← Book details Sartse Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 36 OF 39

Sashe 36

Sartse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Wallahi Abubukar yau sai na raba hannunka da gangar jikinka, ka buWe na faWa maka.  

Can ta wajen window Turaki ya ™ara le™owa.

Ga fuskarta mai kyau, ta iya murmushi.  

Da gudu Sardauna ya dawo wajen tagar, yana faWin.

Abubakar zakaci kutumar ubanka wallahi, karuwa Wan iska, me bin matan mutane.  

Matarka dai akwai kyau ma sha Allah.

Turaki ya faWa daga wajen ™ofa, ni dai ina daga tsaye, na fuskanci Turaki dai haukata Sardauna yake son yi, kamar daga sama na ji yana cewa. 

Uban me kike yi anan? Sai na zo na SaSSallaki, shashasha.  

Ba shiri na shige ciki, ya yo kaina yana faWin. 

Wato Nana ke baki da hankali ko? Da zaki shiga motar wani namiji da ba mijinki ba, Nana ko yayanki uwa Waya uba Waya ai bazaki shiga mota tare da shi ba, shine zaki shiga da wancan ™asurgumin Wan iskan ko? Wallahi Nana yau sai kinji a jikinki.  

Legendspen

08129553971

*SARTSE*

-Amanar-Janafty-

*Sayyid Legendspen*

MAH/2026/001

Sadaukarwa.

RAMLAT ABDULRAHMAN MANGA

(Mai Dambu) 

Shafi na ashirin da bakwai.

    (27)

Ina shiga ciki na yi cikin Wakina na kulle ™ofa nasa Sakata, yadda yake wannan saman ai tsaf ya kamani sai ya Sallani. 

"Nana buWe min ™ofa." 

"Ka yi ha™uri dan Allah." 

"Na ce ki buWen ™ofa zaki zauna kina cewa na yi ha™uri?"

"Karka dake ni dan Allah." 

"Bazaki buWe min ba Nana, na buWe da kaina sai na SaSSallaki." 

Ba shiri na taso na buWe ™ofar, na ma™ale a jikin bango. Da iya ™arfin shi ya kamo hannuna ya matse shi sosai, idanunsa har wani haya™i ne yake fitowa daga cikinsu. 

"Nana! Nana! Nana! Me ya sa kika shiga motar Wan iskan can? Me ya sa ?" 

"Bakomai ka yi ha™uri dan Allah."

"Har wani murmushi kika yi masa? Har ™amshin turaranki ya ji, ya kama miki hannu ko?" 

Da sauri na girgiza kai. 

"A'a wallahi, ko kallona bai yi ba." 

"Ni zaki yi wa ™arya, sai na make ki." 

Da sauri na runtse idona tare da ma™alewa a wajen Waya. 

"Ka yi ha™uri dan Allah." 

"Me ya yi miki?" 

"Bakomai wallahi." 

"Bazaki faWan ba sai na sumar dake?" 

"Zan faWa ma, zan faWa ma wallahi." 

"To faWamin." 

"Babu abinda ya yi min kawai ce min ya yi wai ni da kai mun fara hankali tun da har ina zuwa gida, sai kuma ya ce yanzu saura na makaranta na ce mai tom." 

"Uban mene haWinshi da ke da har zai ce miki saura makaranta, shi uban me ya kaishi unguwar Talakawan nan? Nana daga yau har Abada kar na sake ganin magana guda Waya ta haWaki da Turaki, kin jini?" 

"Eyh! Na ji ka."

"Shi kuma sai na Wau mummunan mataki akansa." 

Yana faWin haka ya fice zuwa Wakinsa ya barni anan, sai da na yi kuka na na gode Allah sannan na yi wanka na kwanta, dan yanzu Sardauna ba ko yaushe muke kwana tare ba. 

Washe gari na tashi da ciwon kai sabida kukan da na yi daren jiya, adaddafena haWa masa shayi da soyayayyen biredi ya ci, har ya fita ya dawo ya kalleni. 

"Nana Har abada bake ba Turaki." 

"Tom." 

