← Book details Sartse Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 7 OF 39

Sashe 7

Sartse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ya faWa yana mi™amin leda, nasan sa™on bai wuce maset da kalkuketa ba, dan su na ce masa ina so Wazu da safe, sai kuma biskit na makarantar gobe, kafin na gama buWewa Ra is ya ce. 

Hajiya nima ina so littafi nawa sun cika, sannan rulata ta karye.  

Dariya na yi masa sannan na ce. 

Ai Hajiya ba ta da shago.  

Barshi dai ya faWa mata, ina ga kantin zata bini ta karSa masa.  

Alhaji ya faWa, Hajiya kuma ta ce. 

Ina ni ina binka kanti, kawai dai a kawo masa.  

Wannan ya yi bacci ne?  

Alhaji ya faWa yana nuna Wakinsu Ya Ridwan. 

Yana ciki yana faman sana ar.  

Hajiya ta faWa, sannan ta ™ara da cewa. 

Wai ni kuwa Alhaji yaushe yaron nan zai fara zaman kantin nan ne? Ya kamata ya fara rage ma wasu abubuwan da wannan zaman asarar da yake.

Murmushi Alhaji ya yi sannan ya ce. 

Yaron da yake shirin shiga jami a, ina yake da lokacin zaman kanti?

Ni kuwa ansama masa Addmision din ne? Bai ma faWan yadda suka yi da bawan Allah nan ba.  

Hajiya ta faWa sai da Ahaji ya sha ruwa sannan ya ce. 

Ai Isah Nadabon ma ya zo waje na Wazu, har yake yi mini maganar ita Rawasiya.  

Da sauri na katseshi da cewa.

Alhaji Nana dai.  

Banza ya yi dani ya ci gaba da cewa. 

Yana tambaya wai aure zata yi itama ko sai ta yi karatu, na ce dashi sai ta yi karatu, to wai da ya nuna sha awar shi ne akan yana son aurenta, sabida ya na son ya yi tafiya ta shekara biyu kuma shi kanshi zaifi son ace ya tafi tare da iyali ne.

Legendspen

08129553971

*SARTSE*

-Amanar-Janafty-

*Sayyid Legendspen*

MAH/2026/001

Sadaukarwa.

RAMLAT ABDULRAHMAN MANGA

(Mai Dambu) 

Shafi na biyar

    (05)

Tunda Alhaji ya fara magana gabana yake faduwa, aure kuma? Ni ba auren ba ma wallahi kwata kwata bana son mutum ya girmeni sosai, gaba daya shekara ta sha bakwai, Isah Nadabo a yanzu ya kai wajen talatin, ni nafi son yaro dan shawalwali, wanda baifi 26 ba haka, maganar Hajiya ce ta katse min tunanin da na shiga da na tana cewa. 

"To Alhaji kamar Isah Nadabo ai yafi ™arfin haka a wajenmu ko, da an bashi." 

"Kai Hajiya!" 

Na faWa a raina, Alhaji ne ya ce da ita.

"A'a dai, ai bama za ayi haka ba ita yarinyar ba ta da zaSi ne?" 

"Ai shikenan dai, Allah Ya bata na gari." 

Alhaji ya ce.

"Amin."

Ni dai nan zaune bance ko ™ala ba, amma naji dadi gaskiyya, na auri Isah Nadabo na ce na auri wa, ™anin babane ko me? Babba dashi da ace ya yi aure a shekara goma sha wani abun da yanzu yana da yarinya kamar ni, kowacce ta girmi ni ma. Gashi wani baki ma, ni Allah Ya gani ina son dan gayu dan zamani, shi kam kallo daya zaki yi ma Isah Nadabo kinsan mutum ne mara walwala, kansa a kulle yake. 

Daga wannan rana ba a sake wata magana da ta shafi Isah Nadabo ba, kuma nima na ji daWin haka, haka na ci gaba da rayuwa ina 'yan matancina a gida har zuwa ranar da ™addarar YallaSaina ta faWa mini. 

Ranar wata lahadi bayan sallar magariba na fito daga gida ina shirin tafiya makarantar dare da nake zuwa, wacca gaba daya banfi a sati biyu da fara zuwanta ba. Tafiya nake kamar ko yaushe cikin nutsuwa,kamar ance Waga idonki. 

