← Book details Sartse Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 28 OF 39

Sashe 28

Sartse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Ka yi ha™uri, komai ya yi tsanani sau™i yana tafe, a yanzu na yi tunani kuma na fitar da wata shawara da nake ganin kamar ita ce mafita Hon." 

"Mecece? faWamin dan Allah." 

"Hon, rayuwa tana bamu zaSi da dama, wani abun da muka tsara da kanmu, wasu kuma sukan afku ba tare da muntsara su ba, kamar yadda bamu taSa tsara zamu san juna ba kafin nan, haka bamu taSa tsara zamanmu zai zo da wata tangarWa ba bayan munsan juna, Honey ubangiji ne ya dasamin sonka a zuciyata, na yi imani da Allah na yi imani da soyayyar da kake min Hon, dan haka ni dai a ganina kawai ™ara auren ne mafita agaremu dukkanmu. Duk son da nake yi maka, duk ™aunar da nake yi miki ba ta da wani amfani a ranar da narasa ka, a ranar da nazama ba mallakinka ba, duk wata iriyar soyayyarka da nake ji ba ta wata rana. Idan har ina son ka me zai sa ba zan so ma farin ciki ba? Me zai sa bazan so ma ladan biyayya ga iyaye ba? Menene wata riba a duniya da ta wuce ta biyayya ga iyaye Sardauna?" 

"Nana wai kina nufin kema kin amince na ™ara aure?"

Wani irin zafi nake ji a zuciyata a duk lokacin da Sardauna ya ambaci ™ara aure, amma ya zanyi ™addara ta riga fata, dole ne na goyi bayansa akan yiwa iyayensa biyayya. 

"Na goyi bayan ka yi biyayya ne Sardauna, domin kasami rabauta da tsira a duniya." 

"Nana bazan iya ba, bazan iya ba, bazan iya ba wallahi, na yi miki kishiya fa Nana, wa zan aura to? Wa nasani ma bayan ke?" 

"Ka duba zaka samu in sha Allah." 

"Cikani." 

Ya faWa yana ™o™arin mi™ewa. 

"Ka fahimce ni dan Allah, idan fa baka yi auren ba rasani zaka yi, zasu ce ka sake ni." 

"Nana su faWa, ai ba lallai ba ne na yi musu biyayya." 

"A'a Sardauna, idan ka neman albarka dole ka yi wa iyayenka biyayya, ni dai ka fahimce ni." 

"Nana kenan, wace kalal fahimta zan miki? Zancen ki anan babu abinda yake nunawa sai zallar rashi Kishina, Nana kalamanki tsaf zasu yi wa zuciyata Sartse mai raWaWi." 

Kuka ne ya ci ™arfina, ni a yanzu ai angama yi wa zuciyata Sartse gaba Waya, domin duk lokacin da na ji a raina wai Sardauna zai ™ara aure sai na ji wani raWaWi daga cikin zuciyata mai haWe da ya ji, amma yana iya? Dole na so farin cikin mijina sama da komai a wannan rayuwar. 

"Ka yi ha™uri Sardauna." 

Na faWa ina jawo shi jikina, ya rungume ni iya ™arfinsa kamar zai mayar da ni jikinsa, ina jin yadda yake shashe™ar kuka. 

"Ka yi ha™uri ka ji."

"Ya zanyi Nana?" 

"Ka yi tunani ta ina ka haWu da ni, har ka tun kare ni, nasan zaka samu zaka samu wacca zaka iya aura." 

"Nana bana so su bani a dangi, bana so su ce na rabu dake Nana, bazan iya ba." 

"A waje zaka samu." 

"Hhhm, Nana kenan." 

*******

Har dare Sardauna ya kasa fahimta ta, ya kasa fahimtar inda zance na yake son nufa, a haka muka ha™ura mu ka kwanata, sai dai fa ni bacci ya™i zuwa idona, tunani nake anya zan iya kasadar barin wata kusa da Sardauna, babban abinda yafi bani mamaki, ban ji mahaukacin zafi a cikin zuciyata ba akan zancen ™arin auren, zafin da fi ji shine na rabuwa da ni, ko dan maganar sake ta shigo ita ce ta cire min raWaWin kishin? Amma kwata kwata ban ji ina mugun kishi ba, ko a baya ma bana iya tuna kishin da na yi akan Sardauna ba. 

