← Book details Sartse Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 16 OF 39

Sashe 16

Sartse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Baice ka gaisheni ba? Shi fa bai taSa zuwa ba. Kuma ya je duk  gidansu Yaya Radiya." 

"To ai su yayunsa ne, ke kuma ™anwarsa ce. Yaya Radiya ma tana gida." 

"Zuwa ta yi?"

"Eyh, ta kwana biyu ma." 

"Tafiya mijin na ta ya yi?" 

"A'a saSani suka samu da shi, wai yana da wata matar a waje." 

"Mata a waje? Yau she ya yi auren ba mu sani ba?" 

"Bawai matar aure ba, abokiyar iskanci." 

Kama baki na yi sannan na ce. "Lallai chaS."

"Jiya kuma Hajja ta zo ta sauke kwandon rashin mutuncinta tsaf a gidan." 

"Da aka yi mata me? Ita kuma."

"Wai ai Yaya ce ba tasan mene darajar miji ba shi ya sa ya fita ya nemi wata." 

Na yi matu™ar mamakin jin wannan abun, ko da yake a son zuciya irin na Hajja inda za a bata kuWi ta bata™i ko kisa aka yi ba ta ce, wanda ya mutum shi ya taso ya kashe wanda ya yi kisan.

"Ita ta sani, yanzu mai Alhaji ya ce?" 

"Ita Yaya ta ce ba zata koma ba, haka kawai ya kwaso wata cutar ya goga mata." 

"Wallahi Allah da gaskiyyarta, kuma ko ya ce zai daina ba lallai ya daina ba tun da daman ba mutunci ne da shi ba." 

Na faWa daman ni tun da ba gaisawa ma muke da shi ba. 

"Haka Yaya Ridwan ya faWa, ya ce ko kotu ne sai anje an raba auren." 

"Uhm, ni kaWai ce Yaya Ridwan ba ya so." 

Kallona Ra'is ya yi sannan ya ce. 

"Waya faWa miki haka?" 

"Ra'is alamunsa na gani, kana ganin ko Allah Ya sanya alheri bai yi min ba, kai ko gidana bai taSa zuwa ba, farkon aure na da na kirashi da ya Waga ya ji ni ce sai ya katse." 

"Kinsan halinsa dai." 

Ra'is ya faWa yana mi™ewa. "Ni zan tafi." 

"Tsaya na baka abu ka kaiwa Hajiya."

Na faWa ina shigewa Waki, na Wauko wata leda da daman na ajiyeya na ba shi ya tafi sannan shima na bashi dubu bakwai, wanda shine kuWina gaba Waya. 

Ko da Sardauna ya dawo sai da ya tambayeni waye ya zo? Na yi mamaki sosai na yadda akayi ya sani, shi ba camera ce da shi ba amma ya sani, ko da na ce masa Ra'is ne bai wani saki fuska ba. Bayan ya ci abinci na Wauko masa takardar da Ra'is Win ya ciro ya kawo min, buWar bakinsa sai cewa ya yi. 

"Kun dage dai sai kin yi karatun ko?" 

"Alhaji yana so kasani kaima." 

"Uhm." 

Ya faWa ya ci gaba da danna wayarsa, ni kuma na zauna ina wasa da ™afarsa. Sai da aka kwana biyar da maganar sannan Sardauna ya kai ni wajen Rijsitar jamb, shima sai da na sake masa magana sannan ya kai ni. 

Masu kuWi basu da al'adar zuwa gidan mutane, amma kuma suna da kirki idan anje musu, duk ranar da mukaje gidan Hajiyarsu kamar zata cinye ni sabida kulawa ita da ™annensa, haka idan na kiranta a waya shima kamar zata goyani, duk mutan gidansu suna sona sosai idan na je musu, sau Waya ™anwarsa Lubna ta zo shima daga lectures ta dawo shine ta biyo. 

Haka lokacin zana jarabarwar Jamb ya zo Sardauna ya kai ni na yi, idan na sami maki 189 na ji daWi sosai domin zan sami Addmission a FUD, haka a gida kowa ya ji daWi ya yi murna. 

A lamarin Yaya Radiya kam, ta dage ba zata koma ba, haka Yaya Ridwan ma domin sun binciko asali ba iya wannan abun ba ne ya baro ta gidan, bayan neman mata harda shaye shaye yake yi, shima dalilin da ya sa su ka gano wata rana ne yazo gidan namu a buge ya yi wa musu tijara da hau na ™arshe, ya ci musu mutunci sai da Ra'is da Yaya Ridwan suka fita dashi. Amma da Hajja ta zo yin ta ta tijirar sai cewa ta yi an dake shi an ji masa rauni. A yanzu Alhaji ya daina damuwa da abubuwan Hajja tsakanin shi da ita sai dai tom, amma ya faWa mata a wannan maganar ba yadda ya iya tun da yarinya da 'yan uwanta sun dage akan ba zata koma ba. Sardauna ya Wan san maganar tsilli tsilli ban saki jiki na faWa mai komai ba, tun da naga kamar bai son maganar. Da kan sa ya kaini gidan Anty Adiza har sau biyu a cewarsa duk ranar da na je ina samu sabon ilimin sarrafa fulawa. 

