← Book details Sartse Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 3 OF 39

Sashe 3

Sartse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Nana duk runtsi duk wuya ka da ki bari wani ya shiga tsakanin ki da mijinki, ina faWa miki hakane a matsayina na mijinki, mai ™aunarki." 

Cike da farin ciki da gamsuwa da soyayyarsa na ce. 

"Tom in sha Allah, yanzu kaje ka yi wanka zan kunna wutar gawayin na soya na kawo ma." 

"Tom ki yi sauri kinsan dai fita nake son yi." 

Ya faWa yana juyawa ya fice, ni kuma na kulle ko ina na kicin din na fara ™o™arin kunna wutar. 

Gaba Waya kicin Win ya turni™e da haya™i wanda ya tsaya mini a ma™wogarona na fara tari babu ™a™™autawa, ba shiri na tsugguna a ™asa na fara kakari, ina jin kamar hanjin cikina zai fito waje, da ™yar na iya tashi na fara buWe kokafin bayan na ga wutar ta kama. Idona fal da ™wallar da ta taru sabida haya™i na tashi na Wakko farantin silba na shiga firfita wutar har takama. 

Na sakko da kaskon daga kan gas din na Wora akan kurfotin, ina yi ina firfitawa har man ya yi zafi na fara sanya fanken ina soyawa. Kusan minti talatin sannan komai ya kammala na juye a filas na fito falo, yana zaune kan kujera Waure da tawul Win wanka. 

Kan Dining na nufa na ajiye plast Win, sannan na koma Kicin na Wakko kufuna da faranti na dawo na jera akan dining sannan na dawo cikin falon. 

"Komai ya kammala." 

Na faWa ina ™o™arin zama sabida sandarewa da na ji bayana ya yi, sakamakon dur™ushen da na yi na soyawa fanken, kallona ya yi sanan ya ce.

"Ni ai ban kammala ba! Ko ni zan shirya kaina ne?." 

Murmushin ya™e na yi sannan na ce. 

"Aha ba dai! Ya zaayi ka shirya kanka ni ina nan, mene amfanina?."

"Babu kam, idan har ba zaki yi mini biyayya ki faranta rai ba, babu." 

"Mene haka?." 

Na faWa arazane sakamakon abinda nagani, sosa ™eya ya fara yi sannan ya ce. 

"To na buWe zan shirya tun da naga kina kicin, kuma ni banga kayan da suka yi mini ba shine sai na fito dasu duka." 

Yanayin yadda ya yi magana ya yi matu™ar burgeni, ya kuma goge mini dukkanin Sacin ran da sheWan yake son san ya mini. 

Na yi murmushi ina matsowa sannan na ce. 

"Ai da ka jirani, amma bari na duba maka nina san wa'yanda zasu yi maka kyau." 

Na tsugunna a ™asa na fara kwashe kayan da ya zuzubar a ™asa ina zuba su kan gadon, sai da nagama kwashe su tsaf sannan na ce.

 "Bari naga wanda zaifi maka kyau." 

"Hon!." 

Na ji sassanyar muryarsa ta kira sunan ds na tabbatar sai soyayya ta yi daWi yake kiranshi. 

"Naam Hon!."

Na amsa masa nima cikin tawa sassanyar muryar da nasan ba ta yi ko rabin tasa a daWi da sanyi ba, abu guda Waya da nake ™ara yararwa kaina shine. Sardauna Mijina ba tsarar aure na ba ne, Sardauna ba aji na ba ne, Sardauna yafi ni komai, ko na™i ko na so Sardauna alfarma ya yi mini ya aureni, sabida yana sona. 

"Kayan nan kamar ba'a taSa gogesu ba ko?." 

