← Book details Sartse Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 26 OF 39

Sashe 26

Sartse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Lallai Nana, ke kenan bamu da amfani sai matsala ta taso tsakaninki da mijinki shine mule da rana, ba kyajin kunya sai ki tunkare mu idan kuma kuna cikin soyayya babu 'yan iska sama damu ko? To wallahi kisani babu wanda zai ™ara shiga al'amuranki tsakaninki da mijinki tun da kin zaSi mutumin da ya haWu dake ta ha™waranki talatin da uku, kin bar wacca ta raini ki a cikinta har kika fito duniya, ta yi Wawainiya dake, kin bar wayanda suka raine ki, su ka so ki, su ka bakk farin ciki, su ka tsoraci kukanki Nana, duk akan wani mutumi guda Waya, ki je rayuwar duniya ce." 

Yana gama magana ya kashe wayarsa, kuka na fashe da shi, tabbas nasan maganarsa gaskiyya ce, kuma ya faWa min abinea nake bu™atar a tinasar da ni, amma ya zanyi da Sardauna Allan da ya hallice ni shi ya sanya mini soyayyarsa. 

Daga wannan lokacin na ™udiri aniyar bazan sake kiran kowa a gidanmu akan damuwa ba sai dak gaisuwa kawai. 

Bayan sati biyu. 

Tun lokacin da maganar nan ta fito gidanmu ya canja daga gidan farin ciki zuwa damuwa, daga gidan walwala zuwa na ™unci, babu wani abu Sai daWi a gidan, kullum muna neman mafita amna ta™i samuwa, ta Sangaren gida kullum Sardauna matsanta masa ake yi, an hana shi sakat. A yanzu Sardauna har baya son zuwa gidan Hajiyarsu ko Family House, kullum daga gida sai Majalisa yanzu ma da mota yake fita majalisar, ni kam bana iya komai banda tunanin mafita. A ko yaushe cikin sa™e sa™e nake, na yi ba™i na rame gaba Waya na fita hayyacina. 

Gashi Bilkisu ba ta sake zuwa ba, tun ranar da na faWa mata matsalal ta ce zata zo a cikin satin, idan ma na kira ta sai ta ce ba ta gari ma baki Waya.  Jiya da muka haWu da Turaki sai da ya tsareni da tambayar me yake damuna, me ya faru tsakanina da Sardauna, amma na ce da shi komai lafiya. Daga ™arshe ma ya fara yi min nasihohi masu ratsa zuciya akam ha™uri da rayuwar aure, sannan ya dinga jaddadamin na dinga yi wa mijina biyayya, har sai da na yi mamakin me ya sa ya yi haka.

Da na dawo Waki ma na yi ta faman tunani maganganun Turaki me suke nufi, yanayin maganar kaman faWa da nasiha yake min daga baya kuma ya dawo shawara. 

"Allah Ya sa alheri ne." 

Na faWa, sai kuma can na yi tunanin ko akan maganar da ta Sullo ne ta haihuwa shi ya sa. 

"Innullahi wa'inna illahir raji'un, ya zan yi ni Nana?"

Na tambaye kaina tare da fashewa da kuka, sai da na yi mai isata na ta shi na shiga Waki, zaman gidanma ya isheni tun da na zo gidan ban taSa fita ba ko sau Waya, a yanzu an kai wata uku zuwa huWu amma ban taSa fita ba ko gida ban je ba. 

Kwanciya na yi akan gadon na shiga tunanin rayuwa, da irin abubuwan da Sardauna ya saukar akaina, gashi kuma yana ™ara fuskantar wasu. 

"Lallai Sardauna ya cika sadauki, Allah Ka ™ara mai lafiya da arzi™i, Allah Ka ™arawa Sardaunana ha™uri da juriya akan abubuwanda suke tun karoshi, Allah Ka sani ina son bawan nan naka, Allah Ka so shi, ka yarda da shi, ka amince masa akan duk abinda ya sa gaba." 

