Sashe 37
Jin Dadi Sabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da Rana Shukura Bata samu taci abinci ba sabo da a tsakar gida Yafendo ta fita ci,Sai yamma ta samu ta fito daga gidan Baki daya,gidan Aishalle taje ta dauki toothpaste da brush dinta tayi sannan ta karbi rancen dari biyu wajen Aishalle wai sai Mijinta Ahleef yazo zata biya ta fice abinta da su ta siya danwake da dafaffen kwai guda biyu taci a garin sannan ta tafi can lambu inda ta Saba zuwa hutawa sai dare ta dawo gidan Yafendo,sai da ta shiga kitchen dinsu taci tuwo da Miya sannan ta shige dakin Yafendo kasan gado, sai da su Indo suka zo zasuyi Dumamen tuwo suka ga ba malmala daya,Gaje tace watakil almajirai suka sata kin San yanzu Haka sukeyi,da sunga baka kusa sai su sace ma abinci.
Kullum Shukura haka takeyi har ta kwashe sati biyu a haka Allah bai sa an kamata ba,bashi kuwa yanzu ta karfi take kwatar kudi tace ta ranta sai Mijinta yazo zata biya,haka masu shaguna ma duk taci bashin sabulan wanka da wanki da wasu abubuwa duk tace sai Mijinta yazo,Haka bangaren masu abincin siyarwa,masu tsire da kifi,har chemist taci bashin paracetamol da maganin ciwon ciki,bashin always pad ma haka,kuma ba roka take a Bata bashi ba kawai shiga zatayi ta faki Ido ta kwashi abin ta fice tace kana Bina bashi sai Mijina yazo,idan kayi magana tace zata siyeka ka koma bawanta ko kuma ta siye shagon naka.
Kwana daya tsakani Yafendo da sassafe tace yau Kwalimar karkashin gadon ta zatayi ta gaji da Jin beraye na motsi gwara taga ko mene a ciki,Katuwar sandarta ta dakko da nufin idan taga bera ta buge shi,ta bude gado sukayi Ido biyu da Shukura,Yafendo tayi mugun tsorata tunaninta gamo da aljana tayi ta fito da gudu tana Kiran Iro da Yahaya,suka raho da gudu da saddunansu,tana nuna musu kasan gado suka dage har katifar da komai sai ga Shukura Shar Shar dake tayi wata kiba da kyau sabo da ciye ciye kuma Bata aikin komai sai tunanin Ahleef dake damunta.
Yahaya yace Yafendo ai Shukura ce,zo kuga masifa wajen Yafendo kamar zata ari Baki,zagi kuwa ba Wanda Bata yiwa Shukura ba sannan tace fada min tun yaushe kike a dakin Nan,Shukura ta zauna sosai ta Basu labari kaf kan gidan Megari da dalilin da yasa har take shugowa tana kwana,Iro yaji tausayin Shukura ko ba komai yar uwarsu ce ai Amma duk gari da dangi an ki ta an kyamaceta bayan Bata da kowa sai su,Nan Iro ya roki Yafendo a barta taci gaba da zama a gidan kafin Nan gaba aga me Allah zaiyi, Duk Masifar Yafendo tana tunawa da yar uwarta Inna tace to ta yarda Shukura ta zauna a gidan su dinga kwana tare Amma sai dai ta kwana a kasa kan karamar katifarta dake gefe.
Dadi ya kama Shukura ta dinga zuba Godiya sannan taje ta kwaso kayanta na wajen Aishalle ta dawo dasu gidan Yafendo, ta fara Taya Yafendo sukayi kwalimar tare Yafendo na Masifa ta Bata mata kasan gado da kazanta duk kwallon magoro,ga ludaya duk ansha Koko da fura a zube, duk aikin da Shukura keyi Yafendo cewa take Bata iya ba ita tafi kowa iyawa.
Da dare Tare da Shukura su Indo sukayi girki a gidan na dare,Ana tsakar gida Ana ci sai Yafendo tace sanata Elrufai an bashi zaben Gomna yanzu a kaduna ko? Shukura tace ai ba Senator bane Yafendo dama Gomna ne ya Kara ci,Nan Yafendo ta ce to yar karya wa Zaki gayawa to sanata ne yanzu yaci Gomna, da shine shugaban majalisar dattijai a Abuja,Shukura tace bafa haka bane,Nan Musu yakacame tsakanin Yafendo da Shukura,Duk su Iro suka ce Zancen Shukura ne gaskiya,Yafendo kuma ba a Isa ance an fita sani ba Nan ta fusata tace to ai na Dade da sanin Gwamna ne har za a Gaya min shi Gomna ne,Ganduje na Kano ma ba ya koma ba ta dole bai ci ba aka kwace dole,kasar Nan ba wani me gaskiya duk karya sukeyi sai yanzu nake nadamar guri'a ta Dana sawa Buhari.
