← Book details Sartse Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 25 OF 39

Sashe 25

Sartse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

A tsakanina da Sardauna abubuwa suna tafiya yadda suke, kawai dai kwana biyu ya ™ulla sabuwar abota da wayarsa da kuma zuwa majalisa, wanda a yanzu ya Wan rage bai cika fita kullum ba. 

Yau tum safe na kammala aikina, dan mu yi da Bilkisu zan koya ma ta yadda ake Samosa wrap, ta ce tana so kuma ta ga ina yi yawan yi tasan dole maza suna so. 

Ina tsaka da aikin gida ta shigo, daman ta ce yau gudun wajen aiki za ta yi, murmushi na sake sannan na ce. 

"Har kin ta so?" 

"Na dai gudu, ai yau sai na koyi abin Samosar nan, har da wasu kayan fulawar tunda nima na kusa aure." 

Murmushi na sakar mata sannan na ce. 

"Ke ce muna da shan biki." 

"Ke ba wanda nake kulawa, kawai ma faWa ne." 

"Wai damam ina ta so na tambayeki me ya sa bakya kula maza ne, ba ayi miki zancen aure a gida?" 

"To Nana ai aurw lokacine, bazan iya biyewa namiji ba inda ba na aure ba, dan ba duka ba ne suke da kirki, yanzu zai yi miki SARTSE a rayuwarki indai namiji ne." 

"Amma nikam Alhamdulillah wallahi, miji dai na yi da ce." 

Na faWa ina shiga cikin kicin, bayana ta biyo tana faWin. 

"Ga alamu nan dai, muma idan mun sami irin nakun sai mu aura, amma wa'yanan samarin shawon ba dani ba." 

Na tuntsire da dariya sannan na ce. 

"Lallai fa Samarin Shawo." 

Haka muka shiga ina yi tana kallo tana 'yan tamnayoyinta har muka kammala. Daga nan muka dawo falo muka shiga hira tana nan har yamma sannan ta tafi. 

Haka rayuwata ta yi ta tafiya, yau daWi gobe akasin haka, abubuwa suna tafiya wasu yadda aka tsara wasu kuma ba yadda aka tsara ba, tsakanina da Sardauna kullum sabuwar soyayya, sabuwar biyayya, a kullum Sardauna yana farin ciki tare da yin alfahari da ni. Yana yawan ce min. 

"Nana kin yi min komai a rayuwa, Allah Ya bani ikon faranta miki rai." 

Ni kuma a kullum duk wata sabuwar na'uin biyayya yi wa Sardauna nake, wani abu ni a kaina na kan ji kamar ya zarci hankali, dan a yanzu takai idan Sardauna yana kan kujera ni a ™asa nake zama, sai ya dage min nake zama akan kujerar ko na ga ya sauko ™asa. 

08:30pm. 

Zauna nake a falo, hankalina yana kan wayata dan nasan Sardauna yanzu ba lokacin dawowarsa ba ne. 

"Hon!" 

Kamar daga sama na ji muryarsa. 

"Kawo min abinci." 

Ya faWa yana nufar kan gadon, a tsorace na tashi gabana ya na faWuwa, me ya sami Sardaunana haka? 

A yanayinsa ma kamar cusa abincin yake dan kamar baya jindaWi. 

"Me ya faru dan Allah." 

"Bakomai." 

Ya faWa yana ci gaba da abincin, yana cikin ci ya tashi ya shige Wakinsa, ba shiri nima na bishi ciki amma kafin na je ya kulle Wakinsa. 

"Innullahi wa'inna illahir raji'un, me ya faru dan Allah, Ya Allah Ka kawo wa Sardauna na sau™i." 

Na faWa ina komawa falon, sai dai gaba Waya na rasa abinda zan yi tunaninma na kasa, halin da Sardauna yake ciki ya dameni, Whatsapp na duba naga Bilkisu na online, na tura mata message

" 'yar uwa da matsala." Na haWa mata da emoji na kuka, cikin ™asa da minti ta dawo min sa amsa. 

