← Book details Ranar Wanka Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 32 OF 40

Sashe 32

Ranar Wanka Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ƙanwata, na kasa bacci tunanin halin da kike ciki da kewar gida sun dame ni.

Murmushi ta yi sosai tana mamakin ƙarfin zuciyarsa, domin ta yi tunanin duk borin da yake yi da xarar sun keɓe a tare zai ba da kai bori ya hau, kasancewar babu namiji da zai kasance da Wajnah ba tare da ya kware mata ba.

Yayana, don Allah ka yi bacci. Ina hadda ne kuma ni ma yanzu zan kwanta.Ta rubuta tare da tura masa tsaƙon sai ta kashe wayarta ta kwanta.

A lokacin da tsaƙon ya shigo, hankalinsa ya tashi sosai don bai yi tunanin idanunta biyu ba.

Da sauri ya janyo wayar, ya karanta murmushi É—auke a fuskarsa. Iska ya ja tare da fesarwa.

Juyawa ya yi ɗaya ɓangaren ya danna numbobinta don ya kira.

"Ba ta yi bacci ba, tana cikin damuwar da na sanya ta. Ki yafe mini Hilah sonki da ƙaunarki suka janyo mini haka.

Ransa ne ya ɓace, matuƙa jin wayarta a kashe. Ya san ta kashe ne don karya kirata.

Ƙaramin tsaki ya ja, tare da jan bargo daidai lokacin da ya ji Wajnah ta ci gaba da buga ƙofa.

Duk yadda ya so ya yi bacci ya kasa.Ji yake gidan kamar ba mallakinsa ba. Miƙewa ya yi ya shiga cikin bayin ya ɗauro alwala tare da shinfiɗa dadduma ya tayar da sallah.

Kamar kullum istikhara kan lamarin ya fara. Tun ranar da ya fara sonta yake istikhara kamar yadda ma'aiki ya umurce mu da mu yi in muna son aikata wani abu.

Istikhara

* Neman zabin Allah, wata sallah ce mai raka'o'ibiyu, wacce yinta sunnah ce mu'akkada (sunnahce mai karfi), wacce manzon Allah ya koyar dasahabbansa ita har tazo garemu kamar yadda al-qur'ani ya iso gare mu, sallace da akeyi yayin neman zabin Allah akan wani al-amari kamar;aure, sayan gida/mota aikin gwabnati da daisauransu, sai dai ita wannan sallar ba'ayin ta a kan abin da ya ke wajibi ko mustahabbi akan ka; kamar neman zabin Allah akan yin azumin ramadan, ko salloli biyar na yini, ko fitar da zakka, azumin alhamis da litimin da dai sauransu.

* Sai dai wurin Mustahabbi ana iyayi idan sun ci karo, misali: mutum ne yake son yaje umra karo na biyu a lokaci guda kuma yana so ya je wata kasa neman ilimi, to yana iya neman zabin Allah akan ya zaba masa wanda yafi Alkhairi a cikin su.

* Hakika Duk wanda ya nemi zabin Mahalicci,kuma ya yi shawara da talikai muminai, kuma yayi azama a cikin lamarin sa, to ba zai yi nadama ba In sha Allah. Domin Allah Madaukakin Sarki ya ce: "Kuma kashawarce su cikin lamarin ka, idan kuma kaquduri aniya, to ka dogara ga Allah" [Ali-Imran :159].

* Hadisi ya gangaro Jabir ibn Abdullah, Allah yakara yarda dashi da Maihaifin saya ce : Manzon Allah (SAW) ya kasance yana koya mana yin Istikhara (neman zabin Allah) a cikin dukkanin al'amura kamar yadda yake koyamana sura daga cikin surorin Alqur'ani. Ya kance: ''Idan dayanku yayi niyyar yin wani al'amarito yayi sallah raka'a biyu ba farillah ba sannanya ce:

"Allaahumma innii astakhiiruka bi ilmika,wa'astaqdiruka bi kudiratika, wa'as'aluka minfadlikal azeem, fa innaka takadiru wala akadiru,wa ta'alamu wala a'alamu, wa anta allamulguyube, Allahumma inkumta ta'alamu anna hazalamri kharal lii fii deenii wama'ashii wa'akibatiamrii, aajilihi wa'aajilihi faqadirhu lii wayassirhulii thumma baariklii fiihi, wa'inkunta ta'alamuanna hazar amra sharrullii fii deenii wama'ashiiwa'akibati amrii aajilihi wa aajilihi fasrifhu'anniiwasrifnii anhu wakadur liyal khaira haithu kaanathumma raddini bihi."

