Kaduna.
Tace haka ne amma ka tsaya kayi breakfast tukunna tunda an kammala, ya fito yana fad'in jirana take fa a hanya idan na dawo xanci tunda ba jimawa xan yi ba, yasa kai ya bar falon.
Wacece ke jiran sa a hanya ta tambayi kanta tana bin sa da kallo har ya bar falon, haka kawai taji sam xuciyar ta ba dad'i wanda ta rasa dalilin haka, falon ta bari taje tayi wanka idanun ta akan clock fiye da minti talatin bai dawo ba, wurin wacece yaje haka?
Fitar mera gidan bada jimawa ba ya dawo, suna falo xaune su biyu, ya xauna yana fad'in mami kin ganni sai yanxu duk na gaji Haneefa tace a gaida ki.
Tace ina kuma ka had'u da ita yaushe ta dawo qasar,
Ya tashi yana fad'in can na same ta tare da su amira,
Tace breakfast d'in fa?
Yace am ok naci a gurin mummy, yayi shigewar sa.
Sam ta kasa sukuni wacece hanifa ma da tun d'axu yake gurin ta sai yanxu yake dawowa.
Kamar daga sama Afiya taji tana tambayar mamee wacece hanifa?
Daughter wata friend d'ita ce kusan sa'annin juna kuke ma amma xata girme ku keda yasmeen kad'an ba anan suke xaune ba ita da iyayen ta suna Cameron,
Hidaya ta jinjina kai tana tabe baki Afiya kuwa kallon ta take ganin damuwa a fuskarta ko kishin sultan take, murmushi tayi tana qara kallon ta tana cewa ke hidaya haka kika ga anayi miji ya dawo baxaki masa sannu da xuwa ba kuma ki ta xama batare da kin bisa kin masa ya gajiya ba, haka kika ga ina yi da nawa mijin.
Hidaya tayi shiru kuma batada niyar tashi, Afiya ta tashi tana fad'in sai ki ta xama kina barin mijin ki cikin kadaice a hakan xai kyallo wata dake nuna masa kulawa ya fara son ta har kiji anan maganar aure Ma kina xaune sake da baki.
Haka kawai taji hankalin ta is tashi karfa mgnr ta xama gaske, ta turo baki tana barin falon kamar baxata je d'akin na sa ba saw kuma ta shiga da sallama ciki ciki kamar bata so.
Jin muryarta ya saka shi juyowa daga wayar da yake, yana kammalawa kallo d'aya yayi mata ya d'auke kansa daga gare ta, kamar bata so tace barka da dawowa, bai amsa ba amma ya kafe ta da idanunta, kamar baxai yi magana ba sai kuma ya matso daf da ita yana fad'in har yanxu xuciyata ta daina xargin cewa tun farko ba sona kike ba, ta d'ago tana kallon sa sai kuma ta juyar da kanta gefe tana yatsina fuska batare da tayi magana ba, shima tabe bakin sa yayi ya juya abinsa, ta fice da sauri.
Daren yau ma ya kasance su biyu kad'ai ne a gidan su yasmeen sun qi dawowa, ta gaji da xaman kadaici sai take jin gidan baya mata dad'i, da kyar ta tashi ta bar falon bayan tayi wa Afiya good night wanka tayi ta shirya cikin doguwar riga iya gwiwa ta hau gadon bayan tayi addu'a ta kwanta tare da light off na d'akin.
Lumshe idanuwan ta tayi cike da tunanin ko wane hali baffa yake ciki yanxu da tana da waya da ta kira taji muryar sa, da ta nemi yasmeen sun yi hira duk da basu tare, sai taji tana son riqa waya a yanxu ko yaya ne saboda sanin muhimmancin ta, ta jima tana tunanin kafin barci mai nauyi yayi awon gaba da ita.
Can cikin barci taji kamar mutum cikin jikinta yana taba ta, a firgice ta tashi xata kurma ihu yayi saurin riqo ta yana fad'in,
Xaki min tonon asiri ne cikin wannan daren, cikin bacin rai tace amma me kake yi anan har kaxo ka kwanta a saman gado.
Ya tashi ya kunna makunnin fitilar d'akin yana fad'in sauko, kallon sa tayi fuskar sa babu alamar wasa, a sanyaye ta sauko daga saman gadon tana kallon sa, hanyar waje ya nuna mata yace muje d'aki na.
Ta langabar da kanta tana fad'in me xanje yi, nifa barci nake ji ka kyale ni.
Yace kika sake bud'e baki kika min magana sai kin gane kuren ki, kuma kada kixo ki gani ya fita daga d'akin, qaramin tsaki taja a hankali batare da ta bari ya ji ba tabi bayan sa tana qunquni kome xan masa a wannan daren da baxai bari har gobe ba.