"Sisi me ya faru?" 

"Sardauna ne ya dawo gida da damuwa." 

"Me yake damunshi?" 

"Bai faWan ba wallahi."

"To me kike da baki tambayeshi ba, Nana kije ki tambayeshi mana, a shawarar da nake baki a kullum ina faWa miki ki mayar da damuwar mijinki taki." 

"Ya kulle Wakin." 

"Toopa, gaskiyya wannan babbar matsala ce, ko dai zuwan da na yi Wazu ne?" 

"Anya kuwa, Sardauna baya son mutane su zo amma ke bai taSa min magana akanki ba." 

"Ikon Allah." 

Ta haWo da emoji na mamaki. 

"Yanzu mene abin yi?" 

"Abin yi kije ki tambayeshi mene, ki yi amfani da duk wani ikon da ™arfinki wajen ganin kin magana ce mai damuwar tasa." 

"Na gode 'yar uwa." 

Daga nan na kashe data ta na kwanta, ina ta faman sa™e sa™e har bacci ya Waukeni, washe gari da safe bayan na yi duk wani abu da nasaba, amma Sardauna har wajen ™arfe tara bai fito ba, ina nan zaune akan a falo ya fito da shirinsa, da sauri na tashi tare da faWin. 

"Ina kwana?" 

"Lafiya, ya kike?" 

"Alhamdu Lillah, ga abin breakfast nan." 

"Nana bazan iya cin abinci ba, ina cikin damuwa ki yi ha™uri." 

"Me yake damunka dan Allah, ka faWa min ka ji." 

"Nana ina cikin damuwa kawai, ki yi ha™uri." 

"Yanzu akwai damuwar da bazaka faWan ba a matsayina na matarka dan Allah?" 

"Ba haka ba ne Nana, ki yi ha™uri zuwa na dawo kinji."

Yana faWin haka ya fice, ya barni tsaye kamar wacca aka dasa, na kusa minti goma sannan na sami waje na zauna, haka na shiga damuwa gaba Waya ko breakfast Win nima ban iya ba, sai wajen sha biyu na rana na iya sa abu a bakina, daga nan na dawo kan kujera na ci gaba da zaman damuwa, sai ™arfe biyu Bilkisu tazo bayan ta dawo daga ofis, ta yi mamakin ganin yadda na rame ma fige duk a iya rana Waya. 

"Nana haka kika damu da Sardauna? Duk akansa kin wani canja hala ji fa?" 

"Bazaki gane ba Bilkisu, wallahi ina son mutumin nan sama da kowa, sama da komai a wannan rayuwar, bana so na ga wani abu guda Waya da zai dami Sardauna a duniya, bana son shi wallahi." 

"Lallai Nana, to yanzu me ya ce miki yana damunsa?" 

"Ya ce sai ya dawo." 

"Allah Ya sa alheri ne, Allah Ya sau™a™a al'amuran." 

"Amin amin." 

Haka tai ta yi bani shwarwrin hamyoyin da zan bi na yi maganin damuwar tasa da yanda zan kwantar mai da hankali, na nuna komai zai zo da sau™i, sai yamma ta tafi kamar ko yaushe. 

Tana tafiya na yi wanka na gyara gidan, bayan na yi sau™a™™en abinci na dawo na zauna, ina nan zaune na ji hayaniyar mutane. Labule na Waga na buWe Turaki na gani yau ma kaya ake shigo masa da shi, da alama yau ya dawo dan dama na ji alamun baya gidan, komawa na yi na zauna akan kujera na ci gaba da tunanin yadda zanyi kwantarwa da Sardauna hankali yana dawowa. 

Sai wajen tara sannan ya shigo gidan, babu damuwar a fuskarsa kamar jiya, amma bayan na shiga Waki na fito na ganshi ya haWa lai da gwiwa, da sauri na ™araso inda yake tare da cewa.