Baki Shukura ta tabe tace tab ni kuwa Ina Buhari sabo da shi Mijina yake so,Ahleef shi yake so,Yafendo ta durma mata dundu a baya Dan ubanki Ina kika ga auren?a Ina Mijin yake Nan aka ce ciki kikayi aka dawo dake shine Zaki ishemu dama Kawu yace Alfahari kike tayi da Kwarton ki na birni kina sonsa tir da halinki,Iro yace Haba Yafendo kufa daina Zurfafawa wlh baku sani ba ni Ina gani kamar tana da gaskiya,Yahaya ma yace a dai bi a hankali lokaci Dole zai nuna.
Megari ya Dade Yana fama da ciwon son Shukura har yanzu bai hakura ba sai ya auri Shukura indai Yana Raye liman sai zuga shi yakeyi,yayin da Shukura ta kame kanta yanzu kullum tana gida ko fita Bata yi a garin sabo da ko Ina taci bashi,kuma gashi tana tsarewa Ahleef igiyoyinsa ko ba komai ita da auranta tasan idan Ahleef Yana Nan bazai bari a dinga kalle Masa mata ba shi yasa take tayashi.
Labarin Ahleef kuwa su Yafendo har sun gaji daji a bakin Shukura Kai kaf garin Babu Wanda bai San labarin Ahleef ba Mijin Shukura na bariki,manya da Yara sun sani har dattijai in kaji yanda ake tsara kyawunsa Ana dariya suna ganin Shukura karya take, akwai wani da yazo daga Birni garin yasha dinkin Shadda Shukura tana gani cikin bainar mutane tace irin style din Ahleef na wata farar shaddarsa,tana Nan a cikin kayana nazo da ita,,shike Nan samarin garin suke layin karbar aronta wajen Shukura Ana yi musu irin dinki kusan kowa a garin kana cewa Ayi Maka dinkin Ahleef kowa yasan mene har telolin wasu kauyukan kana ce musu ayi min dinkin Ahleef style to za ayi Maka,yanzu dinkin shi ke tashe a kauyukan, Shukura ita kanta tana mamaki kowa yasan Ahleef a Baki,Ahleef style.
Kuma abinda yasa suka Kara yarda cewa Shukura da gaske take Ahleef ko dai Mijinta ko farkanta ne yanda suka ga tana sa dinkunan maza iri iri har jallabiya tabbas na Namiji ne kuma da gani mutumin me kudi ne shi yasa hankalinsu ya kwanta suna ganin Shukura zata biya su bashin da taci da gaske take.
Shukura zaman hakuri kawai take da Yafendo sabo da fadanta kuma komai baka iya ba Babu abinda zakayi ka birgeta bare ta yaba.
Ahleef kuwa tun bayan tafiyarsa yake fama da son kasancewa da Shukuransa,ya kasa komai sai tunaninta,gashi ko a waya ba ita ba labarinta kuma harda Umma sun kasa fada Masa gaskiya,Idan ya gama wa Momee komai zai dawo sai Momee ta Kara tura shi wata kasar ba tare da ta bari ya tako Nigeria ba,gaba daya ya fita daga tunaninsa ya kasa gane wa Momee,Matarsa yake son kasancewa da ita,yanzu ya tabbatar tsananin son Shukura yake ba kadan ba,Momee kam tuni ta sanarwa Abba cewar Ahleef ya tafi wani aiki kasashe,Amma Matarsa ta zabi tafiya garinsu ta zauna da Yan uwanta kafin ya dawo sabo da ta gudu ta Bata musu rai Dole zata wanke kanta wajensu,Abba yace ahlmdllh yarinyar tayi tunani,Momee tayi Murmushi tare da cewa ai tana da tunani da kaina muka je na kaita sannan akayi musu bayanin aurenta nace Nan gaba ma zakuje dasu Baba shi mahaifin Mijin nata,wlh masu mutunci sun karramamu,Abba dadi ya kamashi yace sai Ahleef ya dawo kasar idan za a dakkota sai mu taru muje gaba daya aga juna ayi abinda ya dace Allah yayi Miki albarka kema,Momee ta waya tace na gode mijina,Abba hankali ya kwanta tunaninsa abinda Momee tace gaskiya ne kuma da sanin Ahleef.
