← Book details Jin Dadi Sabo Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 30 OF 59

Sashe 30

Jin Dadi Sabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Da sauri Su Baba suka rankaya tare da kaka suka kirawo Abba gefe suka labarta masa komai murna wajen Abba ba a magana,yace ayiwa Shukura godiya ta fitar dasu kunya,farko Niima ce ta tozarta su aka fasa yau ma again kai Alhmdllh.Abba ne yace aci Gaba da Khuduba,Ahleef dai wani takaici ne ya kara ziyartarsa tunaninsa daidaitawa akayi da iyayen Nafeesa za a daura auren,idonsa yayi jajir Sabo da bacin rai,Baba da Kaka sune na Shukura,Abba da Yayan Momee kuma na Ahleef, nan take aka Naura Auren Ahleef da Shukura kan Sadaki dubu dari,Abba shi ya biya sadaki,Maroka Masu kade kade ana ta yi.

Ana ta kara Sanarwa da daurin aure ya dauru,mutane Sun sheda, Shukura saida tayi Sujjada ta godewa Allah,sannan ta karbi biro hannun wani ta rubuta short note a jikin yagin kwalin taba data tsinta a kasa.
Baba ka fadawa Ahleef da sauran Masu sona na tafi gidan kawata a Apo qrts cikin Abuja ina nan zan dawo gobe.wani saurayi ta bawa tace idan yaga Baba ko Ahleef ango ko Abba ya bashi,taxi ta shiga tayi tafiyarta cike da farin ciki.

Ahleef kuwa yaji dadin daura aure da Shukura duk da ba soyayya Suke ba,amma taya za a daura aure kuma Sun San Shukura ta bace ? Amma kuma wani irin farin ciki yake ji marar misaltuwa.Farhan da sauran abokai ma haka,labari tuni ya kai kunnen Momee amma taji haushi dole sai da aka daura da jarababba Shukura Ai gwara a kyale Ahleef ba aure akan a bashi Shukura.

Su Niima,Hafcy,Islam etc basu ji dadin lamarin ba, Zahra kuwa tace sai ta raba Auren sannu a hankali.
kowa da abinda yake furtawa har akayi hotuna da komai mutane suka watse sai ango da abokanansa shakikai suna guess house dinsa ana ta tsokanarsa musamamman da Baba ya bashi dan Note din da Shukura ta rubuta.Kaka da Jamilu an kaisu masauki can gidansu Farhan aka kaisu Sabo da matsalar Momee.

Angwaye Suna zaune sai tsokanar Ahleef Sukeyi dan gatan Amarya da kanta tazo wajen ta bada Umarni a daura da ita,Shukura ta birge mutane ta fitar da ango kunya tayi halacci ana ta mata addua,Nafeesa kusan haukacewa tayi da taji ba da ita aka daura ba, laifin iyayenta take gani,fushi tayi tace wlh kuma baraki yanzu ta soma tunda su suka jawo ba a daura da ita ba.

Su Niima Dasu Momee Sai tuge kwalliyarsu sukayi tunda da shukura aka daura to baza suyi kwalliyar bikin ba.

Shukura kuma gidan wata Fauziyya yar makarantarsu taje Suna dan shiri da ita kuma Fauziyya nutsatsiyace ga kirki da wayewa gata ta Iya kwalliya, abinda yasa Shukura taje can Sabo da Momee sannan tafi so ango ya ganta Amarya kamar kowacce.
Ango ya rude kawai shi Shukura yake son gani,ba wai dan tana Amaryarsa ba Dan ya dade bai ganta ba, kuma yana so yaji ina aka kaita wacce rayuwa ta tsinci kanta,yana son ganin lafiyarta.

AsmaBaffa
[7/22, 1:13 PM] Sis Asma: 🍱🍱🍱
JIN DADI SABO

26-30

Official

By
AsmaBaffa

JANNAT,MAMAN MEENAT, QUEEN KK da BBY LUV
Page nakune.

Fauziyya ta damu Shukura da zancen ina kika tafi ana ta cewa karuwanci kika tafi tafi,Shukura tace nasan Latifa ce ta fada bani da lokacin wannan ni yanzu ma da kika Sani Amarya ce wlh so nake ki karbo min rancen Dubu talatin tunda gidanku Masu kudi ne gobe zan baki, so nake na fito a amarya ta kamar kowacce,mamaki Fauziyya tayi ace kamar yar Shukura da aure abin mamaki,a fili tace to Mama ta bani dubu hamsim zan kai mata bank,zan cire talatin ciki na baki zuwa gobe lallai ki karbo wurin ango a sa mata kudinta ba tare da ta gane ba,Shukura tace Inshaallah,yanzu ta Ina za a fara yamma nayi,gidan gyaran jiki zamuje Masu sauki ayi miki na rana daya Kafin ango yazo ya bada kudin na 3mnths,Fauziyya Mamansu ta fadawa komai na iya bikin Shukura,Mama tace kuje gidan sady me gyara tayi mata kyauta ni zan biya,da murna suka tafi driver ya kaisu,Sady tace yanzu za ayi miki gobe ma haka,idan Miji kuma ya yarda sai kiyi ta zuwa har tsawon 2-3mths,kaf jikinta aka yiwa gyaran, sai kuma gashinta yasha uban gyara sai kyalli da sheki.

