← Book details Sartse Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 8 OF 39

Sashe 8

Sartse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Na kalli me mashin Win na kalli hanya, sannan na ce. 

"Wannan layin zaka shiga." 

********

08:30pm

Kamar wancan lokacin na farko da na haWu da Fahad Ta'ambo na kasa mantawa da komai na shi, to yau ma haka. Tun dawowa ta na ™ure a Waki ina zaune ni kaWai ina maimaita duk wata kalma guda Waya da ya faWa a cikin zuciyata. 

Hajiya ce ta le™o tare da faWin. 

"Rawasiya me kike yi a Waki ne, bazaki ci abinci ba ne?" 

"A'a Hajiya na ci acan, duk gjiya ce wallahi ke ci na." 

"Mene abin gajiya a zuwa Fagoji? Sai ka ce yau kika fara?" 

"Bazaki gane ba Hajiya." 

Na faWa ina juya baya. 

"Eyh, bazan gane wannan karatun sangartarba." 

Ta faWa tare da ficewa, ni dai daren nan haka na ™arar dashi a Waki ina ta hango kammanin kyakyawan matashi Fahad Ta'ambo. 

Washe gari ma dai da mafarkin kyakyawar fuskarsa na tashi, ni dai ban taSa soyayya ba, amma nasan yanayin da nake ji game da Fahad na san yanayi ne na soyayya. A gurguje na yi shirin makaranta na fito tsakar gida na Wauki abin kari na na yi, bayan na karya na amshi kuWin makaranta wajen Alhaji na nufi makaranta. 

FUD STAFF SCHOOL

11:30am. 

Tun da aka fita break ban matsa ko ina ba daga kan bencina, duk ™awayena su Fauziya Tasi'u su Malaika sun fita sun dawo amma sun tarar dani anan zaune. Malika safwan ce ta zauna kusa dani tana faWin. 

"Nana meke dumunki ne haka? Tun Wazu kina zaune sai faman murmushi kike?" 

"Murmushi?"

Na faWa da alamun tambaya. 

"Au baki ma san kina murnushin ba, sai dake malamar soyayya." 

Ta faWa tana dariya, na kalleta na ga yanayin ta ko a jikinta, daman Malika irin wayayyun 'ya'yan nan ne, dan a yanzu haka ma tana da saurayi abunta, idan anyi magana sai ta ce 'idan basu yi min aure ba, ji™ani zasu yi su sha?.' A yanzu haka har cikin Malamai tana da saurayi, sabida wayewarta ma Malaika Arora ake ce ma ta. 

"Ni Malaika ban faWa wata soyayya ba." 

Na faWa bakina yana rawa, kallona ta yi sannan ta ce. 

"Mai da karuwa 'yar iska." 

Tana faWin haka ta juya ta shiga sabgoginta ta barni da faman tunani. 

"Ya zaayi ace na faWa soyayya, faWawar da har wani zai iya ganewa, ko da yake a wayewa da gogewa irinta Malika ba abun mamaki ba ne dan tasan haka, amma ta ya zaayi na fara soyayya da mutumin da ko sunana bai ta Sa tambaya." 

Haka na yini sukuku, har washe gari ma hakan, sai da aka sake Waukan sati ina cikin wannan yanayin kafin na ji na dawo daidai, sai dai a cikin wannan satin fa duk ™awaye na sun yarda da maganar Malaika kan na faWa soyayya. Ni kam tsakanina dasu sai da ido, daga baya ne ma na fara biye musu har wata rana suka ce wai sai na zayyane musu kammanin mutumin, da na rufe idona kawai sai na ganshi ya harWe hannu yana kallona. 

Duk yadda na kai ga gaya musu cewar yadda na fasalta musu shi, haka yake a gaske sun ™i yarda, dan daga masu cewa jaruman indiya nake fasaltawa, sai mai cewa larabawan Dubai ne, ni kam daga ranar ban sake biye musu ba. 

