Sashe 6
Jin Dadi Sabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Shukura kwance take cikin dare Tana ta kwasar baccinta taji kamar hayaniya a hankali ta bude idonta ta kunna torchlight kenan taji ashar da zage zage,ai sai ta kashe torch ta leka ta window nan take ta hangame baki tare da fara Hawaye taga Baffanta da Innarta an dauresu ga wasu jibga jibgan arna sunkai su 15 dauke da bindigu,Baffa taga sun kafe da mari,da sauri ta bude kofa ta fito da gudu Tana kuka tana rokonsu su bar mata Baffanta itama mari suka zuba mata nan take ta sume sharaf a kasa Inna ta fasa Ihu sabo da rashin Imani wani yasa wuka yayi mata yankan rago,Baffa ya rafka salati tare da dafe zuciyarsa nan ya fadi matacce zuciyarsa ta buga.
Arnan dariya suka dinga Yi ta mugaye sannan suka kada shanu da dabbobin Baffa kaf suka tafi dasu,a garin basu kadai ba har sauran fulani da dama wasu an kashe su an tafi da dabbobinsu, Tunda Shukura ta suma bata farfado ba sai da gari yayi haske lokacin Mutane sun cika gidan taf,da kuka hade da salati ta farka Tana Ihun Baffa...Inna.... Wayyo...nan tayi arba da gawarwakin Inna da Baffa sai ta haukace gaba daya tana birgima da ihu tana na Shiga uku ina zan sa kaina na huta,gatana ya kare Inna... Baffa sambatu takeyi Kala kala sai da kowa ya tausaya mata harda masu kuka gaba daya ta haukace bata san inda kanta yake ba, har akayiwa Inna da Baffa sutura tare da kaisu makwancinsu ana ta zaman makoki,Shukura kuwa suman ta yafi sau goma tana farfadowa kamar zata sheka lahira,sai maza ne suka riketa aka shiga yi mata addua tare da Kiran Nasuru me Chemist yayi mata allurar bacci ya sa mata Drip nan bacci ya kwasheta,bata farka ba sai dare Ta dora daga inda ta tsaya ana mata nasiha amma abanza cewa take ni bazan Hakura ba, in Allah ya yarda kuma sai iyayenku sun mutu Allah yasa babanku da babarku su mutu suma,bazan ba kowa hakuri ba sabo da nima bazan hakura ba.
wata tsohuwa tukuf ta shigo gaisuwa gidan Shukura wacce ta gama rama sallolinta Tana kuka ta Kalli tsohuwar tace ai gwara da wannan ce ta mutu tunda ta tsufa bata da amfani mene amfaninki,wata ma cikin dangin Baffa na sallama tace ga wannan Ma shekara nawa kullum cuta takeyi ai da ita ta mutu,matar tace Allah sarki yar nan kowa na can ne lokaci nane baiyi ba.
Wasu yan mata su biyu sunzo gaisuwa Zaraf shukura tace ga Baban wannan Ma shanyashi ake a Rana sai an kwantar sai an tayar mene amfaninsa Ai ni wlh iyayena sunfi na kowa Amfani, ana mutuwa amma mutuwar su Baffa ta musamman ce..ba shiri Nasuru me Chemist yazo ya kara dannawa Shukura allurar bacci da Drip, bata farka ba sai washe gari,ba laifi ta dan dawo hankalinta amma sai taji masu zaman makoki dangin Baffa suna lissafa mutanen da arnan suka kashe a garin,nan Sai ko akaji Shukura ta kece da dariya tace Alhmdllh uban kowa ya mutu wlh tunda ubana ya mutu uwar kowa ta mutu tunda na rasa tawa,yanzu har Dantani Baban Aishalle ya mutu?kai Alhmdllh amma Allah na gode maka,yawwa gwara Kowa iyayensa su mutu duk mu zama daya,ai wlh bazan Kara jimamin mutuwa ba, Ni mutum ya sake yace min ubansa ko uwarsa ta rasu sai dai aga ina nishadi wlh.
Wani ne ya rafka sallama tare da cewa bayin Allah Ashe arnan Jos har rigar yan jalo suka je sunyi kashe kashe da yawa yafi na wannan kauyen namu,ayyiriri nanaye akaji Shukura tace yawwa su dandana suma suji Me naji.
Kwana uku kullum sai anyiwa Shukura Allurar bacci bata ci bata sha sai an mata Jan Ido har akayi Bakwai.
