← Book details Sartse Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 24 OF 39

Sashe 24

Sartse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Na tashi na shige Wakin na haWa masa, bayan ya fito ya shirya sosai ya yi kyau kamar ko yaushe. 

"Nana, zancen dinner Win abokina ne, na ga kamar kin damu." 

Na yi murmushi sannan na ce. 

"Allah Ya tsare zaka yi dare ne?" 

"Bazan wuce goma ba ina ga." 

"Tom adawo lafiya, amma dan Allah ko Tv ne zan iya kunnawa zaman ni kaWai ba daWi wallahi." 

Kallona ya yi baice komai ba ya fice, sai na ji kamar ban kyauta ba, na dawo na zauna kan kujera tare da haWa uban tagumi, bayan na yi sallar isha na dawo na sake zama, tun ina sa tan ganin Sardauna ™arfe goma har sha Waya shiru, ta dole na bawa baccin da yake fisgata damar Waukana. 

Cikin bacci na na ji ana cewa.

"Anan kika kwanta? Tashi Nana tun da ba zaki iya jirana na dawo mu yi magana ba." 

A hankali na buWe idona na kalleshi, cikin muryar bacci na ce. 

"Ka dawo?" 

"Eyh, tashi kije ki kwanta." 

Mi™ewa na yi na nufi Waki na kwanata, ba tare da nasan asalin daidai lokacin da Sardauna ya dawo ba. 

Washe gari ma kamar jiya haka na tashi na shiga kicin, wani abu daban nasake haWawa Sardauna, sanna na Wauko wasu cikin cake Win jiya nasake docorating Winsu da icing suger, yau ko da naje Wakinsa ma ya shirya da kansa, sai da wayarsa na kare a kunnesa yana magana. 

"Breakfast ya zama ready."

GyaWamin kai kawai ya yi alamun ya ji, ni kuma na shiga nawa Wakin na shirya, bayan na fito na sameshi akan dinning yana danna waya. 

"Ina kwana?" 

"lafiya ™alau Nana." 

Zama na yi na fara zuba masa abin breakfast Win, bayan na zuba mai nima na zuba, sai a lokacin ya kashe wayar ya fara ci. 

"Nana!" 

Ya kira sunana a hankali, na Wago kai tare da cewa. 

"Na'am." 

"Kince bakya jin daWin zama ke kaWai ko?" 

"Ba banajin daWi ba ne, kawai bansaba da gidan ba ne." 

"Hakuri ake yi Nana, yau da gobe  zaki saba, amma tun da kina so na baki damar amfani da TV Win shikenan?" 

"Eyh shikenan, sai kuma zancen sabon sim Win da ka ce zaka bani, ina son na dinga jin lafiyar Hajiya, kuma nasan itama zata nemeni, ya kamata na sanar dasu mun canja gida." 

"Eyh, to da wannan kam." 

Ya faWa yana cire bayan cover wayarsa, ya ciro min sabon sim card sannan ya ce. 

"Gashi, amma Nana bana son na ga lambar kowa sai ta Hajiya ita kaWai, sai kuma tawa." 

"Tom in sha Allah, na gode." 

Daga nan ya ™arasa abinda zai yi ya fita, bayan ya fita na sim Win na kira Hajiya muka gaisa nake sanar da ita muncan gida, umarni ne daga familynsu kan rashin zaman daWi da suke da Turaki gidan ma guda Waya ne mu da shi. 

Daga nan muka gaisa da su Yaya Radiya da su Ra'is, daga nan muka yi sallama na kashe wayar, haka kawai na ji zuciyata na ingizani akan na je na haWa kayan Sardauna na wanke su, ba tare da na yi wani ja'in ja da zuciyata ba na Wauka na shiga toilet na hau wanki, tun wajen sha biyu har uku na rana ina wanki, sannan na shan ya su na dawo na Waura girki, gaba Waya har na dare na yi. Bayan na ci na yi wanka na zo na kwanta na huta gajiya. Cikin barci na ji kamar ana bugu ™ofar tawa, buWe da idona na yi tare da faWin. 