˜arfe uku na dare na tashi, bayan na yi nafila raka'a biyu na yi addu'o sosai, sannan na dawo na kwanta, sai a lokacin bacci ya Wauke ni. 

Washe gari ma haka muka tashi da Sardauna yanayin babj daWi, na yi masa bayani yafi sau cikin carbi amma amsa Waya yake ba ni. 

"Honey bazan iya ba, Honey ban da ita." 

Ya koma kamar wani ™aramin yaro ba abinda yake iya ganewa, abinda ya ™aramin tausayin Sardauna kenan, gaba Waya ji nake duk ni ce na ja masa komai ma, ko kuma na ji dama akaina waWannnan abubuwan suke faruwa ba akan Sardauna ba, domin duk damuwar sardauna guda Waya, sau dubu nake jinta a zuciyata. 

Legendspen

08129553971

*SARTSE*

-Amanar-Janafty-

*Sayyid Legendspen*

MAH/2026/001

Sadaukarwa.

RAMLAT ABDULRAHMAN MANGA

(Mai Dambu) 

Shafi na ashirin da Waya.

    (21)

Da ™yar na iya lallaSa Sardauna ya fita ofis, amma da ya ce wai bazai iya fita ba sabida kowa ya ganshi zai san yana cikin damuwa. Sai da na yi masa daWin baki sosai na nuna masa babu wanda zai gane yana cikin damuwa, sannan ya fita. 

Tun bayan tafiyar Sardauna na shiga aikina na kullum, amma sai dai na yau zuciyata tafi nuna min wa Sardauna zai aura, wani irin zama zamuyi shin zai so ta kamar yadda ya so ni, ko ma zaifi sonta, za ta yi masa biyayya irin yadda nake yi? Ko za tafi ni? Dole fa na dinga raba mata kwana da Sardauna, duk da hakan bai dameni ba amma tabbas ina jin ba daWi. 

Har yamma ina ta faman tunani, da kuma tsoron me Sardauna zai dawo da shi, zai sami matar ne ko sai gobe?

"Ya Allah ka sa wannan auren ya zama ™arshen duk wata wahala, da wani tashin hankali." 

Knocking na ji ana yi min, na tashi a raina ina addu'ar Allah Ya sa Bilkisu ce, sai ina buWewa na ga Turaki. 

"Ina wuni?" 

"Lafiya ™alau Nana." 

Ya faWa yana kallona, ganin shirun ya yi yawa na ce. 

"Bayan nan." 

"Nana komai lafiya a gidanki?" 

"Lafiya ™alau." 

"Kinje wajensu Hajiya?" 

"Na je." 

"Amma Ra'is ya ce kin fi watanni baki je ba, me ya sa?" 

"Ina zuwa." 

"Nana yakamata kije ki yi magana da Hajiya, ki faWa mata duk wata matsala da take damunki." 

Yana faWin haka ya juya ya shige Sangarensa, haka na dawo ciki duk jikina babu daWi, ni shikenan kullum rayuwata a babu daWi, zaman ba daWi, gidan ba daWi, ni narasa wace irin rayuwar aure ma nake yi. 

Waya ta na Wauka na kira Hajiya, na yi sa'a kira Waya ta Wauka. Bayan mun gaisa nake ce mata bani da lafiya ne kwana biyu. 

"Me yake damunki?" 

"Hajiya na yi Sari ne."

"Allah Ya ™ara lafiya."

"Amin Hajiya, ya mutan gidan?" 

"Nana kowa yana lafiya, Ra'is ya ce kun yu waya kwanaki, Nana duk wanda na ce ya zo gidanki sai ya ce bazai zo ba mijinki, sai  da wancan Wan Albarkan Turaki ya zo na yi masa magana, nasan yanzu ma shi ya yi miki magana ko?" 

"Eyh Hajiya shine." 