Kullum Shukura bata daina kuka tana Tuna iyayenta zata fashe da kuka,haka har aka kwashe 40days Dan abinda Baffa da Inna suka mallaka aka siyar gaba daya har gidan da Shukura ke ciki,dangin Baffa dama tunda akayi bakwai suka tafi da Shukura gidansu,haka aka raba gado yanda Allah yace aka bawa shukura kudi dubu Dari biyar kasancewar Kauye ne filaye da gonaki basa tsada,Shukura ba kunya ta karbe kudinta a ledar Viva tana kukan su Baffa.
nan ta samu Kudin nan ta Fara dagargazar dadi,ba irin shawarar da yan Uwa basu ba shukura ba yanda zatayi da kudinta ta Samu ci gaba amma tace a'a Sabo Da tun farko bata da mafadi sai abinda taga dama take yi ba a sata ba a hanata, gashi bata daukan ko tsinke a gidan dama sun San halinta ganin maraicin da take ciki suke daga mata kafa,ga shegen iyayi wajenta, kudinta ta sasu gaba tayi kyauta taci dadi,yauma da Yamma liss taga wani katon zabuwa Tana yawo tace nawa wannan Zanbon Goggo ko na uban waye zan siya a siyar min shi,Goggo ta tabe baki tare da cewa nawa ne kuma ni dubu biyu zan siyar,nan ta zaro 2k ta biya tasa yara suka Kama mata shi aka yanka Sabo da Kiwa ma wata budurwa ta bawa tace gyara naman nan ki soya min Zan baki Dari biyar,jiki na Rawa budurwa ta Karbe tayi yanda take so, ta karba tare da figawa mutanen gidan nasu sabo da bata da rowa,zama Tayi da Maltinarta a gefe tana ci tana kora Maltina sai kuma ta fashe da kuka ta tuno Baffanta da Inna yanda watarana ma abincin a baki suke bata ana lallabata taci,haka takeyi kullum barnar kudi ga Dunkuna tana faman yi iri Iri har shopping taje cikin garin Jos ta siyo cosmetics da turaruka masu kyau,abinda kawai take birge mutane dashi addini ne da ita sosai bata wasa da addini.
A kwana a tashi Dangin Baffa suka takura su ta ishesu tayi girma da yawa dole sai tayi aure ko su bata duk wanda suka ga dama,ita kuma tace ba wanda ya isa yayi mata dole,su kuma Suka ce baza ta ja musu abin kunya ba sai dai ta bar musu gida baza su iya da halinta ba, Kawunta ta samu tace Kawu kasan bana Zance bani da saurayi kuma ina so na cikawa Baffa burinsa na zuwa abuja nayi kallo kallo.
Takaici ya kama Kawu kawai ya jawo sanda ya fara zane Shukura Yana Karuwanci zaki shiga tsinanniya,sai da ya farfasa mata jiki abinda iyayenta ko zagi basu taba yi Mata ba, haka suka bi suka tsaneta a gidan da sauran dangi bata da ikon magana sai duka kuma yanzu aiki ake sata sosai a gidan kamar jaka lallai taga maraici, ko wanke wanke idan tayi To ranar da zazzabi zata kwana bata saba ba,Kwatsam sai Kawu sukayi shawara a junansu suka zabowa Shukura miji wani Me kiwon Shanu Halilu,Halilu Dan shaye shaye ga neman mata kaf garin an sanshi,Shukura bata da labari sai da bikinta ya rage saura 1wk taji ana kiranta da Amarya tana tambaya taji a garin ana ta mata dariya anga karshen iyayi da jin dadi.
Kukan Maraici Tayi tana tuna so da gatan da iyayenta ke nuna mata amma ga yanda ta koma dare daya,ragowar kudinta ta duba saura Dubu Saba'in kacal Duk ta kashesu a siyi banza siyi Wofi Trolley dinta ta jawo ta shirya kayanta a ciki kaf sauran da bata so ta barsu,Handbag dinta ta zuba kayan kwalliyarta ciki tare da kudinta ta shirya tsab,sai da ta Bari an shiga masallaci sallar asuba ta sadada cikin duhu ta bar Garin bata tsaya ko ina ba sai garin Jos ta zarce Tasha inda zata shiga motar Abuja,a Tashar tayi sallar asuba da Asuba,ta dauko Toothpaste dinta da Brush tayi da ruwa pure water,a tashar ta siyi kosai da biredi tare da shayi hadin kauri taci ta koshi sannan ta wanke fuskarta da sabulunta harda shafa powder da jan baki sama Sama,ji tayi Driver yana cewa shigo yan mata zamu wuce,da sauri ta shiga ta zauna mota ta tashi sai Abuja.