"Waye?" 

"Ni ce." 

Na ji muryar wata mata, tashi na yi zan nufi ™ofar sai dai idona ya kai kan waya ta na ga agogon wayar ya nuna ™arfe 06:16, gaba na ne ya faWi afili na ce. 

"Ya ubangiji kasa ba ba™uwa na yi ba, a daidai wannan lokacin da Sardauna zai dawo ba."

˜ara bugu ™ofar a ka yi na fita ina faWin. 

"ina zuwa." 

Na faWa ina ™arasawa wajen ™ofar, a hankali na buWe gabana yana faWuwa, aikuwa ba™uwar ce sai sai bansanta ba, murmushu ta yi min sannan ta ce. 

"Sannu!" 

"Yawwa sannu, shigo mana." 

Na faWa ina matsa mata ™ofar, ta shigo cikin falon. 

"Ina wuni."

Na faWa ganin ta girmeni sosai ma. 

"Yawwa Sunana Bilkisu, anan baya nake, na ga an kawo amarya kuma ina yawan cewa zan shigo Allah Bai nufa ba sai yau da na zagayo gidan kisto." 

Ta faWa tana nuna hannunta baya alamun kwatancen inda take, na yi mata wani murmushi mai wuyar fassara, domin ni kaWai nasan irin bugun da zuciyata take, lokacin dawowar Sardauna ne yanzu, kowanne lokaci zai iya shigowa, gashi baya ™aunar ya ga wata ™awa ta kusa ko ta nesa ta zo wajena. 

"Zauna mana to." 

Na faWa ina nuna mata kujera, ta yi min wani irin murmushi sannan ta ce. 

"Ai sauri ma nake, amma zan dawo." 

Ban kai ga buWe baki ba na ji horm Win Sardauna, wanda yake yi daidai lokacin da zai kashe motarsa, wanda yake yinsa domin sanar dani ya dawo. 

"Mai gidan ne ya dawo?"

Ta tambaya ne, na yi murmushi sannan na ce. 

"Eyh shine." 

"Ayyah to kinga kuwa ba sai na zauna ba, amma in sha Allahu zan dawo."

Ta faWa tana juyawa zata fita, daidai lokacin kuma shi ya shigo. Kamar ana buga ganga haka na ji zuciyata na bugawa, da sauri na runtse idona sannan na buWe. 

"Sannu da zuwa." 

Na faWa ina ™arasowa inda yake, ga mamakina ya sa hannu ya komo ni tare da faWin. 

"Nanaty ba™i ne damu?"

Ya faWa yana shigewa ciki, na bi bayanshi ina faWin. 

"Ina zuwa." 

"Uhmm."

Ta faWa tare da zama, ni kuma na bishi ciki. 

"Sannu da zuwa." 

Nasake faWa ina ajiye jakarsa a ma'ajiyinta. 

"Yawwa" 

Ya amsa yana zama kan gado, tsugunnawa na yi tare da fara cire mai takalmi ina faWin. 

"Wallahi bansanta ba, yanzu ta shigo wai anan baya take." 

Kallona ya yi tare da kamo hannuna

"To mene a ciki? Ai hakan yana da kyau sosai da sosai, ke fa kika ce min zaman ke Wai ba ya yi miki daWi kuma daman ka yi ta zama a waje bakasan kowa ba? Ta shi kije ku gaisa." 

Da wani irin yanayin mamaki nake kallon Sardauna. 'Sardauna dai? yau shi ke barin wata tazo gidan nan, har da cewa ayi ta zama a waje ba asan kowa ba, Sardauna da ya tsani ganin ba™o a gidan?' 

"Ki tashi mana." 

Muryarsa ta katse min tunanin da nake, na mi™e na nufi falon. 

"Ki yi ha™uri na bar ki." 

"A'a babu komai fa, ai mai gidan ne ya dawo, bari na zo na wuce amma zan dawo." 

"Tom shi kenan na gode sosai da sosai, nima idan na samu fita zan shigo gidan naku in sha Allah."