A lissafina ranar da na cika kwana goma da haWuwa da Fahad Ta'ambo na sake ganinsa, sai dai abun da ya yi matu™ar bani mamaki shine inda na gansa, daga can gaban gate Win makarantarmu, da sauri na juya baya sai dai naga idanun ™awaye na akansa. Fauziya ta yi saurin matsowa kusa dani sannan ta ce. 

"Ke Rawasiya! Wannan ai shine sak mutumin da kika fasalta mana, ko shine?" 

Na gyaWa mata kai, gaba Waya na rasa nutsuwa ta, kamar ko da yaushe. Da zarar ya Wor ™awayar idonsa a kaina, shikenan na rasa nutsuwata. 

"Gaskiyya ™arya kike Rawasiya." 

Mailaka ta faWa a saitin kunnena. 

"Kina ganin yadda yake kollonta, zaki ce ™arya ne." 

Amina Aminu ta faWa.. 

"Wannan ai yafi ™arfinki Rawasiya, bama haWi wallahi."

Na ji muryar Malika ta faWa, a take Amina Aminu ta cafe da cewa. 

"Ni ban ma yarda ba, gashi dai gani nake da idona, amma na kasa gasgatawa." 

"Kinsan kuwa wane ne Fahad Ta'ambo?" 

Malaika ta faWa, daidai kuma lokacin ya fara takawo kusa da mu, ni kam gaba Waya sai na ji maganganunsu sun tsayan a raina, ni kaina nasan tabbas wannan saurayin yafi ™arfina, bazan taSa samun wannan saurayin ba domin kuwa duk wani abu da ake nema ya haWa. Kyau, kuWi, Nasaba, gayu, ilimi da duk wani abu da 'ya mace ke nema wajen datattacen Namiji. 

Gaba Waya daskarewa na yi na kasa motsi, kar na yaudari kaina Fahad ba tsarar aure na ba ne. 

"Yau ba magana ne, kin wane tsari ni da ido kamar yau kika fara kallona?" 

Ya faWa daidai lokacin da ya iso, gaba Waya yau sai na rasa wannan yanayin da nake ji idan yana gabana, jikina sanyi ™alau na ce da shi. 

"Ina wuni?" 

Kallona ya yi sannan ya kalli ™awayena ya ce. 

"Baki da lafiya ne?" 

"A'a, ina da lafiya." 

Na faWa ina kallonsa.

"Uhm." 

Ya faWa yana taSe baki irin bai damu ba. Ganin na yi shiru kusan minti biyar, kuma ban tafi ba ya sa shi cewa. 

"Ina so mu yi magana ranki ya daWe, naga yau a saurauniyar ki kike." 

Bin shi kawai na yi a baya, ™awaye na dai suna bina da na mujiya. Har mu ka ™arasaa bakin motarsa ina jin idanunsu akaina. 

"Me yake damunki?"

Ya faWa yana kallona, girgiza kai na na yi sannan na ce. 

"Bakomai" 

"™awayenki ne?"

Na Waga sannan na ce. 

"Wai sun ce idan kai saurayi na ne yaudarata zaka yi ba zaka taSa aurena ba. Sabida kafi ™arfina." 

"To ke me kika gani?" 

Ba tare da wani lissafi ba na ce. 

"Da gaske suke." 

Ya yi murmushi sannan ya ce. 

"Rawasiya daman ni na ce saurayinki ne?" 

Na gwalalo ido waje sannan na ce. 

"Kasan suna na? Aina?" 

"Taambayar da na yi miki kenan?"

Na girgiza kai sannan na ce. 

"A'a da a'a." 

"Mene a'a da a'a?" 

Ya tambayeni yana kallona. 

"Da ka ce tambayar da ka yi min kenan shine a'a ta farko, a'a ta biyu da ka ce daman ka ce kai saurayi na ne?" 

Murmushi ya yi sannan ya ce. 

"You're very funny, I love it girl." 

Na yi murmushi sannan ya ce. 

"Baki tambayeni me nake yi anan ba?"

A raina na ce. 

"Duk inda nake ganinka da na taSa tambayarka me kake yi a wajen?" 

"Sabida yau wajenki na zo shi ya sa na tambayeki." 

Na ji muryarshi ta katse min tunani na. 