Bikin Ahleef saura kwana uku ango ba zama Sun gama gayyatar abokai,ba abinda ba a gama ba na shiri,sun narkar da kudi,Abba yana sama a dakinsa yaji ance yazo ga manyan danginsa sunzo Maza biyu da mata biyu,ya fito Sun gaisa kenan sai ga yayan Momee da kaninta tare da yayarta,abin ya basu mamaki,bayan an gaisa anci ansha,suka ce abinda yake tafe damu ba komai bane sai akan auren Niima,Gaskiya bamuji dadi ba Sam da ilminku da komai zakuyi mata auren dole,jiya taje mana Tana kuka ita bata so auren dole za ayi mata,Abba ne ya dakatar dasu yace ku bari Niima tazo shima Ahleef yazo, Nan Momee ta Kirasu a waya,5mnt dukkansu suka zo, Momee tace gata nan gashi kuji daga bakinsu,Ahleef suka kalla kai kaine da kanka kake son Niima tsakani da Allah?da Sauri Ahleef yace ae,Niima kefa?kinje kin Kai mana kukanki yanzu maimaita a gaban kowa,ai kuwa ba tsoro Niima tace uhmm... Ahmm..Ina sonsa amma bada aure ba,ni ban shirya aure ba, kuma ni bana...Mari taji Abba ya kifa mata shi,Tana kuka tace wlh ni bana son aurensa,Abba Hawaye suka gangaro masa,Momee kam dama zancen ya dade da zuwa kunnenta,a hankali tace Baban Suhail kyaleta,ai dai kin tabbatar bakya sonsa ko? Niima tace ae,Abba yace ni zaki wulakanta sai ki fada mana sabo da me? Tana kuka tace bashi da asali wa ya sani ko shege ne,Momee Kuka kawai take shekawa, Abba yana Jin haka yace Ahleef kayi tawakali kayi hakuri,Allah zai baka wacce ta fita,ke kuma baza muyi miki baki ba amma ki sani sai kinyi nadama,yan Uwansa ya kalla yace na gode kuje kawai,jiki ba kwari suka tafi,itama Niima ranta Fari kal ta koma dakinta tana bugawa samari da yanmata frnds nata waya Tana Murna suma haka.
shiko Ahleef ya mike kenan ya yanke jiki ya fadi kasa sumamme,
Arnan dariya suka dinga Yi ta mugaye sannan suka kada shanu da dabbobin Baffa kaf suka tafi dasu,a garin basu kadai ba har sauran fulani da dama wasu an kashe su an tafi da dabbobinsu, Tunda Shukura ta suma bata farfado ba sai da gari yayi haske lokacin Mutane sun cika gidan taf,da kuka hade da salati ta farka Tana Ihun Baffa...Inna.... Wayyo...nan tayi arba da gawarwakin Inna da Baffa sai ta haukace gaba daya tana birgima da ihu tana na Shiga uku ina zan sa kaina na huta,gatana ya kare Inna... Baffa sambatu takeyi Kala kala sai da kowa ya tausaya mata harda masu kuka gaba daya ta haukace bata san inda kanta yake ba, har akayiwa Inna da Baffa sutura tare da kaisu makwancinsu ana ta zaman makoki,Shukura kuwa suman ta yafi sau goma tana farfadowa kamar zata sheka lahira,sai maza ne suka riketa aka shiga yi mata addua tare da Kiran Nasuru me Chemist yayi mata allurar bacci ya sa mata Drip nan bacci ya kwasheta,bata farka ba sai dare Ta dora daga inda ta tsaya ana mata nasiha amma abanza cewa take ni bazan Hakura ba, in Allah ya yarda kuma sai iyayenku sun mutu Allah yasa babanku da babarku su mutu suma,bazan ba kowa hakuri ba sabo da nima bazan hakura ba.
wata tsohuwa tukuf ta shigo gaisuwa gidan Shukura wacce ta gama rama sallolinta Tana kuka ta Kalli tsohuwar tace ai gwara da wannan ce ta mutu tunda ta tsufa bata da amfani mene amfaninki,wata ma cikin dangin Baffa na sallama tace ga wannan Ma shekara nawa kullum cuta takeyi ai da ita ta mutu,matar tace Allah sarki yar nan kowa na can ne lokaci nane baiyi ba.
