← Book details Sartse Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 15 OF 39

Sashe 15

Sartse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Haka mu ka ci gaba da rayuwa cikin so da ™aunar juna, Sardauna yana riritani tamkar ™wai akan cokali wanda ake tsoron faWuwarsa. Ina rayuwa ta cikin farin ciki kowa yana ta ya ni murna, na je gida sau biyu sannan na je gidan yayuna sau Wai Wai, suma sun zo baki Waya har da Ra'is amma banda Yaya Ridwan.  

Ranar wata juma'a bayan ya dawo, yake sanar dani wai ™arshen wannan satin ranar Lahadi suna da baban family meeting, kuma ana bu™atar kowa yaje har da iyalansa. 

Tun da Sardauna ya faWan na fara tunani, danni ban taSa haWuwa da 'yan uwansa ba tun lokacin biki, sai dai 'yan gidansu da ya kaini sau Waya. Hajiyarsa mutuniyar arzi™i da ™annensa duk ba su da matsala, amma fa wannan ya ce wai babban famili meeting, duka 'yan uwansa zasu je. 

Washe gari na kira Yaya Rumaisa a waya na faWa mata bayan ya fita, nan ta bani shawarar irin yadda zan shirya, yadda zan kama kaina a cikinsu, da sauran abubuwa.

Ranar Sunday tun safe, na fara shirina amma ina yin komai cikin nutsuwa sabida kar ya ga rawar kaima, kamar yadda Yaya Rumaisa ta faWa. Bayan munyi breakfast ya ce dani. 

"Ki shirya muje da wuri, zan ajiye ki sai na fita zuwa 12:00 ake farawa, zan dawo kafin lokacin." 

Tashi na yi na shiga Waki, na ™arasa shirina daga nan na dawo falo lokacin shima ya gama shiryawa. 

FADA AREA

09:30am. 

Babban gidane na gaske da ya ji kayan more rayuwa, mutane ne tsilli tsilli cikin gidan sabida basu gama hallara ba, yana gaba ina binsa a baya ya yiwa wayanda ya ga dama magana, ya yi banza da wayanda ya ga dama, har ya kaini inda Hajiyarsu take tare da 'yan uwansu. Dukkansu na gaishesu kamar yadda na ga ya yi, suna ta samin albarka kowacce fuskarta washe da fara'a. 

Bayan mun gaisa ne na koma gefe na zauna a babban falon inda naga Lubna ™anwarsa ta zauna, shi kuma ya tashi ya fice. Kowa sabgar gabansa yake masu danna waya na dannawa masu hira na taSawa cikin harshen turanci, ba ruwan kowa da ni, hakan ya sa nima na ja waya ta na fara dannawa, nan ga message Win Amina Aminu cewar an fara cire WAEC, sun cire tasu a cafe kuma sun sami 8 credit, sannan an fara registration Win Jamb. Na yi mata reply da cewar Okay idan ya shigo zan faWa masa sai ya ciro min. 

"Salamu alaikum."

Da sauri na Waga kai sabida yadda na ji muryar kamar ta Sardauna sai da ba shi ba ne, wannan wani matashin ne daban shima Wan gayu amma Sardauna yafi shi kyau nesa ba kusa ba. 

"Uncle Turaki Welcome." 

Na ji muryar wata yarinya ta faWa tana nufo sa. 

"Dotti, how are you." 

Ya faWa cikin wani irim ™warewar turanci, kamar ma bai iya hausa ba, a raina na ce. 

"Wannan shine TURAKIN? Duk rashin girman SARDAUNA da nake gani, sai naga wannan yafi ™an™antar jiki." 

Na faWa a cikin raina, ™arasowa ya yi inda iyayensu suke ya fara gaishesu cike da girmamawa, ya Wan fi Sardauna sakin fuska amma Sardauna yafi shi komai na duniya, haka kawai sai na ji bai yi min ba sabida yadda suke da mijina. Daga nan ya juyo inda sauran yayunsu suke suka ya fara gaishesu, yadda yake Wan wasa da su Sardauna duk ba ya haka, dan ko da yazo daga Ina wuninku, Ya iyalai shikenan ya tashi ya fice. Amma shi gashinan sai hira suke har da wasa da yaransu, suma sai jan shi suke da hira mafi akasarin hiran na su ma cikin harshen turanci suke. 