Cikin ikon Allah wani bacci ya Waukeni, wanda kiran sallar magariba ne ya tayar da ni, ina tashi na Waura alwala na yi sallah, dan yanzu Sarduna a waje yake magariba, idan aka yi isha kuma ya fita, tara da rabi zuwa goma yake dawowa. 

Ina idar da sallah na shiga haWa masa abinci akan dinning, ina cikin haWawa ya shigo, fuskarsa kamar kullum amma yau ma tafi raunana, ajiye abinda nake na yi tare da tawowa inda yake. 

"Sannu da zuwa Mijina." 

"Yawwa Nana." 

"Ya ofis?"

"Nana rayuwa babu daWi, abubuwa duk sun kacame." 

"Innullahi wa inna illahir raji'un, me aka sake cewa kuma?" 

"Mene ma ba a ce ba Nana, mene ba a ce ba? Kinsan yau kwanakin da Big Daddy yaban zasu ™are gashi babu wata mafita da muka samu." 

"Ya baka kwanaki ne?" 

Na tambaya cike da mamaki, ya gyaWa kai kusan minti biyar sannan ya ce. 

"Big Daddy ya ban 10days akan na fitar da mafita, na ce ya ™ara min zuwa sati biyu to kinga yau anyi sati biyun." 

Hawaye na ji suna gangaromin a fuskata, da sauri na gogesu sabida kar Sardauna ya gani, ni da zan ™arfafa masa gwiwa bai kamata na raunana ba. 

"Nana bansan abinda Big Daddy zai ce ba." 

"Ni kaina kwana biyu na dage da addu'a sosai da sosai, abinda nake gudu kenan tun farko akan rashin haihuwar nan ka ce kai ba komai, yanzu ga shi komai ya juye." 

"Nana ni kaina matsamin aka yi a gida, shi ya sa kuma wallahi nauyinki nake ji Nana, ina jin kunyar yi miki magana akan haihuwa Nana." 

"Nasani, duk wannan matsi da takurar da muka shiga akan haihuwa ba ra ayinka ba ne, na kasance me yi maka uziri a ko yaushe Sardauna, ina sonka son da na yarda da kai fiye da kowa fiye da komai, na yi imanin har abada ba zaka taSa cutar da zuciyata ba Sardauna." 

Na kama hannunsa, ya Wago ya kalle ni. Idanuwansa fal da damuwar da ta dame ni. 

"A ko da yaushe ina mi™awa ubangiji Amanarka Sardauna, ina mi™awa Allah ragamar kula da kai, nasani Allah zai amss addu'a ta, ba zai taSa Woramin abinda zaifi ™arfinka ba, a ko da yaushe ina sonka zan kasance mai sonka Sardauna har numfashi na ™arshe."

Ji na yi ya jawo ni jikinsa ya rugumeni tare da faWin. 

"Nana, bani da wata kalma guda Waya da zan iya godewa kan alherin soyayyarki agareni, Nana nasami damarmaki masu yawa sanadiyar soyayyarki, na gode Nana, nima ina sonki."

Haka mu ka yi ta lallaSar juna, ina ™ara nunawa Sardauna girman soyayyarsa a zuciyata, har na samu ya ci abinci ya shirya ya fita Majalisa.  Sai goma ya dawo gida, ina nan inda ya barni ina ta faman sa™e sa™e dan yanzu babu abinda na ™ware da shi kamar damuwa, ina sa™a wancan na since wancan. 

"Honey baki yi bacci ba?" 

Ya faWa yana zama. 

"Ban yi ba tukunna, har ka dawo?"

"Eyh na dawo Honey, kin ga."

Ya faWa yana buWe ledar da ya shigo ita, kwalin wayar iphone, ya mi™omin. 

"Nana take." 

Na sa hannu na amsa ina mai jindaWi. 

"BuWe mana." 

Na fara kici kicin buWewa, iphone 16normal ce pink kala mai kyau. 

"Na gode sosai mijina, Allah Ya ™ara arzi™i lafiya da wadata." 