"Shekararka nawa?"

Na tsince kaina da tambayarsa, sai da ya ™are min kallo sannan ya ce. 

"Ashirin da shida." 

Wani daWi na ji ya ratsani, irin mijin da nake so. 

"Ke fa?" 

Na ji ya tambaya. 

"Goma sha bakwai da rabi." 

"Ko ba rabi ba?." 

Ya tambaya yana dariya.

"Yau na ganka da sau™in kai, daman haka kake?" 

Na tambayeshi, sai dai ya yi dariya sannan ya ce. 

"Au da da zafin kai nake zuwa kenan?" 

"™awayena bari na tafi." 

Na faWa ina nuna masa su, nan take ya haWe rai ya dawo asalin Ta'ambo da nasani. 

"Je ki." 

Ya faWa cikin wani irin amon murya, ba shiri na tsaya na kasa tafiya. 

"Je ki mana." 

Ya faWa yanzu muryarsa da alamun fusata. 

"Ka yi ha™uri."

"What do you do? Kin nuna sun fini amfani da muhimmanci to sai me?" 

Gaba Waya jikina ya fara rawa, duk na rikice lokaci Waya, bakina har rawa yake na ™ara cewa. 

"Ba haka ba ne fa."

Legendspen

08*SARTSE*

-Amanar-Janafty-

*Sayyid Legendspen*

MAH/2026/001

Sadaukarwa.

RAMLAT ABDULRAHMAN MANGA

(Mai Dambu) 

Shafi na shida

    (06)

Bai ko kalleni ba ya shige mota ya tafi, na kusa minti biyu a tsaye sannan na juya ga su Malaika. 

Ku zo mu tafi.  

Wallahi Nana ban yarda saurayinki ba ne sai yanzu.  

Fauziyya ta faWa bayan sun ™araso inda nake. 

Ni har yanzu ma mamaki nake, kinsan su waye familyn Ta Ambo kuwa? Kaf jihar jigawa suna cikin manyan masu kuWi guda biyar,  yan kasuwa ne na gaske masu arzi™i, duk a turai suke rayuwarsu baki Waya, wannan ma kina ganinshi kinsan ba rayuwar nan ba ne, gashi duk ya yan attajirai suke aure.

Tin da Malaika ta fara magana har ta dire idanuna na kanta, domin nasan gaskiyya take faWa zalla ma kuwa. 

Idan kuwa hakane tabbas wannan yafi ™arfinki Nana, ina baki shawarar karki Waurawa kanki abinda bazai Waure ba, kizo ki sha wahala a banza.  

Fauziyya ta faWa tana dafa ka faWa ta, ni basu san abinda ke damuna ba wannan ba ne, fushin da ya yi ya tafi ya barni yafi komai Waga min hankali. 

Yanzu yaushe zan sake ganinsa?  

Na tambayi kaina sai dai ba mai bani amsa, tsoro na Waya kar ya yi dogon fushi, fata na dai Allah Ya kawo shi da wuri, sai dai fatan ba ai amso ba dan haka aka yi sati Waya babu shi babu alamunsa, duk na damu gashi ni irin mutanen na ce da ba su iya faWar damuwarsu wa wani ba, sai dai na bar abu a zuciyata ya yi ta cina, ni kam sai dai aga ina ta rama duk na zagwanye. Haka kuwa aka yi na yi ta faman rashin lafiya a tsaye babu zazzaSi sai ciwon kai sama sama, tari da kuma Wacin ma™wogwaro, haka na yi ta fama sati Waya sati biyu har sati uku, hankali Hajiya da Alhaji duka ya tashi, kowa yasan akwai abinda ke damuna amma nakasa faWa. 

Haka su Malaika ko da yaushe sai sun tambayeni saurayina, kuma a ko yaushe sai sun nusar dani cewar yafi ™arfina, tun ban fiya sa abun a rai ba har na yardarwa kaina Fahad yafi ™arfina, har na fara jin cewa ya gane yafi ™arfina ne shi ya sa ya tafi bai sake zuwa ba.
Chapter 8 · 0% Book details