"Ya Ubangijina! ina neman zabin ka da ilimin Ka,kuma ina neman tabbatuwar ikon Ka, ina rokanfalalar Ka Mai gaima, Kai ke da iko ni banda shi,Kai ne Masani ni ban san (komai ba) Kai nemasanin abin da yake boye. Ya Ubangiji na! Inkana ganin wannan abu ('sai ya fadi abin da yakeistiharan a kai') shi yafi min a addinina da rayuwata da qarshen lamarina, to ka tabbatar min dashi, ka sauqaqe min sannan ka yi min albarka acikinsa, in kuwa kana ganin wannan abu sharri negare ni a addinina da rayuwata da qarshen lamarina, ka juyar da shi daga gare ni, ni ma kajuyar da ni dagagare shi, ka kudurtarmin da alkhairi sannan kaamintar min da shi" [Bukhari]

* Na tabbata banbanci ya bayyana a fili gama'abota hankulla da tunani tsakanin wannan karantarwar ta shugaban talikai SAW, da Tsirfe-tsirfe da shafi fadin, wasu marubuta littattafan koyarwa don neman kudi, da masu tsibbace tsibbace

* Ita dai wannan Sallah Mustahhabbi ce anso kayita (domin sunnah ce mai karfi, sannan zakasamu lada idan kayi), amma idan bakayi babalaifi.

* Wannan Addu'a ta istikhara ana yin tane bayan ka sallame, sallar nan da kayi mai raka'a biyu,duk da wasu malaman na ganin ana karanta tane,bayan tahiya da salatin manzon Allah SAW kafinSallama, domin mafi Al-khairin bijiro da addu'aacikin sallah shine sujuda da bayan tahiya, saidai magana mafi rinjaye shine bayan Sallama.Allah shine Mafi Sani..* Babu Laifi ga mutum ya maimaita istakharasama da daya, hakam ya tabbata daga cikinmagabata, kamar Abdullahi dan zubair Allah yakara yarda dashi yayi istakhara sau ukku.[Muslum - 970].

* Babu wani hadisi daya inganta da yazo dasurorin da ake karantawa, a cikin sallar nemanzabin Allah.

* Haka kuma babu wani hadisi da yazo daga Annabi cewa idan mutum yayi istakhara zaiyimafarki ko zaiga wani mutum yana yi masa bayani al-amarinsa.

* Babu shakka duk wanda ya yi zai samu natsawa cikin abin da Allah madaukakin sarki ya zaba masa.

* Ba mafarki ake yi ba kamar yadda mutane dayawa suka dauka, ana ganewa ne da yanayin nutsuwar zuciya, idan aure ne sai kaji zuciyar kata qara nutsuwa da yarinyar, idan sana'a ne kakeso ka farasai kaji zuciyar ka tanutsu da sana'ar.

* Za'a iya yin wannan sallah raka'a biyu da rana,ba dole sai da daddare ba, sannan zaka yita ne daga lokaci zuwalokaci har sai ka sami biyan buqata, sannan Ana yin tane ko da lokacin da aka hana yin sallah ne,idan bukatar hakan ta taso, domin ita tana daga cikin "Nawafilul Asbab" - "Nafiloli masu dalili".

* Wannan kenan don gane da abunda ya shafi Sallar neman zabin Allah madau kakin Sarki,Muna fatan Allah ya bamu damar Aiki Abin da muke rubutawa da karantawa.

Still yanzu ma natsuwa fiye da ta, da ya samu wanda ya ƙara ninka masa ƙaunarsa.

Ajiyar zuciya ya saki tare da janyo filo ya kwanta a sallayar.

Wajnah kuwa tun tana buga ƙofa, tana kuka tana kiran sunansa, har ta kasa sakamakon mararta da ya riƙe ya murɗe ko numfashi ta kasa.

Kallonsa kawai xai sanya ta rikice ballantana da ta haÉ—a jikinsa da nata.

Rintse idanunta ta yi cikin azaba tana kiran sunan Allah. Ta haƙura ne saboda duba agogo da ta yi ƙarfe ɗaya har da kwata. A lokacin ta gane ko kwana ta yi tana buga wa sam ba zai buɗe mata ba.