Kyakyawan matashin saurayi, mai kyakyawan yanayi da kyakyawar shiga, fuskarsa fara ce sosai yana da tarin kwantacciyar suma. Gaba Waya kammaninsa ba sa yanayi da na 'yan nigeria sabida yanayin idonsa har wani wal™iya suke mai daukan ido, hancinshi mai matsakaicin tsini haka bakinsa, wani kyakyawan gashin baki ya yi masa ™awayan ya gangaro gefe da gefe ya haWe da Wan ™aramin gemunsa. 

"Ya Hayyu Ya Qayyum!" 

Abinda na faWa a raina, sannan na ce.

"Wasu kamar sune suka hallicci kansu, sabida tsabar tsagwaran kyau, ina ganin Yaya Ridwan yafi kowa kyau ashe mummunane a gaban wannan." 

A hankali ya fara ta kawo yana tun karo ni, wani irin "Dif! Dif!" Na ji ™irjina yana bugawa, ™afafuna suka fara karkarwa, ™walla ta taro a idona sakamakon matsanancin bugun da zuciyata take mai ™arfi. A lokacin da ya matso gab da ni, sai da na ji numfashina ya Wauke na da™i™a.

"Salamu alaikum." 

Wata sassanyar murya mai yanayi da busar sarewa ta shiga kunnena, bayan sassanya ™amshin turarensa ya cika min rayuwa gaba Waya.  

"Ina wuni?." 

Na tsinci kaina da faWa har da dur™usawa, ya yi murmushi sannan ya ce.  

"Gidan can zan aiki ki." 

Ya faWa yana nuna min gida dake kallon namu, na juya na kalli gidan sannaan na ce. 

"Toh!" 

"Nan ne gidan Alhaji Hadi ko?"

Ya tambaya, ni kuwa jikina har Sari yake amsa tare da gyaWa kai. 

"Eyh! Nan ne." 

"Ki shiga ki ji yana nan? Idan yana nan ki ce masa Fahad Ta'ambo ne, wanda su ka zauna tare a jirgi daga Dubai zuwa Nigeriya, ya yi mantuwar ne a cikin jakata shine na zo kawo masa." 

Tun da ya fara magana gabana yake faWuwa har ya ™arashe. Yana gamawa kamar wacca aka umarta na fara tafiya, ban tsaya ba sai da na shiga gidan, bayan na isar da sa™on Alhaji Hadi ya ce dani yana zuwa, na dawo na faWa masa ya yi min godiya, amma maimakon na kama hanyar makarantar sai na dawo gida, gaba daya ji na nake wani sukuku, unguwar ta yi min faWi, ™amshi turarensa ne ka dai yake yawo a kwanyar kaina, sai kuma maganarsa tun daga farko hat karshe, ban manta ko kalma daya ba. 

"Ki shiga ki ji yana nan? Idan yana nan ki ce masa Fahad Ta'ambo ne, wanda su ka zauna tare a jirgi daga Dubai zuwa Nigeriya, ya yi mantuwar ne a cikin jakata shine na zo kawo masa." 

Abinda na fada kenan da safe bayan na buWe idona, da sauri na daki kaina tare da faWin. 

"Rawasiya wake-up, me yake damunki ne haka?" 

Mi™ewa na yi tare da nufar banWaki na wanke baki na na fito zuwa tsakar gida, sai da ™amshin turarensa har yanzu yana yawo a hancin na, 

yanayin da na ji jiya yana nan kamar yanzu yazo unguwar. 

Haka kwana daya ya wuce ina jin wannan yanayin a tare da ni, kwana na biyu ya wuce, sai da na yi sati sannan na ji yanayin ya fara raguwa, sai da na Wau tsawon wata guda ina fama, kafin manta amma kuma har lokacin kammaninsa da sunan sa suna nan a kwakwalwata, domin a kallo daya kwakwalwata ta dau™i hoton sa, wanda ya tsaya a a zuciya.