A raina na ce. "Su waWannan sun maida turanci yaren uwarsu da ubansu, ba ga yaran ba ga iyayensu ba." Daga nan kuma ya juyo inda muke nan kowa ya fara gaisheshi, nima na gaisheshi ya amsa ba tare da ya kula da ni ba™uwa ba ce a cikinsu. Wata da na ji suna cewa Sister Seemah ta ce. "Blood meet your Amarya." Ta faW tana nuno ni, gaba na ne na ji yana faWawa sabida irin kallo daya ke min, sai da ya kalleni tas sannam ya dawo inda nake. 

"Daga ina?" 

Ya tambayeta, Sister Seemah ce ta matso sannan ta ce. 

"Sardauna's Wife." 

Kallona ya sake yi tare da jijjiga kai, sannan ya ce. 

"Matar ™anina kenan? Me sunanta?" 

"Nana." Lubna ta faWa. 

"Sannu Amaryarmu, sunana Turaki yayan mijinki Sardauna, kuma babban abokinsa." 

Na yi murmushi sannan na sake cewa. 

"Ina kwana?" 

"Lafiya ™alau, ina Wan uwan nawa?" 

"Yanzu ya fita zai dawo."

Na faWa a raina na fara mamakin me ya sa to basa mutunci da Sardauna, amma shi ga shi anan yana sakar min fuska har da cewa matar ™aninsa. 

"Okay zan jirashi a main falo, ya gidan?" 

"Lafiya lau." 

"To Allah Ya sanya alheri, Allah Ya bada zaman lafiya." 

Na buWe baki da niyar cewa Amin, muryar Sardauna ta cika Wakin. 

"Malam matsa daga kusa da matata." 

Legendspen

08129553971.

*SARTSE*

-Amanar-Janafty-

*Sayyid Legendspen*

MAH/2026/001

Sadaukarwa.

RAMLAT ABDULRAHMAN MANGA

(Mai Dambu) 

Shafi na sha Waya.

    (11)

"Kai yaro gyara bakin ka." 

Turaki ya faWa yana kallon Sardauna. 

"Ni kake cewa yaro?"

Sardauna ya faWa yana ™arasowa wajen. 

"Relax boy." 

Turaki ya sake faWa, hannu Sardauna ya sa ya fisgo ni na faWi ™asa, da sauri Matar da na ji suna cewa Hajiya Maama ta shi tana faWin. 

"Sardauna bita a hankali, ba ita a lamarinku."

"Maama me ya sa zai zo kusa da iyalina, mene haWin shi da ita." 

"Shut up malam, bansan har yarintarka ta kai haka ba, na yi tunanin duk wani abu da yake tsakaninmu zai ™are a tsakaninmu ba sai ya shafi iyalanmu ba, amma na fuskanci har yanzu da yarinta a kanka." 

Cike da wani irin fushi Sardauna ya yo kansa, Hajiya Maama ta ce. 

"Dakata Sardauna, anan kaine baka da gaskiyya. Duk wani abu da yake between you guy's ku tsayar da shi iya ku biyu, karku sanya familinku."

"But she is not our family she is mine, my family, so ya yi baya da ita." 

"Sardauna karSi wannan, ka ce she is not our family she is yours?" 

Wata dattijuwar mata ta faWa, ni mamakina ma yadda aka yi ta iya turanci har haka. 

"Dada wasa yake." 

Turaki ya faWa, sai a lokacin na fuskancin yafi Sardauna wayo ne. 

"No let him, allow him to say his mind." 

"Dada wasa nake." 

Sardauna ya faWa. 

"Are you kidding your parents?" 

"Wannam tsohuwa da mita take."

Na faWa a raina. 

"Kar nasake jin irin wannan." 