Ya faWa yana taSa kayan a yamutse kamar ba na sa ba. Da mamaki na kalleshi, sannan na kalli kayan, inda sardauna yake kai wanki da guga ba ™aramin waje ba ne a Duste, idan suka yi maka wanki zaka rantse kayan ba a taSa sa su ba, gasu nan suna she™i amma yake cewa kamar ba'a taSa gogewe ba, 'ko ya fara ciwon ido ne?'

"Ko?" 

Ya sake faWa, sai da na yi murmushi sannan na ce .

"Wai Hon me ka gani ne?"

"Duk sunyi wani sikwizin, kamar an ™wato su daga bakin kura." 

Na yi dariya ganin yadda yake taSe hanci, kamar yana ri™e da kashi. 

"To ai duk kaine ka yi musu haka." 

Na faWa ina ci gaba da duba kayan. 

"To ai bansan zasu yi haka ba, yanzu haka zan dinga fita kamar almajiri?." 

Ya faWa kamar zaiyi kuka, gaba Waya naji nustuwata tana shirin barin gangar jikina, a ruWe na ce. 

"A'a Hon! Ya zaayi ka fita a haka? Zan bawa Madu ya kai wajen guga a sake gogewa, tun da kaga mu nan bama amfani da abu mai jan huta, mussaman dutsen guga, Tv, hita, da kukin gas, wani lokacin ma cewa kake a kashe fanka sabida Mita kuWin wuta da wahala." 

"To ya zaayi idan abu yakama dole ayi, ki yi amfani da dutsen kawai ki gogesu, amma kafin na dawo fa dan Allah Hon." 

Haka kawai sai naji jikina ya yi wani iri, Miji na da nake so, nake ™auna sama da komai shine zai dinga haWani da Allah akan na yi masa guga, guga dai abar banza. 

"Haba Hon! Haba Haba! Kafin ka dawo angama in sha Allah." 

Na faWa ina mi™a masa wani light bulun yadin. 

"Kaga wannan bai yi sikwizin sosai ba." 

KarSa ya yi yasa, ni kuma na Wau mataji na hau taje masa gashi, sai da gashim ya yi kyau sannan na sa masa hularsa, na fesa masa turare muka fito. 

"Nifa na makara gaskiyya, na yi birek fas a ofis kawai." 

Ya faWa yana niyar ficewa.

 "Haba Hon, ka tsaya dan Allah."

"Hon it is almus 10:30, na makara sosai fa, ki ajiye min idan na dawo na ci."

Bai jira amsa ta ba ya fice, yunwar da nake ji tun ta daren jiya da kuma ™arin ta yau da safe ya sa na nufin kan dinning Win na fara cin abincina, bayam na kammala na kwashe koma na kai kicin, sannan na shiga ayyukana. 

Ban ni na kammala komai ba sai wajen ™arfe tara da rabi, Sardauna ya kawo mun masu aiki har guda huWu amma ina sallamarsu, Allah Ya gani ina tausayin mijina bana so na ga yana ta kashe kuWi a aikin banza, shi ya sa da ya kawo nake sallamarta, amma sai ya sake kawo wa, wai ance yawan aiki yana sa mace ta tsufa shi kuma bai son ma tsufa, sai da na yi da gaske kafin na fahimtar dashi cewar na haka ba ne. 

Ina zama kan kujera bacci Sarawo ya yi gaba dani ba tare da sani na ba. 'Gur! Gur! Gur!' Cikin bacci nake jiyo kukan wayata, ba shiri na buWe ido na kai hannu na Wauka, sunan Fauziyya ya bayyana akan Skirin Win wayar, bude ido na na yi gaba daya na ™arewa wayar kallo, ina son Wauka ina jin tsoron Sardauna ya rabani da kula ™awaye, haka wayar ta ™araci kukanta ta gama kiran ya katse, sai a lokacin na duba naga wannan shine kira na bakwai da ta yi mini. 

"Ko mutuwa aka yi?." 

Na tambayi kaina, ba shiri na fara kokarin buWe wayar na kira ta, sai dai ban kai ga kiran ba na ta kiran ta sake shigowa, Wagawa na yi da faWin. 