Saudatu da Baba yanzu sunga Momee ta daina musu magana Sam tsakaninta dasu sai Harara da kallon banza,ganin haka suka yanke sanarwa Ahleef zasu bar musu gida,tunda Matar gidan da alama Bata kaunar zamansu yanzu.
AsmaBaffa
[7/22, 1:13 PM] Sis Asma: 🍱🍱🍱
JIN DADI SABO
41-45
Official
By
Asmabaffa
Saudatu da Baba da kansu suka sanarwa Ahleef sufa sun gode da taimakonsa Amma zasu bar gida ga abinda Momee ke Musu sannan suka bashi labarin abinda ya faru na tafiyar Shukura,Ran Ahleef idan yayi dubu to ya baci kamar zaiyi hauka,Farhan ya Kira a waya ya bashi Umarnin ya kwashe su Umma da kayansu ya kaisu can Wani sabon gidansa daya siya kwana Nan me shegen kyau ba abinda Babu a gidan na rayuwa. Farhan ba Bata lokaci yaje ya kwashe kayan sawarsu ya Kai can gidan,ya zuba kayan abinci da komai sannan ya kawo masu aiki mata su biyar da maza sabo da su Umma suji dadin rayuwa a gidan girki kawai Umma zatayi ba abinda zatayi.
Sun Sha mamaki da murna suna sawa dansu albarka Babu adadi,Momee kuwa tunda taga Farhan ne ya dauke su tasan Umarnin Ahleef ne tace Umma ta gaida aisha Haka kawai tsofaffi sunzo sun rikita min gida baku San wahalar yaro ba kuce zaku Sha dadinsa.
Mubaraq yayan su Hafcy ya nacewa Niima har sai da ta fara kulashi ta karfi,tun Bata damu dashi ba har ta fara sonsa,Mama tafi kowa Murna zasu ci kudin su Momee tace saura ku Hafcy ko ke ko Zahra ku dage Ahleef ya auri daya ko zamu samu kudin da yawa sabo da shine me kudin, ko mata dari yayiwa ciki suka haife Babu ruwanmu ku aureshi kudi muke nema ba wani tarbiya ba.
Hafcy tace nima Dana yi tunani Haka na gani kawai ayi asan abin yi, tunda mun sallami shegiyar matar tasa.
Kullum Shukura haka takeyi har ta kwashe sati biyu a haka Allah bai sa an kamata ba,bashi kuwa yanzu ta karfi take kwatar kudi tace ta ranta sai Mijinta yazo zata biya,haka masu shaguna ma duk taci bashin sabulan wanka da wanki da wasu abubuwa duk tace sai Mijinta yazo,Haka bangaren masu abincin siyarwa,masu tsire da kifi,har chemist taci bashin paracetamol da maganin ciwon ciki,bashin always pad ma haka,kuma ba roka take a Bata bashi ba kawai shiga zatayi ta faki Ido ta kwashi abin ta fice tace kana Bina bashi sai Mijina yazo,idan kayi magana tace zata siyeka ka koma bawanta ko kuma ta siye shagon naka.
Kwana daya tsakani Yafendo da sassafe tace yau Kwalimar karkashin gadon ta zatayi ta gaji da Jin beraye na motsi gwara taga ko mene a ciki,Katuwar sandarta ta dakko da nufin idan taga bera ta buge shi,ta bude gado sukayi Ido biyu da Shukura,Yafendo tayi mugun tsorata tunaninta gamo da aljana tayi ta fito da gudu tana Kiran Iro da Yahaya,suka raho da gudu da saddunansu,tana nuna musu kasan gado suka dage har katifar da komai sai ga Shukura Shar Shar dake tayi wata kiba da kyau sabo da ciye ciye kuma Bata aikin komai sai tunanin Ahleef dake damunta.