"Nana ki dinga addu'a kin ji." 

"In sha Allah Hajiya." 

*****

Wayar da na yi da Hajiya ta rage min wani abu daga cikin damuwar da nake ciki, yamma lis sai ga Bilkisu ta zo itama a kiWime, al'amarin mahaifinta ya ta azzara akan auren da ya ce  zai yi mata. 

Itama gaba Waya ta yi wani sukuku, ta fita hayyacinta. 

"Bilkisu to ke ki duba cikin masu zuwa wajenki mana."

Na faWa dan dai nasan Bilkisu ba zata taSa rasa masu zuwa wajenta ba, domin dai tana da kyanta yadda yakamata, ga ilimi kuma yar gayu ce sosai da sosai. 

"Nana bazaki gane ba kwata kwata, duk masu zuwa wajena ba na aure ba ne, burinsu na basu haWin kai su Sarar mun da mutunci su cuceni."

"Ya salam, Allah Ya tsare ki."

"Amin amin, ku yanzu kun sami matsaya?" 

"Eyh mun samu, aure kawai Sardauna zai ™ara kamar yadda suka umarta."

"Allah Sarki Nana gaskiyya kinyi namijin ™o™ari Allah Ya baki haihuwar nan." 

"Amin Bilkisu, Allah Ya kawo miki mafita." 

Itama ta ce Amin, nan muka zauna kowa na jajantawa kowa har Sardauna ya dawo ya sameta, sai bayan ya dawo ta tafi. 

A yanayin Sardauna na yau dai babu wata sabuwar matsalal, kuma na ji daWin hakan sosai da sosai, haka washe gari ma babu wata matsalal. Al'amuran kamar sun sau™a™a wajen kwana biyar, sai ranar kwana na huWu Sardauna ya dawo cikin tashin hankali, Hajiyarsa ta ce lallai lallai ya sake ni idan har bai fito da mata ba cikin kwana biyu, a kiWime na ce. 

"To baka ce musu kana dubawa ba ne?" 

"Nana wa zan duba, har yanzu fa ban ga wata da na ji zan iya haWa ta dake ba, Nana mata basu da kama ko kaWan, bazan iya auren wacca zata hula™anta ki ba ko kaWan Nana." 

"Kar ka damu Sardauna, ni zan iya zama da kowace muddin kana nan kuma kana ganina a matsayin da kake ganina yanzu, Sardauna ka auri duk wacca ta yi maka." 

"Nana anya kuwa kina kishi na?" 

Kallonshi na yi, sannan na kalli ™asa. 

"Tayar maka da hankali shine kishi? Sardauna indai sai na Waga maka hankali na saka a damuwa bayan wacca kake ciki shine kishi to ni bana kishi, hasali ma babu zuciya a tare da ni, ina sonka a kowanne irin hali, zan ci gaba da sonka a kowanne irin yanayi Sardauna." 

"Nana bana jin zan iya neman wacca zan aura, ina neman alfarma a wajenki guda Waya dan Allah." 

Ya faWa yan goge ™wallar da take idonsa, bai bari na yi magana ba ya tsugguna a gabana, tare da ri™e min hannuna. 

"Nana! Dan Allah, dan girman ma'aiki ki ta ya ni duba wacca zan aura, Nana kowa kika kawo indai kin aminta da ita to zan aura Nana, dan ke zan yi auren kuma ina so ki nema min waccan zan aura da kanki da hannunki Nana." 

Wani irin nauyi na ji ya danne ni kamar an Wauramin gungumen dutse. Tabbas wannan alfarmar da Sardauna ya nema a wajena da girma take, ta ina zan fara? 

"Nana dan Allah, mutuncina da darajata duk suna hannunki a yanzu ki tallafa min Nana." 

"Ka tashi zaune dan Allah." 

"Nana ki yi min wannan alfarmar dan Allah." 

"Tom na yi ka tashi zaune ka ji."

"Na gode Nana."

Ya faWa tare da zama kan kujerar, ya ™ureni da ido sannan ya ce. 

"Nana!" 

"Na'am." 
Chapter 28 · 0% Book details