Ta faWa tare da komawa ciki, ni kuma na tashi zaune, Sardauna ya fice sauran kowa ya koma ya zauna. Haka su ka yi ta fira har zuwa 12 iyayensu maza su ka shigo suka tattauna abinda zasu tattauna daga nan aka ci gaba da hirarrakin su, banda Sardauna da ya fice. Duk lokacin da na Waga kai sai na ga munyi ido huWu da Turaki, wani lokacin ya yi min murmushi wani lokacin kuma ya yi kamar bai ganni ba. 

Haka aka gama zama kowa ya watse ya tafi, Sardauna ko a mota baice dani ™ala ba, bare kuma da aka koma gida. Nima dai ban ce masa ci kanka ba haka shima bai ce min ba, sai zuwa dare bayan ya sake dawowa na yi masa sannu da zuwa, sai da ya kallani sannan ya ce. 

"Aini yanzu dole na kama kaina, nasan matsayina tun da kin raina ni bakya so na." 

Bakina har rawa yake na fara magana. 

"Wallahi ba haka ba ne, shi da kan shi ya yi min magana kuma ni bansan shi ba." 

"Waye? Kar dai ki ce min yaron can, bana so! karki sake maganarsa a gidana, ni ba akan shi nake magana ba, akan ™yale ni da kika yi."

"Ba ™yaleka na yi ba wallahi Allah.." 

"To me kika yi?" 

"Bakomai, kawai bana so ma cika takura ma a yadda kake ranka babu daWi." 

Jawoni ya yi kusa da shi, sannan ya ce. 

"Ni na taSa ce miki kina takura min?" 

"A'a ba ka ce ba." 

"To me ya sa kika yi wannan tunanin?" 

Na yi shiru na rasa amsar da zan bashi. "Uhm? Magana nake." 

"Kawai." 

Kawai me?" 

Ya faWa yana mi™ewa tare da ni zuwa Waki, ya ajiye ni kan gado ya hawo. 

"Ina tambayarki?" 

"Ba kowa." 

"Tom." 

Ya faWa yana matseni a jikinsa, tun zamana a gidansa kusan wata huWu yau ce rana ta farko da wani abu na aure ya shiga tsakanina da shi. sardauna ya zauna da nine kaiwa yana kallona kuma yana ba ni kula, sai a wannan ranar nagane aure da wata wahalal shi da ake faWa. 

Tun daga wannan lokacin zamanmu da Sardauna ya canja taku, da ba ya nuna sha'awarsa a kaina, amm yanzu kullum ne, WaiWaikon rana kune yake fashi. Tun ina jin wahala da azaba har komai ya wuce. Irin azabar da na sha a ranar ta mantar da ni zance jarabawa ta sai da aka kwana biyu sannan na tuna, shima sakamakon wayar da muka yi da Ra'is yake ce min na ba shi number exam card Wina zai duba min, Jamb kuma na yi wa mijina magana ya yi min Regostration. 

Da dadare bayan ya dawo na faWa masa amma dai ya yi banza da ni kamar bai ji ba, haka aka kwana Waya aka kwana biyu shiru bai sake min maganar ba, a kwana na uku na yanke shawarar ™ara tun kararsa da maganar, sai dai a lokacin ma banza ya yi da ni. 

Washe gari Ra'is ya zo mun da sakamakona na WAEC da NECO na yi ta murna ganin result Win, ya ce da ni wai Abba ya fara tambaya akan wai na yi rijistar JAMB ko banyi ba, kar su rufe. 

Lokaci na farko da na fara yi wa wani na gidanmu ™arya akan al'amuran gidan aure. 

"Ra'is ban masa maganar ba, kwana biyu suna aiki a kamfaninsu ne, bai ma cika dawowa da wuri ba, amma in sha Allah zan faWa masa." 

"Tom yakamata dai gaskiyya, kinsan su Jamb ba wani dogon lokaci suke badawa ba fa." 

"Nasani sosai, ina Yaya Ridwan?" 

"Yana nan." 
Chapter 15 · 0% Book details