Yahaya yace Yafendo ai Shukura ce,zo kuga masifa wajen Yafendo kamar zata ari Baki,zagi kuwa ba Wanda Bata yiwa Shukura ba sannan tace fada min tun yaushe kike a dakin Nan,Shukura ta zauna sosai ta Basu labari kaf kan gidan Megari da dalilin da yasa har take shugowa tana kwana,Iro yaji tausayin Shukura ko ba komai yar uwarsu ce ai Amma duk gari da dangi an ki ta an kyamaceta bayan Bata da kowa sai su,Nan Iro ya roki Yafendo a barta taci gaba da zama a gidan kafin Nan gaba aga me Allah zaiyi, Duk Masifar Yafendo tana tunawa da yar uwarta Inna tace to ta yarda Shukura ta zauna a gidan su dinga kwana tare Amma sai dai ta kwana a kasa kan karamar katifarta dake gefe.
Dadi ya kama Shukura ta dinga zuba Godiya sannan taje ta kwaso kayanta na wajen Aishalle ta dawo dasu gidan Yafendo, ta fara Taya Yafendo sukayi kwalimar tare Yafendo na Masifa ta Bata mata kasan gado da kazanta duk kwallon magoro,ga ludaya duk ansha Koko da fura a zube, duk aikin da Shukura keyi Yafendo cewa take Bata iya ba ita tafi kowa iyawa.
Da dare Tare da Shukura su Indo sukayi girki a gidan na dare,Ana tsakar gida Ana ci sai Yafendo tace sanata Elrufai an bashi zaben Gomna yanzu a kaduna ko? Shukura tace ai ba Senator bane Yafendo dama Gomna ne ya Kara ci,Nan Yafendo ta ce to yar karya wa Zaki gayawa to sanata ne yanzu yaci Gomna, da shine shugaban majalisar dattijai a Abuja,Shukura tace bafa haka bane,Nan Musu yakacame tsakanin Yafendo da Shukura,Duk su Iro suka ce Zancen Shukura ne gaskiya,Yafendo kuma ba a Isa ance an fita sani ba Nan ta fusata tace to ai na Dade da sanin Gwamna ne har za a Gaya min shi Gomna ne,Ganduje na Kano ma ba ya koma ba ta dole bai ci ba aka kwace dole,kasar Nan ba wani me gaskiya duk karya sukeyi sai yanzu nake nadamar guri'a ta Dana sawa Buhari.
Baki Shukura ta tabe tace tab ni kuwa Ina Buhari sabo da shi Mijina yake so,Ahleef shi yake so,Yafendo ta durma mata dundu a baya Dan ubanki Ina kika ga auren?a Ina Mijin yake Nan aka ce ciki kikayi aka dawo dake shine Zaki ishemu dama Kawu yace Alfahari kike tayi da Kwarton ki na birni kina sonsa tir da halinki,Iro yace Haba Yafendo kufa daina Zurfafawa wlh baku sani ba ni Ina gani kamar tana da gaskiya,Yahaya ma yace a dai bi a hankali lokaci Dole zai nuna.
Megari ya Dade Yana fama da ciwon son Shukura har yanzu bai hakura ba sai ya auri Shukura indai Yana Raye liman sai zuga shi yakeyi,yayin da Shukura ta kame kanta yanzu kullum tana gida ko fita Bata yi a garin sabo da ko Ina taci bashi,kuma gashi tana tsarewa Ahleef igiyoyinsa ko ba komai ita da auranta tasan idan Ahleef Yana Nan bazai bari a dinga kalle Masa mata ba shi yasa take tayashi.
Labarin Ahleef kuwa su Yafendo har sun gaji daji a bakin Shukura Kai kaf garin Babu Wanda bai San labarin Ahleef ba Mijin Shukura na bariki,manya da Yara sun sani har dattijai in kaji yanda ake tsara kyawunsa Ana dariya suna ganin Shukura karya take, akwai wani da yazo daga Birni garin yasha dinkin Shadda Shukura tana gani cikin bainar mutane tace irin style din Ahleef na wata farar shaddarsa,tana Nan a cikin kayana nazo da ita,,shike Nan samarin garin suke layin karbar aronta wajen Shukura Ana yi musu irin dinki kusan kowa a garin kana cewa Ayi Maka dinkin Ahleef kowa yasan mene har telolin wasu kauyukan kana ce musu ayi min dinkin Ahleef style to za ayi Maka,yanzu dinkin shi ke tashe a kauyukan, Shukura ita kanta tana mamaki kowa yasan Ahleef a Baki,Ahleef style.