"Salamu alaikum, Fauziyya." 

Na faWa murya ta ™asa ™asa. 

"Nana ina kika saka wayarki, ina ta kira?." 

"Wallahi bacci nake Fauziyya, Ya kike?."

"Ina lafiya, matar nan gaskiyya kina hutawa abunki. Sardauna ya tsaya miki."

Na yi murmushi mai nuna jindaWi, sannan na ce. 

"Wallahi tun da ya fita kawai na kwanta." 

"Ai haka ake so, kin ga nazo bayan ku ne gidan yayar mijina shine na ce ko kina gida na biyo, kuma gashi na samu tabbaci." 

Dum! Dum! Na ji gabana ya shiga faWuwa, Sardauna baya sona da kowacce ™awa, bai taSa ce mini kar da ™awayena su zo, amma ya fito ya nuna baya son ina kula su, ba ma iya su ba kowa ba ya so, ni kuma duk wani abu dai zai Sata ran Sardauna bana maraba dashi. 

"Kinyi shiru?" 

Muryar Fauziyya ta dawo dani daga tunanin da na fara. 

"Dan zaki zo gidana sai kin tambayeni? Kawai ki tawo, amma da wuri dan Allah kafin huWu zai zo mu fita." 

"Ah to ko ba sai na zo ba." 

"Kai! Ya zaayi kive haka, kizo mana dan Allah." 

"Toh shikennan yanzu zaki ganni." 

Daga haka ta katse kiran, na mi™e na shiga Wakina na Waura alwala na gabatar da sallah azahar ganin karfe Waya  ta yi, ina idarwa na shiga kicin na Wora taliya jollop, sanin cewa zata iya zuwa a kowanne lokaci yasa na yi amfani da gas na Wora girkin.

Ina fitowa daga Kicin Win, na koma Wakin Sardauna na fara haWe kayan ina ninke su, daniyar idan ta tafi sai na goge su tunda mu nan bama rasa wuta kwata kwata.

Ina cikin ninke kayan na ji sallama a falo, Allah Ya gani bana maraba da dukkan abinda zai Sata ran mijina, na yarda da Allah, na yarda da cewar ina son Sardauna sama da komai.  Hakan ya sa bana farin ciki da zuwan Fauziyya, ™aramin tsaki naja sannan na mi™e na fito, sai na zo dab da falon sannan na janyo murmushin ya™i na sanya shi a fuskata. Itama fuskarta Wauke da murmushin ta tare ni da cewa. 

"˜awatah, ™awar yarinta, ™awar girma." 

Na yi dariya na zauna akan kujera ina faWin. 

"Tawo mana." 

Zama ta yi tana ™are mini kallo. "kin canja gaba Waya abinki, kinsami aljannar duniya."  

Na yi dariya da faWin.

"Alhamdulillah wallahi, bara na kawo miki ruwa kafin mu ci abinci." 

"A'a yana ji ba sanyi a wannan zafin?." 

Ta faWa bayan na kawo mata ruwan, na yi murmushi sannan na ce.

 "Kinga ni mura nake, shi kuma kwata kwata ba ya shan sanyi."

Sai bayan na faWa na yi mamakin yadda na iya shirya ™arya a lokaci guda, na tuna lokacin da muka yi magana da Sardauna akan firjin. 

"Nana! A gidanku babu firinji, baki sa ba shan sanyi ba, sabida yanayin unguwar ku ma zafi ake yi, dan haka anan ma ba zai zama wani abu ba dan na ce ba zaki dinga kunna firinji ba, sabida yanayin jan wutarsa." 

Allah Ya gani ina tausayin mijina, ko bai ce ba nasam yadda kuWin wuta yake anguwar masu kuWi, shi ya sa ma yana faWin haka, na ce Babu matsala. 
Chapter 3 · 0% Book details