Na faWa ina rakata waje, a gurguje na dawo haWa masa ruwan wanka sai na tarar yana toilet Win ma.

Na fito na dawo na jera masa abinci akan dinning, bayan na fito masa da jallabiyar da zai sanya na ajiye mai kan gado, nima na tafi Wakina na gabatar da magariba na dawo falon. 

*****

"Ko ka kirani na yi serving Winka." 

Na faWa ina zama kan dinning Win. 

"Ah bakomai, har ba™uwar ta tafi?" 

Ya tambaya, na gyaWa masa kai sannan na ce. 

"Ta tafi wai amma zata dawo, ni ba ma so nake ta dawo ba, nasan kai baka fiya son mutane suna zuwar mana ba. Zan ma taka mata burki." 

"Nina faWa miki? kawai dai akwai waWanda ban yarda dasu ba ne."

Legendspen

08129553971

*SARTSE*

-Amanar-Janafty-

*Sayyid Legendspen*

MAH/2026/001

Sadaukarwa.

RAMLAT ABDULRAHMAN MANGA

(Mai Dambu) 

Shafi na sha takwas.

    (18)

"Su waye baka yarda da su ba?" 

"Nana kenan? Ni wannan ma duk da ba wani kallo na yi mata ba amma tabbas tafi ™awayenki da yayyunki da yawa kalal nutsuwa." 

Haka kawai na ji ta kwantamin a raina sakamakon abinda Sardauna ya faWa, daman kuma tabbas zaman ni kaWai Win ya isheni na gaji da zaman. 

"To yanzu ba matsala kenan?" 

"Eyh! Ba matsala kam amma dai ba ko yaushe anyhow ba gaskiyya kinsan tsarina." 

"Tom shikenan na gode." 

Na faWa ina ci gaba da cin abincin, shima ya ci gaba da ci bayan mun kammala ya kalleni sannan ya ce.

"Na yi wasu abokai anan baya, suna da majalisa ina tunanin zan fara zama ina rage dare kafin mu saba da yanayin unguwar." 

"Eyh hakan yana da kyau kam gaskiyya, Allah Ya taimaka." 

Na faWa shi kuma ya tashi ya shiga Waki, can ya fito bayan ya ™ara gyarawa ya fice. 

Daga wannan rana kullum Sardauna sai ya fita majalisar nan, baya dawo sai  goma ta gota tun bana jindaWin zaman har nasaba, Bilkisu kam ba ta sake zuwa ba tun ranar ba gaba Waya na damu, har na fara tuanin ko sardauna ne ya dakatar da ita sai kuma na tuna kwata kwata basu haWu ba tin da ya shiga Waki bai fito ba sai da ta tafi. Sai da aka yi sati biyu sannan ta sake zuwa, ranar na yi murna kamar na cinye ta, haka itama ta dinga biya min mun hira sosai kuma na ji daWin zama da ita sosai da sosai, tun daga wannan lokacin ta fara zuwa duk da ba ko yaushe ba,  babban abin daWin Sardauna bai taSa yi min ™orafi akan zuwa na ta ba, duk da wani lokacin su kan haWu. 

Na yi mata maganar rashin haihuwata, ta ™ara ™arfafamim gwiwa tare da ba nj hakuri akan hakan, da cewa na dage da addu'a, babban abinda ya burgeni da Bilkisu shine karatunta ta ti degree a yanzu ma ta Waura masters sannan tana yin aiki, mace mai ilimi daban ce, komai na ta gwanin ban sha'awa akwai tsari, ban taSa zuwa gidansu ba, amma ina yawan  ce mata zanje idan na fita. 

A Sangaren Turaki har yanzu auren shiru, sai dai kawai na ji mostintsa idan ina falo amma bai taSa shigowa ba kuma ko a waje bamu taSa haWuwa ba, da muka yi magana da Ra'is ta wayar Hajiya ya ce da ni wai Turakin nema yake nemansa a waya lokaci zuwa lokaci ya ji lafiyarsa da ta mutanen gidan. 
Chapter 24 · 0% Book details