Ya sa kai ya fice, nasan dai asibitin su Bilkisu zai tafi, wai ashe ma ™anin babanta ne ba shi da lafiya shine duk ya ruWe, bai fi awa Waya sa fita ba ya kirani a waya wai 'yan uwan Bilkisu zasu su yi mata jere acan part Win, ban ce masa komai ba bayan tom, ni a yanzu kalaman Yaya Rumaisa nake son zama na baje su a faranti na yi musu filla filla. Amma bansami damar hakan ba sabida kiran da Sardauna ya sake yi min akan lallai na yi wa 'yan uwan Bilkisu abun taSawa. Ta dole na tashi na shiga kwaSa musu cup cake, bayan na yi na haWa musu sa cincin, sabida bana son abun da zai wahalal da ni.

Wajen ™arfe biyu na ji motoci suna shigowa nasan sune, hakan ya sa na ™ara gyara jikina na fito. Manyan matane masu kyau, gayu da ilimi, kowacce tafiya take cike da izza, sai na ji ma na raina kaina abun da na yi musu. Kowacce ta shigo zata Wibi iska daga gabas ta watsa yamma, sai na zama kamar wata 'yar aiki, dan ba wadda tabi ta kaina, hakam yasa na tattare jikina na koma Waki, sai da suka kammala na ji wata na cewa. 

"Ba mutane a gidan ne?" 

Fitowa na yi, tare da faWin. 

"Gani." 

"Ke kamar ba kya ganin mutane ne?"

Murmushi na yi sannan na ce. 

"Na gaisheku tun zuwanku, ganin kamar ba ku kula dani ba ya sa na shige nawa part Win." 

"Ke 'yar talakawa 'yar mitsiyatan Yelwawa, ki iya bakinki nan baki ga mai kama da wacca zaki gayawa magana ba." 

Wani irin Sacin rai na ji ya ziyarce ni, wannan da ta yi maganar ba manta ta ba, ita ce ta ce danj ballagaza a lokacin da na je wajen Bilkisu, cike da Sacin rai na ce. 

"Ko da na ke 'yar mitsiyatan Yelwawan na sami ilimi da tarbiyar da nasan na girmama ba™o a duk inda ya same ni, kuma a 'yar mitsiyatan Yelwawan nake da ™imae da 'yar masu kuWin Takur zata nemeni da kanta." 

"Ya isa." 

Wata mata ta daka tsawa, sannan ta nuna yarinyar da ta yi maganar. 

"Subisha baku kyauta ba, Nana ki yi ha™uri." 

Na yi mata murmushi, sannan na ce. 

"Bakomai Anty, har zaku wuce ne?" 

"Eyh, zamu wuce sai kuma mun dawo kawo amarya." 

"Allah Ubangiji ya kawo ku lafiya, ga Snacks da ya ce ayi muku." 

Na faWa ina shigewa kicin, box uku na yi na snacks Win na Wauko na kawo musu, tare da faWin. 

"Gashi an gode, Allah Ya sanya alheri." 

"Amin amin, ku Wauka mu tafi." 

Suna fita na koma Waki na kwanta, dan ni yanzu gidan ma gaba Waya ya daina min daWi, na ™agu ayi auren nan a gama hankalin Sardauna ya dawo jikinsa. 

Washe gari ta kama rana littinin, ranar suka yi football match, tsakanin familyn Ta Ambo da na su Bilkisu, ba Sardauna ya shigo gida ba sai wajen Waya saura na dare, lokacin har na yi bacci na farka. 

"Honey! Duk na yi busy al'amuran aure da wahala." 

Iaa daga kwancen na yi mishi murmushi, sannan na ce. 

"Sannu ko na yi ma tausa?"

"Mene tausa Nan?"

"Massage."

"Uhm, ai kema kin gaji Nana." 

"Idan kana so ai sai na yi ma."

"Ki huta kawai Sarauniyar mata Nana, uwar gidan Sardauna Ta ambo." 