Suna shiga d'akin kai tsaye toilet ya nufa ya barta gurin, ta gaji da tsayuwa ta xauna tana tunxure baki, jin motsin fitowar sa yasa ta juya tana kallon wurin, yana tsaye da d'aure da towel iya qugunsa ga qarami a hannunsa yana tsane gashin kansa, kallon shi take cikin mamaki komai nasa na manyan maza ne tun daga faffadan qirjinsa, ya qaraso cikin d'akin qofar ya rufe da key yana kallon ta, xo ki taimaka min na shirya.
Hankalin ta ya tashi, ta yamutsa fuska kamar xatayi kuka Dan Allah kayi haquri ka barni na tafi ni barci nake ji.
Yace ai anan ma barci xakiyi, daga yau har na bar gidan nan tare xamu riqa kwanciya kuma duk ranar da baki xo ba ko... amma ki gwada ko sau d'aya ki gani, cikin fad'uwar gaba take kallon sa tana fad'in barci tare xamu riqa yi saboda me, da can tare muka saba kwanciya ne, ta tashi tana fad'in ni baxan kwanta da kai d'aki d'aya ba, ya fisgota tare da maida ta saman gadon yana nuna ta, xan nuna maki nafi ki taurin kai da kafuwa kuwa, ya juya ya cigaba da abinda yake, tana xaune tana kallon ikon Allah ya shafa wannan ya goga wannan sai kace wata mace, lokacin da yaxo saka kaya ganin babu kunya a gabanta xai saka yasa tayi saurin rumtse idanu tana innalillah, ko da ya gama ya rage hasken d'akin ya kwanta yana nuna mata kusa dashi, xo nan ki kwanta.
Ta tsura masa ido batare da ta motsa ba, cikin tsawa yace bakya jine? ba shiri jiki na rawa taje kusa da shi amma ta kasa kwanciya sai ruwan hawaye take, fisgota yayi ya kwantar da ita a jikinsa tare da rungume ta sosai yana lumshe idanuwan sa, tsura masa ido tayi har lokacin ta kasa rumtse idanunta saboda tsoro, sultan bai ma san tana yi ba yanayin da suke ciki ya saka barci mai dad'i yayi awon gaba dashi, jin saukar numfashin sa da yanda ya sassauta riqon da yayi mata ya tabbatar mata yayi barci, ta kai fuskarta dai dai wuyansa tana shaqar qamshin jikin sa tuni barci yayi awon gaba da ita.
Tun daga ranar tare suke kwanciya duk da ba abin dake had'asu sosai ta saba da kwanciya tare dashi kuma tana jin dad'in haka, wani lokacin ma idan ya jima bai dawo ba takan je d'aki ta jira sa, sai dai ya dawo ya same ta tayi barci.
Ranar da su yasmeen suka dawo sai wani bata fuska take musamman da dare yayi, yasmeen sai labari take bata soyayyar ta da fu'ad da bata ma so dawowa ba amma hankalin hidaya baya kanta yana gun nata mijin, kwanciya tayi a gadon sai take jin ba dad'i duk da yasmeen na kwance akai amma ganin sa take ya mata kwanciya, ta tashi tana gyara igiyar rigar barcin ta tana yatsina fuska kamar bata so kada yasmeen d'in ta xarge ta, tace yaya sultan ke nema na tun d'axu.
Yasmeen ta dube ta tana fad'in shine baki je ba sai yanxu kin ma raina sa, da yaya fu'ad ne ya kirani tun d'axu baxa ki ganni anan ba, ni wlhy banji dad'in dawowa ba kinga acan sai mu raba dare muna tare muna hira kamar kada mu rabu.
Hidaya ta bud'e idanun ta tana kallon ta like serious sis, ke bakya jin tsoron sa?
Tsoron me?
Yasmeen ta tambaya tana kallon ta cikin mamaki.
Hidaya ta cije yatsa cikin tunani sai kuma ta dube ta tana fad'in qila baya maki irin abinda yaya sultan ke min ne, yanxu tare fa muke kwanciya kullum sai ya wani matse ni a jikinsa a hakan kuma naji na saba baxan iya barci batare da shi ba.
Yasmeen ta gimtse dariyar ta tana fad'in chab garin dad'i na nesa Allah ya kaimu lokacin ni da yaya fu'ad xaki ga love bird, ki cigaba da yiwa yaya sultan wulaqanci kin san namiji da son gata yana son ana kula dashi da shagwaba shi idan bakya masa haka xai je ya nema a gurin wata before you know xaki ji ana maganar xai qara aure.
Hidaya ta bata fuska tana kallon ta amma ni menene bana masa.
Yasmeen ta tabe baki tana fad'in komai ban gani ba, ke da kike nuna masa halin ko in kula ma baki damu dashi ba, abinda yayi maki a baya ya kamata ace kin yafe kin manta ki dawo da soyayyar da kike masa before.
Hidaya tace ni na gayamiki bana son sa, tuntuni na yafe masa amma kinsan me yayi min ranar fa da safe inda wata yaje ko hanifa ne sunan ta ko miye ma na manta.