"Amin My love." 

Ya faWa tare da Waukana zuwa Waki. 

Washe gari Sardauna bai fita ko ina ba, muna gida gashi ba weekend ba, da na tambayeshi sai ya ce. 

"Bana som fita ofis, zan haWu da Big Daddy. Kuma kinga yau kwana goma sha huWu ta cika." 

Kamo hannunsa na yi, sannan na ce. 

"Wane irim hukunci kake tunani kake tunanin zai yanke?" 

"Nima bansani ba, amma bana son ya bani hukunci mai tsauri Nana." 

"Duk tsaurinsa bai zai yanke ma hukuncin da zaka rasa rayuwarka ba, Sardauna nasan ba zai yanke ma hukuncin da zai cutar da lafiyarka ba, to ina ganin duk wani hukunci da ya biyo bayan wannan mao sau™i ne a wajena da kai, ni zan ta ya ka karSar kowanne irim hukunci ne Mijina." 

"Na gode Nana, Na gode amma bana son wani hukunci da zai cutar da rayuwarmu, ko wani hukunci da zai sa mu yi abinda ba zamu ji daWi ba, Nana ke nake so ke kaWai a duniya, ban damu da 'ya'ya ko rashin su ba Nana, amma tabbas ina jin ba daWi idan na ga Hajiya ta a cikin halin damuwa, na kan ji zafi idan na ga Alhajina a cikin damuwa, duk akan yara." 

"A kullum kaine mai cemin haihuwa da rashinta duk na Allah ne, akan wannan na tashi, akan shi na Waura yarda ta, kuma nasan suma sun san da haka, dan haka nasan ba zasu yanke maka hukuncin da zaka kasa Wauka ba." 

"Nana ki yi ha™uri, na yi miki laifi mai girma." 

A tsorace na ce. 

"Wane irin laifi kuma?"

"Nana, na sanar da Hajiya asalin matsalal rashin haihuwarmu, a tunani za ta fahimta ko ta yi mana uziri, kuma nasan ta sanar da Big Daddy." 

Shiru na yi na rasa me zance, yanzu tun da sun san matsalal daga wajena ne zasu iya cewa ya sakeni? A fili na furta. 

"Innullahi wa inna illahir raji'un." 

"Nana calm down kin ji, ko mai zai zo da sau™i, kece mai faWin haka." 

Gaba Waya na tsorata idan babu Sardauna ina zan sa rayuwata ni Nana, ina zan kalla na ji daWi, ta ina zan iya numfashi bayan babi Sardauna a kusa da ni, na shiga uku ni Nana. 

"Ki nutsu ba zasu yanke hukunci mai kamar wanda kike tunani ba in sha Allah." 

Cikin muryar kuka na fara magana. 

"Wallahi cewa zasu yi ka sake ni wallahi, me ya sa  ka faWa musu haka?" 

"Nana baza su ce haka ba kwata kwata, in sha Allahu."

"Sardauna." 

Na faWa tare da tsugunnawa a ™asa.

"Na'am Nana." 

"Dan Allah, dan Annabi da girman iyayenka Sardauna kar ka sake ni, ko mene zai faru, wallahi ina sonka, ina sonka ban da wanda nake so bayan kai, Sardauna idan ka rabu dani bani da wata rana a rayuwata, ka yi min al™wari dan Allah." 

"Tashi Nana, tashi ki zauna." 

Ya faWa yana kamoni na zauna. 

"Nana, ina sonki fiye da yadda kike tunani, na yi ya™i mai girma kafin na aureki, sabida haka zan yi wani ya™in akan na rayu da ke." 

"Tabbas Sardauna idan ba kai ni gawa ce." 

"Nasani Nana." 

"Sardauna kai ne dalilin da yasa nake numfashi, Sardauna kai ne dalilin da murmushi yakw fitowa a fuskata, ka tausayamin dan Allah." 

Rumgume ni Sardauna ya yi sannan ya ce.
Chapter 26 · 0% Book details