"Sardaunana, jarumina, Honey me ya faru?" 

"Nana! Bansan ta inda zan fara yi miki bayani ba, amma tabbas akwai matsala." 

"Wace irin matsala ce haka dan Allah?"

"Nana su Big Daddy da Hajiya ta sun matsamin wai suna ganin jikokinsu na wajena, wai shirun ya yi yawa, Nana duk bayanin da yakamata na yi musu, amma su kasa fahimta, faWi kawai suke duk inda matsalal take na nemo to na yi maganinta, Nana na shiga damuwa matu™a na rasa abinda zan yi shi ya sa kika ga na damu kwana." 

Shiru na yi nima kaina na rasa abinda zan faWa, matsalal daga ina take, me ya kawo duka wannan zancen? 

"Kinji abun wani kala ko?" 

Na gyaWa kai, sannan na ce. 

"Yanzu mene abun da za ayi?" 

"Ni kaina bansaniba, ina ta faman tunani." 

"Allah Ya sau™a™a mana." 

"Amin Honey nah." 

Haka muka zauna jigun jigun gaba Waya na rasa abinda ke mun daWi, me ya kai 'yan uwan Sardauna wannan zancen? Su da suke wayayyu, 'yan boko masu ilimi, amma zasu zo da wannan zancen? 

"Kar ki sakawa ranki damuwa kinji Hon, komai zai zo da sau™i." 

"Nasani." Na faWa tare da yi masa murmushin ya™e, sai yanzu na ji ina ma ina da halin kiran su Hajiya na faWa musu, gaba Waya rabona da su an kusa wata guda, Sardauna duk ya hanani. 

Ko da muka je bacci ma haka kowa ya kwanta, ransa babu daWi, ni barcin ma rabi da rabi na yi, Sardauna ne daman shi duk girman damuwa ba ta hanashi bacci, ni kuwa ko ya damuwa take mussamman ta al'amarin Sardauna to ba ni da wata nutsuwa akai. 

*SARTSE*

-Amanar-Janafty-

*Sayyid Legendspen*

MAH/2026/001

Sadaukarwa.

RAMLAT ABDULRAHMAN MANGA

(Mai Dambu) 

Shafi na sha tara.

    (19)

Gaba Waya Sardauna ba walwala ya yi komai har ya fice, a yanzu ba ni da kowa na kusa sai Bilkisu ita kaWai nake magana da ita, itama sabida mijina ya zaSe ta, kiranta na yi a waya duk da nasan tana wajen aiki, har ta ™araci ringing Winta ba ta Wauka ba, sai da na kira sau uku sannan ta Wauka. 

"Hello Nana, ya aka yi ina ofis ne." 

"Bilkisu akwai matsala ne babba ba ™arama ba." 

"Ta mece? Me yake damun Sardaunan?" 

"Matsalal daga gidansu take, akan zancen haihuwa ne." 

"To ai Nana ba ke ce me matsalal ba ko? Kamar kince min kin taSa Sari ko?" 

"Eyh na taSa, nice me matsalal, wai mahaifata ™arama ce, shi ya sa jariran basu fiya zama ba." 

"Innullahi yanzu Nana mene abun yi?" 

"Wallahi Bilkisu bansaniba, duk na shiga damuwa, mussamman ganin Sardauna da na yi a yanayin damuwa." 

"Ai ba daWi irin haka, ki lallaSashi ki ji ko akwai wafa mafita da yake gani, yau bazan shigo ba sabida zani unguwa amma zan zo a satinan." 

Daga haka ta kashe wayarta ta barni cike da damuwa. Ina nan zaune na rasa abinda ke min daWi, kawai na kira Ra'is bayan mun gaisa na ce da shi. 

"Ra'is akwai matsala a gidana." 

"Ta mece ba dai mijinki ba." 

"Shine Ra'is."
Chapter 25 · 0% Book details