Wani daWi na ji kamar na jawo shi ma haWiyeshi, washe gari Talata suka yi wani party, tsakanin 'yan gidan Ta ambo da 'yan gidasu Bilkisu, ina daga gida amma nasan su kansu 'yan uwa Sardauna sun fi farin da auren Bilkisu akan nawa, ranar kam sai bacci na yi na ™yale Sardauna, dan ban san lokacin da ya dawo ba. 

Ranar Laraba suka tafi Abuja, zasu dawo ranar juma'a bayan anyi Waurin aure, duk irin hidimar da Sardauna ke ciki ba cikakken awa sai ya kirani. 

"Nana karki kula Turaki, karki kula wani namijn, ko su Ra'is."

Shine kaWai abinda yake faWa da zarar ya kirani, na kira Hajiya awaya na ce mata dan Allah Yaya Radiya ta zo ta yani zama, a yanayin ina bu™atar wani a kusa da ni, Hajiya ta ce sai dai ta dinga zuwa tana yini idan dare ya yi sai ta tafi, ta dole na amince da hakan. 

A zuwan da Yaya Radiya take yi, ta kan Wan bani 'yan shawarwari akan yadda zan rayu da kishiyata, ba kowanne al'amuranta zan shiga ba har Sardaunan ma, na dinga kama kaina akansa a gabanta, na ja mutuncina. Haka dai ta dinga ba ni shawarwari. 

Ranar juma'a ™arfe Waya aka Waura auren SARDAUNA DA BILKISU, a babban masallacin birnin tarayya na Abuja. Duk da Yaya Radiya da Yaya Rumaisa suna nan hakan bai hanani zubar da hawaye ba, Sardauna dai ya zama ba nawa ba ni kaWai, ya zama namu mu biyu da wata, Wakin Sardauna ya zama ba sirrina ni kaWai ba, ya zama sirrinmu mu biyu, na yi kuka kamar raina zai fita daga baya kuma na ha™ura na fawawwala komai. 

A daren juma'ar su ka dawo, amma Sardauna bai shigo, arz™ina Waya ina jin motsin Turaki dan baije Abuja ba kwata kwata, sai washe gari asabar Sarduana ya shigo, shima a gurguje ya zo yana shirye shiyen tafiya dinner ta yau. Bai ko tsaya ya ji yana ke ba, ya na rayu bayan tafiyarshi, ta dole na ha™ura na sallama Sardauna, Allah Ya kaimu a gama bikin. 

Anyi gagarumar dinner ta gani ta faWa, wacca gaba Waya jihar jigawa ta Wauka, ko ina kaduba sune suke yawo, Malaika daga kano ta kira layina, ina Wagaqa ta fara magana kamar zata hau ni da faWa. 

"Nana ashe tun can da Sardauna ba sonki yake ba kika aureshi? Yanzu gashi duniya ta shaida a yanzu yake auren matar so." 

Wani ™ululun abu ne ua tsayamin a raina, na fashe da wani irin kuka sannan na kashe wayar gaba Waya, mutane daman har jira suke wani abu ya faru su hau turama salan su Waga ma hankali, haka na yini ina kuka babu me rarrashina, ni dai har na yi bacci banga Sardauna ba, banji Wuriyarsa ba. Haka na tashi da wani irin ciwon kai mai azaba, ko breakfast ban iya ba na watsa ruwa da ™yar na kira Sardauna a waya akan banda lafiya, amma bai Wauka ba sai na kira Yaya Rumaisa na sanar da ita, ba ta ce min komai ba rta kashe wayarta, can sai na ga ta turumin text da wata lamba DR NA'IMA DA˜AYYAWA. Tabbas a yanzu nake ™o™arin gano gaskiyyar cewa 'yan uwa 'yan uwa ne, duk daWin da namiji yake baki bai ko rabi 'yan uwa ba, duk da irin fushin da suke da ni, bai hana su zuwa gidana ba lokacin da nake cikin matsala, haka bai hana su ba ni taimako ba a lokacin da na bu™ata. Lambar na kira bugu Waya aka Wauka. 

"Salamu alaikum, ina kwana?" 

"Lafiya ™alau Alhamdulillah." 

Ta amsa muryarta a sake, sai da na gyara murya sannan na ce. 
Chapter 36 · 0% Book details