Jikinta ya yi sanyi matuƙar gaske! Domin bata taɓa tunanin bayan auren ba zai iya ɗauke kansa daga jikinta har ya wulaƙanta ta ta.

"Wace ce wannan da ta sace zuciyar mijina?" Ta yi wa kanta tambayar tare da jifa da filon da ta danne mararta.

Kuka sosai take yi yayin da wani sashe na ɓangaren zuciyarta yana gaya mata Huwais ba zai so ta ba.

Hawaye masu zafi suka ƙara kwaranya a idanunta, daidai lokacin da mararta ta ƙara murɗawa. Gurmususu a ƙasa ta shiga yi, tana kiran sunan Allah har ta samu sauƙi.

A hankali ta miƙe tana jan ƙafa ta shiga cikin ɗakinta. Kan gado ta kwanta tana nishin wahala da ƙyar.

Ta daɗe a haka har zuwa ƙarfe uku. Wayar Wahida kuwa ta kira yafi cikin kwandon masaki.

Labarin ya zo da wani irin salo da nishadi, karku baru a ba ku labari. Ku biyo ni domin it’s just like a little introduction part, and guess what? You will really enjoy it. Believe me, my dear readers. Your happiness is my concern. Follow me on Facebook, Whatsapp, Wattpad, Arewaboo, and Bakandamiya. Ta ku, Jamila Lawal Zango (Jamsy).

FOR WHATSAPP: 07072971093
CALL: 008144072423

*RANAR WANKA...*

NA

JAMILA LAWAL ZANGO
"JAMCY"

☀️ *First Class Writers Asso* ☀️

Hame of Qualities And Trusted writer's of The Nation

*GARGAGAÆŠI*

Ban yarda kuma ban amince a juya mini labari ko ta wace siga ba, sannan ban bada lamuni a ɗora mini littafi a kowane kafar sadarwa ba sai da izinina a kiyaye⚠️

JAN HANKALI

Kirkirarran labari ne ban yi shi don wani ba, idan har ya yi daidai da labarin ki/ka to arashi ne.

SADAUKARWA

Kacokam labarin daga farkonsa har karshe sadaukarwa ne ga ƙawata sahibata Aysha Na Lado. Allah saka miki da alkairi ya raya zuri'a.

PAGE 20

BISMILLAHIR RAHMANINR RAHIM
Ta daɗe a haka, har zuwa ƙarfe uku. Wayar Wahida kuwa ta kira yafi cikin kwandon masaki.

Tun da take ba ta taɓa kwanar wahala ba, domin yadda ta ga dare haka ta ga rana. Har zuwa kiran sallar farko ba ta rintsa ba

Kiran sallah na biyu ta É—auki wayarta, tana dafe da mararta ta kira numbar Wahida, tana adduar Allah ya sa ta É—auka.

Ta cika da farinciki jin wayar na ringing.

"Wash! Fahima ki taimaka mini mutuwa zan yi." Ta furta tana nishin wahala.

"Innalillahi lafiya?Ai sai da na gaya miki kar ko sha maganin nan da yawa, saboda shegen kafiyarki kika kai kanki kika baro. Allah ya sa bai illata ki ba." Ta faÉ—a tana mata dariyar mugunta.

"Ni in da ma ace wannan ne ya sanya ni wahala sai na ji daɗi, saboda na tabbata kwana zan yi mala'iku suna rubuta mini lada. Wahida ban san wane irin kalar miji na aura ba, domin wallahi jiya kallon kirki ban samu ba, daga ƙarshe ya tura ni waje ya rufe ƙofarsa." Ta ƙarashe maganar tana share hawaye sai kuma ta ɗora da cewa jin ta yi shiru.

"Na rantse sai Hajiya Zamzam ta biya ni kuɗina, saboda da na shafa turaren kin san Allah, toshe hancinsa ya yi, baya ta gaya mini haka zai rinƙa bina sai yadda na yi dashi."

Matuƙar mamaki ya kama ta matuƙa jin abin da ta ce.

"Anya mijin ki ba aljana ta aure shi ba? Domin na ga ko ni da na ke har na haihu, wallahi ina shafa turaren haka oga yake bina ina shan ƙamshi."
Chapter 32 · 0% Book details