Wasu yan mata su biyu sunzo gaisuwa Zaraf shukura tace ga Baban wannan Ma shanyashi ake a Rana sai an kwantar sai an tayar mene amfaninsa Ai ni wlh iyayena sunfi na kowa Amfani, ana mutuwa amma mutuwar su Baffa ta musamman ce..ba shiri Nasuru me Chemist yazo ya kara dannawa Shukura allurar bacci da Drip, bata farka ba sai washe gari,ba laifi ta dan dawo hankalinta amma sai taji masu zaman makoki dangin Baffa suna lissafa mutanen da arnan suka kashe a garin,nan Sai ko akaji Shukura ta kece da dariya tace Alhmdllh uban kowa ya mutu wlh tunda ubana ya mutu uwar kowa ta mutu tunda na rasa tawa,yanzu har Dantani Baban Aishalle ya mutu?kai Alhmdllh amma Allah na gode maka,yawwa gwara Kowa iyayensa su mutu duk mu zama daya,ai wlh bazan Kara jimamin mutuwa ba, Ni mutum ya sake yace min ubansa ko uwarsa ta rasu sai dai aga ina nishadi wlh.
Wani ne ya rafka sallama tare da cewa bayin Allah Ashe arnan Jos har rigar yan jalo suka je sunyi kashe kashe da yawa yafi na wannan kauyen namu,ayyiriri nanaye akaji Shukura tace yawwa su dandana suma suji Me naji.
Kwana uku kullum sai anyiwa Shukura Allurar bacci bata ci bata sha sai an mata Jan Ido har akayi Bakwai.
Kullum Shukura bata daina kuka tana Tuna iyayenta zata fashe da kuka,haka har aka kwashe 40days Dan abinda Baffa da Inna suka mallaka aka siyar gaba daya har gidan da Shukura ke ciki,dangin Baffa dama tunda akayi bakwai suka tafi da Shukura gidansu,haka aka raba gado yanda Allah yace aka bawa shukura kudi dubu Dari biyar kasancewar Kauye ne filaye da gonaki basa tsada,Shukura ba kunya ta karbe kudinta a ledar Viva tana kukan su Baffa.
nan ta samu Kudin nan ta Fara dagargazar dadi,ba irin shawarar da yan Uwa basu ba shukura ba yanda zatayi da kudinta ta Samu ci gaba amma tace a'a Sabo Da tun farko bata da mafadi sai abinda taga dama take yi ba a sata ba a hanata, gashi bata daukan ko tsinke a gidan dama sun San halinta ganin maraicin da take ciki suke daga mata kafa,ga shegen iyayi wajenta, kudinta ta sasu gaba tayi kyauta taci dadi,yauma da Yamma liss taga wani katon zabuwa Tana yawo tace nawa wannan Zanbon Goggo ko na uban waye zan siya a siyar min shi,Goggo ta tabe baki tare da cewa nawa ne kuma ni dubu biyu zan siyar,nan ta zaro 2k ta biya tasa yara suka Kama mata shi aka yanka Sabo da Kiwa ma wata budurwa ta bawa tace gyara naman nan ki soya min Zan baki Dari biyar,jiki na Rawa budurwa ta Karbe tayi yanda take so, ta karba tare da figawa mutanen gidan nasu sabo da bata da rowa,zama Tayi da Maltinarta a gefe tana ci tana kora Maltina sai kuma ta fashe da kuka ta tuno Baffanta da Inna yanda watarana ma abincin a baki suke bata ana lallabata taci,haka takeyi kullum barnar kudi ga Dunkuna tana faman yi iri Iri har shopping taje cikin garin Jos ta siyo cosmetics da turaruka masu kyau,abinda kawai take birge mutane dashi addini ne da ita sosai bata wasa da addini.
A kwana a tashi Dangin Baffa suka takura su ta ishesu tayi girma da yawa dole sai tayi aure ko su bata duk wanda suka ga dama,ita kuma tace ba wanda ya isa yayi mata dole,su kuma Suka ce baza ta ja musu abin kunya ba sai dai ta bar musu gida baza su iya da halinta ba, Kawunta ta samu tace Kawu kasan bana Zance bani da saurayi kuma ina so na cikawa Baffa burinsa na zuwa abuja nayi kallo kallo.