Ranar da Allah Ya nufa zan sake ganinsa ranar wata laraba da yamma, lokacin Hajiya ta aiki ni gidan wata ™awarta a fagoji, banson zuwa fagoji kwata kwata, ni ba ma fagoji ba gaba daya ban fiya son zuwa wani waje nesa ko kusa ba. Daidai bakin titin Rasheed shekoni special hospital mashin din da nake kai  ya tsaya, me mashin Win ya tsaya yana duba mashin Win ni kuma na sauka ina jiranshi.  

A jiki na naji ido na yawo a kaina baya ga matsananciyar faduwar gaba da naji. Ina kai idona bakin asibitin na ganshi tsaye ya harWe hannusa a ka faWa yana kallona. Da sauri na sunkuyar da kaina ™asa ina faWin. 

"Wayyo Allah." 

Dan wani irin ™arfaffan bugu zuciyata ta yi lokacin da muka haWa ido dashi. 

"Sannunki." 

Na ji muryarsa dab da ni sai dai na kasa Wagowa, idanuna suka kai kan ™afarsa, takalminsa ma kaWai abun tsayawa a kalla ne. 

"Kamar ke ce ta unguwarsu Alhaji Hadi ko?" 

Da sauri na gyaWa kai, tare da faWin. 

"Eyh! Ni ce." 

"Lol, me kike yi anan?" 

"Mashin ne ya sami matsala, amma gashinan ya gama dubawa." 

Ya kalli mashin din sannan ya kalli ni. 

"Kuma a wancan unguwar kike?" 

Ya faWa yana baya da hannu alamun can. Na gyaWa kai tare da cewa. 

"Eyh! Yalwawa." 

"Uhm! I see." 

Ya faWa yana shafa gashin bakinsa daga tsakiya zuwa gefe sannan ya ja shi zuwa ™asa. 

"Mu tafi ko?" 

Mai mashin Win ya faWa, na juya zan hau mashin Win sai na ji ya ce. 

"Na ce ki tafi?" 

Ba shiri na tsaya kaina a ™asa. 

"You're eager to go, kin gaji ko?"

Ya faWa cikin wani irin yanayi na fushi, da sauri na girgiza kai sannan na ce. 

"A'a, bangaji ba.... Me mashin Win." 

Kallon me masahin Win ya yi sannan ya ce. 

"Malam ka jira." 

"Alhaji sana'a fa nake, idan na ajiyeta wasu zan Wauka." 

Hannu Ya sa a aljihu ya zari kuWi 'yan dubu dubu da a ™alla sun kai guda goma ko sha, ya mi™a masa. Ba shiri me mashin Win ya amsa tare da matsawa gefe ya zauna, a raina na ce. 

'Yanzu mu dai babu yaren da muke ganewa sai na kuWi." 

"So ba zaki tambayi sunana ba?." 

Ya faWa yana kafe ni da idanun da nake jin su tamkar na zaki sabida kaifi. 

"Ka yi hakuri ai naga ranan ka faWa min." 

"Ni... when?" 

"Da ka ce na cewa Alhaji Hadi Fahad Ta'ambo ne." 

Shiru ya yi yana kallona na kusan minti biyar sannan ya ce. 

"So kin ma ri™e sunana, shine da kika ganni kika yi kamar baki sanni ba ko? Na gode." 

"Ba haka ba ne, ban kula da kai ba." 

Na faWa murya ™asa ™asa. 

"Amma ni na kula da ke?" 

"Ka yi ha™uri." 

"It's fine, you can go. Na gode." 

Shiru kamar an shuka ni a wajen na kasa matsawa. 

"You can go fa." 

"Ka yi ha™uri." 

"Kije kawai." 

Ya faWa yana barin wajen, sai da ya shiga cikin motarsa sannan na iya matsawa zuwa ga mai mashin Win, ya Wauke ni muka ci gaba da tafiya. 

Gaba Waya hankali na ba yaga hanya, na tafi tunanin wannan mutumin, komai na shi burgeni yake, ya iya magana. Amma abinda ya bani mamaki shine kwata kwata banji ya tambaye ni sunana ba, ko da yake mene ala™arshi da sunana da zai tambaya, kamar daga sama na ji ana cewa. 

"Mun kusa wuce jakshon Win fa." 
Chapter 7 · 0% Book details