Kuma abinda yasa suka Kara yarda cewa Shukura da gaske take Ahleef ko dai Mijinta ko farkanta ne yanda suka ga tana sa dinkunan maza iri iri har jallabiya tabbas na Namiji ne kuma da gani mutumin me kudi ne shi yasa hankalinsu ya kwanta suna ganin Shukura zata biya su bashin da taci da gaske take.
Shukura zaman hakuri kawai take da Yafendo sabo da fadanta kuma komai baka iya ba Babu abinda zakayi ka birgeta bare ta yaba.
Ahleef kuwa tun bayan tafiyarsa yake fama da son kasancewa da Shukuransa,ya kasa komai sai tunaninta,gashi ko a waya ba ita ba labarinta kuma harda Umma sun kasa fada Masa gaskiya,Idan ya gama wa Momee komai zai dawo sai Momee ta Kara tura shi wata kasar ba tare da ta bari ya tako Nigeria ba,gaba daya ya fita daga tunaninsa ya kasa gane wa Momee,Matarsa yake son kasancewa da ita,yanzu ya tabbatar tsananin son Shukura yake ba kadan ba,Momee kam tuni ta sanarwa Abba cewar Ahleef ya tafi wani aiki kasashe,Amma Matarsa ta zabi tafiya garinsu ta zauna da Yan uwanta kafin ya dawo sabo da ta gudu ta Bata musu rai Dole zata wanke kanta wajensu,Abba yace ahlmdllh yarinyar tayi tunani,Momee tayi Murmushi tare da cewa ai tana da tunani da kaina muka je na kaita sannan akayi musu bayanin aurenta nace Nan gaba ma zakuje dasu Baba shi mahaifin Mijin nata,wlh masu mutunci sun karramamu,Abba dadi ya kamashi yace sai Ahleef ya dawo kasar idan za a dakkota sai mu taru muje gaba daya aga juna ayi abinda ya dace Allah yayi Miki albarka kema,Momee ta waya tace na gode mijina,Abba hankali ya kwanta tunaninsa abinda Momee tace gaskiya ne kuma da sanin Ahleef.
Saudatu da Baba yanzu sunga Momee ta daina musu magana Sam tsakaninta dasu sai Harara da kallon banza,ganin haka suka yanke sanarwa Ahleef zasu bar musu gida,tunda Matar gidan da alama Bata kaunar zamansu yanzu.
AsmaBaffa
[7/22, 1:13 PM] Sis Asma: 🍱🍱🍱
JIN DADI SABO
41-45
Official
By
Asmabaffa
Saudatu da Baba da kansu suka sanarwa Ahleef sufa sun gode da taimakonsa Amma zasu bar gida ga abinda Momee ke Musu sannan suka bashi labarin abinda ya faru na tafiyar Shukura,Ran Ahleef idan yayi dubu to ya baci kamar zaiyi hauka,Farhan ya Kira a waya ya bashi Umarnin ya kwashe su Umma da kayansu ya kaisu can Wani sabon gidansa daya siya kwana Nan me shegen kyau ba abinda Babu a gidan na rayuwa. Farhan ba Bata lokaci yaje ya kwashe kayan sawarsu ya Kai can gidan,ya zuba kayan abinci da komai sannan ya kawo masu aiki mata su biyar da maza sabo da su Umma suji dadin rayuwa a gidan girki kawai Umma zatayi ba abinda zatayi.
Sun Sha mamaki da murna suna sawa dansu albarka Babu adadi,Momee kuwa tunda taga Farhan ne ya dauke su tasan Umarnin Ahleef ne tace Umma ta gaida aisha Haka kawai tsofaffi sunzo sun rikita min gida baku San wahalar yaro ba kuce zaku Sha dadinsa.
Mubaraq yayan su Hafcy ya nacewa Niima har sai da ta fara kulashi ta karfi,tun Bata damu dashi ba har ta fara sonsa,Mama tafi kowa Murna zasu ci kudin su Momee tace saura ku Hafcy ko ke ko Zahra ku dage Ahleef ya auri daya ko zamu samu kudin da yawa sabo da shine me kudin, ko mata dari yayiwa ciki suka haife Babu ruwanmu ku aureshi kudi muke nema ba wani tarbiya ba.
Hafcy tace nima Dana yi tunani Haka na gani kawai ayi asan abin yi, tunda mun sallami shegiyar matar tasa.