Takaici ya kama Kawu kawai ya jawo sanda ya fara zane Shukura Yana Karuwanci zaki shiga tsinanniya,sai da ya farfasa mata jiki abinda iyayenta ko zagi basu taba yi Mata ba, haka suka bi suka tsaneta a gidan da sauran dangi bata da ikon magana sai duka kuma yanzu aiki ake sata sosai a gidan kamar jaka lallai taga maraici, ko wanke wanke idan tayi To ranar da zazzabi zata kwana bata saba ba,Kwatsam sai Kawu sukayi shawara a junansu suka zabowa Shukura miji wani Me kiwon Shanu Halilu,Halilu Dan shaye shaye ga neman mata kaf garin an sanshi,Shukura bata da labari sai da bikinta ya rage saura 1wk taji ana kiranta da Amarya tana tambaya taji a garin ana ta mata dariya anga karshen iyayi da jin dadi.
Kukan Maraici Tayi tana tuna so da gatan da iyayenta ke nuna mata amma ga yanda ta koma dare daya,ragowar kudinta ta duba saura Dubu Saba'in kacal Duk ta kashesu a siyi banza siyi Wofi Trolley dinta ta jawo ta shirya kayanta a ciki kaf sauran da bata so ta barsu,Handbag dinta ta zuba kayan kwalliyarta ciki tare da kudinta ta shirya tsab,sai da ta Bari an shiga masallaci sallar asuba ta sadada cikin duhu ta bar Garin bata tsaya ko ina ba sai garin Jos ta zarce Tasha inda zata shiga motar Abuja,a Tashar tayi sallar asuba da Asuba,ta dauko Toothpaste dinta da Brush tayi da ruwa pure water,a tashar ta siyi kosai da biredi tare da shayi hadin kauri taci ta koshi sannan ta wanke fuskarta da sabulunta harda shafa powder da jan baki sama Sama,ji tayi Driver yana cewa shigo yan mata zamu wuce,da sauri ta shiga ta zauna mota ta tashi sai Abuja.
Bikin Ahleef saura kwana uku ango ba zama Sun gama gayyatar abokai,ba abinda ba a gama ba na shiri,sun narkar da kudi,Abba yana sama a dakinsa yaji ance yazo ga manyan danginsa sunzo Maza biyu da mata biyu,ya fito Sun gaisa kenan sai ga yayan Momee da kaninta tare da yayarta,abin ya basu mamaki,bayan an gaisa anci ansha,suka ce abinda yake tafe damu ba komai bane sai akan auren Niima,Gaskiya bamuji dadi ba Sam da ilminku da komai zakuyi mata auren dole,jiya taje mana Tana kuka ita bata so auren dole za ayi mata,Abba ne ya dakatar dasu yace ku bari Niima tazo shima Ahleef yazo, Nan Momee ta Kirasu a waya,5mnt dukkansu suka zo, Momee tace gata nan gashi kuji daga bakinsu,Ahleef suka kalla kai kaine da kanka kake son Niima tsakani da Allah?da Sauri Ahleef yace ae,Niima kefa?kinje kin Kai mana kukanki yanzu maimaita a gaban kowa,ai kuwa ba tsoro Niima tace uhmm... Ahmm..Ina sonsa amma bada aure ba,ni ban shirya aure ba, kuma ni bana...Mari taji Abba ya kifa mata shi,Tana kuka tace wlh ni bana son aurensa,Abba Hawaye suka gangaro masa,Momee kam dama zancen ya dade da zuwa kunnenta,a hankali tace Baban Suhail kyaleta,ai dai kin tabbatar bakya sonsa ko? Niima tace ae,Abba yace ni zaki wulakanta sai ki fada mana sabo da me? Tana kuka tace bashi da asali wa ya sani ko shege ne,Momee Kuka kawai take shekawa, Abba yana Jin haka yace Ahleef kayi tawakali kayi hakuri,Allah zai baka wacce ta fita,ke kuma baza muyi miki baki ba amma ki sani sai kinyi nadama,yan Uwansa ya kalla yace na gode kuje kawai,jiki ba kwari suka tafi,itama Niima ranta Fari kal ta koma dakinta tana bugawa samari da yanmata frnds nata waya Tana Murna suma haka.
shiko Ahleef ya mike kenan ya yanke jiki ya fadi kasa sumamme,