Kwance ta shi ba wuya a wajen Allah har aka zo lokacin da jami'a ta fara raba Addmission, kuma ina cikin mutanen da suka samu a lokacin farko. Alhaji bai taSa zuwa gidana ba sai a lokacin ya zo ya yi wa Sardauna godiya akai, daga nan na fara shirye shiryen makaranta sai dai har zuwa wannan lokacin babu ciki a jikina, tun ina Soyewa har abim ya fara damuna, har na fara sanar da Sardauna amma sai ya ce shi haka yake so, da ya ga dai na fara damuwa da al'amarin bisa ga auren Malaika da akayi bayan namu, ta tafi jihar kano kuma a yanzu ta sanar da ni cikinta ya shiga watan haihuwa. Hakan ya sa na sake damuwa, sai shima ya fara nuna damuwarsa, yake kuma kwantar min da hankali. Da dai ya ga abun namu ba ™arami ba ne sai ya ce na shirya zai kai ni naga likita. Rasheed shekoni special hospital ya kaini, asibiti da na yi ma sa gani na biyu a rayuwata, lokacin da mai mashin ya tsaya gyara. Kai tsahe wajem likitan muka je wanda daga yanayinsu kasan abokinsa sa ne, bayan ya yi masa bayani likitan ya sa na kwanta akan wani gado anan ya yi dube duben da zai yi sannan ya ce na koma na zauna. 

Kusan mintina goma sha biyar, sannan ya fara bayani. "Madam mahaifar ta yi ™an™anta ne da Waukan ciki, amma kuma yau da gobe ya sa ta fara girma, idan kika yi ha™uri kuma kin zuwa ganin likita in sha Allah za ta buWe." 

"To wane magani za'a ba ni." 

"A'a babu magani fa." 

"A'a a bata wannan pils din mana." 

Sardauna ya faWa, wani kallo na ga Dr ya yi masa sannan ya ce. 

"Ai zai yi mata ™arfi, sai dai a dinga ba ta sha sau daya ko biyu a wata." 

"Eyh hakan ma ya yi." 

Sardauna ya faWa, sannan ya dafa ni yana faWin. 

"Nana ki daina damuwa kin ji ko, rashim haihuwar ba matsala ba ne." 

Na gyaWa masa kai, sannan ya ce. 

"Ki jirani a mota." 

Na mi™e na fice na barsu a cikin ofis Win, ina fitowa waya ta ta hau ruri, ina dubawa na ga sunan Ra'is na Waga da faWin. 

"Ra'is ya aka yi?" 

"An raba auren Yaya Radiya fa." 

Gaba Waya sai na ji wani iri, Allah ya gani ina matu™ar tsoron mutuwar aure a rayuwata. 

"Yaushe?" 

"Shekaran jiya Hajiyarsa ta zo ta yi wa Hajiya rashin arzi™i. Yaya Ridwan ya sa 'yan sanda suka kamata, amma a ranar aka sake ta shine Wazu ya aiko da takardar." 

"Ka ce tashin hankali aka yi kenan? Allah Ya tsare gaba zan shigo in sha Allah." 

"Amin amin, ya shirin makaranta?" 

"Ranar monday zamu fara lectures." 

"Allah Ya sa albarka." 

"Amin amin." 

Daga haka na katse wayar na shiga mota na jira Sardauna, sai da ya Wau wajen mintina ashirin sannan ya fito, a hanya nake sanar da shi mutuwar auren Yaya Radiya, ya tausaya har muka koma gida. 

Ranar Monday ranar da zan fara lectures Sardauna ya tashi baya jindaWi kwata kwata, ta dole na ha™ura da makarantar ban je, sabida bai samu kansa ba sai wajen sha biyu na rana. Haka washe gari ma ya tashi da irin ciwon, gaba Waya na ruWe kamar shafar aljanu, duk asuba idan ya fara juye juye bai nutsuwa sai rana ta fito, kusan sati biyu a haka, ta dole na ha™ura da makarantar sabida lafiyar mijina tafi min komai a duniya, har da ni kaina. 

Legendspen

08129553971.

*SARTSE*

-Amanar-Janafty-

*Sayyid Legendspen*

MAH/2026/001

Sadaukarwa.

RAMLAT ABDULRAHMAN MANGA

(Mai Dambu) 

Shafi na sha biyu.

    (12)

Abu kamar wasa ciwon Sardauna yana ta tsananta har lectures Win mu ta yi nisa, tun da ina bibiyar al amarin makarantar ta waya har wasu malaman suna shirn fara yin test. 

Tun ban damu da lamarin makarantar ba har na fara damuwa, mussaman da Baba ya kan kirani ya ce min ya karatu, gashi har Ra is ya aiko ya kawo min dubu ashirin wai na ™ara kuWin makaranata kar a bar mijina da wahala, ranar har da ™wallata, da Sardauna ya dawo na yi masa maganar sai ya ce da ni, lafiyarsa zan sa a gaba sama da komai, daga ba ya na ce masa ai har lectures Win 12 muna yi har 2 wata ma 4 ce dan haka idan ya fita zan iya zuwa, ya daWe yana kallona kafin ya ce ya amince. 

Daga nan na fara zuwa, amma duk wata lectures ta ™arfe takwas ko goma babu ni a ciki, cikin ikon Allah kuma ciwon na shi ya fara baya daga nan na samo damar hallartar ta ™arfe goma amma dai banda ta takwas. Tabbas yanayin makarantar ta burgeni, kuma ina jindaWin zuwa makarantar sannan na mayar da hankali akan karatun sosai, dan dana ta shi cikin masu ™o™arin ajin na shiga ana damawa da ni. 
Chapter 16 · 0% Book details