Lalle aka Zana mata na Amare,da yake Fara ce sai kaji kamar ka saceta tsabar kyau,sai 8pm suka gama sannan,Maman Fauziyya tace saura tsumi kuje gidan Hajiya Mariya itace me tsuma Amare yanda ya dace,basu koma gida ba sai da suka je karbo maganin kala kala Wanda ya dace da Amarya wacce bata taba aure ba tayi amfani dasu,a gajiye suka koma gida, Maman Fauziyya tausayin Shukura takeyi shi yasa bata bari ta kashe kudinta ba albarkacin kawar yarta ce yasa tayi mata,Sabo da haka sai kawai suka siyo ready Made wata Riga ta dubu goma wata yar ubansu,Takalmi da jaka,Sai lace da suka siyo dan dubu goma suka bawa tela Emergency zasu karba gobe da safe komai Sun tsarashi Ahleef ji yake kamar ya zunguro gobe tayi yaga Shukura, da kyar bacci ya saceshi sabo da Murna.

Washe gari da sassafe suka koma gyaran jiki aka yi mata etc.
Sai 5pm Shukura zata ta nemi inda Ahleef yake ba tare da ta koma gidan Momee ba.
Ahleef da wuri ya tashi yana ta duba agogo ko zaiga Shukura,har Bakin gate yake fitowa ya tsaya amma Shuru ya koma Bedroom ta Window kawai yake kalon kofar har 2pm ta wuce sunyi Sallah ana hira amma banda Ahleef ya kasa cin abinci,4pm yana yin Sallah ya fada toilet yayi wanka yasa wata Shadda fara kar dinkin zamani,ba karamin kyau yayi ba sumarsa tasha gyara kamshi kawai yakeyi da sheki,yau harda coka hula baka a gaban goshi,yasa Bakin takalmi,kowa yasan ba karya ya hadu karshen karshe,da sauri ya sakko kasa da niyyar zuwa ya binciko Shukura duk inda take,Farhan da sauran Frnds suka kulle kofar da key zasu tsokane shi,ai kuwa ya dinga masifa suka ki budewa har 5:44pm sannan suka bude suna masa dariya,tsaki yaja tare da ficewa.

Yana fitowa inda motocinsu suke,Sai ga Fauziyya taci uban wanka dake itama me kyau ce fara amma ba kar ba, Sai wata budurwa makwaftan su Fauziyya itama tasha wanka tace sai ta bisu taga bikin Masu kyau da kudi Zeenat kenan, Shukura ce ke binsu a baya tasha doguwar rigar material black and White kamar tasan Ahleef shima Black and White yasa, dinkin irin na Amare ba karamin kyau ta tsula ba, Bata Sa gogoro ba, Dan siririn gyalen Rigar sharara ta yana a saman kanta, ba kowa zai gane Shukura ba zai rantse bakuwar balarabiya ce ko yar India.
takalminta me dan tudu black dai dai tana tafiya dos dos har pose din ta black,Ahleef kallo daya ya mata ya gane abarsa.

Tsayawa yayi jikin motar tare da kafeta da kallo kana ya sakar mata murmushi me kayatarwa,Shukura kunya ta kamata kawai sai ta sadda kai kasa tana tafiya,Su Fauziyya dariya ma ta basu,wani farin ciki ya lullubesu gaba daya kowannensu yana ji kamar ya hadiya dan uwansa,Dago kanta tayi a hankali tana murmushi idanunsu suka sarke da juna,kafin ta karaso shima ya taka yaje har inda take,Su Fauziyya suka gaisar da shi ya amsa,yace su dan jirashi a garden,hannun Shukura ya rike kawai ya jata suka nufi daya Part din,Shukura kuma cewa take Yaya ayi party mu gaskiya,yace yau da kafa daya zanyi rawa cewar Ahleef,dariya tayi tare da cewa kana rawa da kafa daya ni kuma ina dariya da hakori daya,muje muyi wata magana ya furta.

a palo ya zauna saman kujera itama ta samu one Seater, bani lbr me ya faru Bayan sun saceki ? Tiryan tiryan ta bashi labarin komai shi kuma ya kafeta da ido,zuciyarsa cike da tausayinta,waya ya zaro tare da kiran Abba ya sanar masa ya za ayi da Amarya kar Momee ta bada matsala, Abba yace karka damu dole za a kaita gidanka yanzu so nake jibi mu shirya da kai tare da Shukura, Baba da Ummanka muje kauyen yarinyar a sanar musu sannan ta zauna kamar 2wks sai danginta su kawota gidanka kamar ko wacce Amarya,Momee fa Abba ? Kyaleta wannan zanyi maganinta karka damu,bayan ya gama wayar Shukura tayi bacci ashe,a hankali ya taka zuwa gabanta yana kare mata kallo tun daga sama zuwa kasa,lallenta ne ya tafi da hankalinsa ya shiga kallo yana yabawa a zuciyarsa,Kasa daurewa yayi har saida ya rike hannunta yana shafawa,rigarta ya yaye kadan ya shiga kallon Zanen lallen dake kafarta,yafi 10mnt yana kallonta farin ciki yana ratsashi.

Farhan ya kira a waya yaje wajen su Fauziyya ya kaisu gida wajen Umma, shi anjima zai taho da Shukura ta samesu a can.
Yasa an masa take away na abinci yasan tana tashi sai tace abinci Zata ci,sai wuraren magrib ta farka lokacin Ahleef tuni Sun fita Masallaci,bakinta ta wanke yau Bata sallah shi yasa ta zauna tana jiran Ango ya dawo ita kuma ta tafi,
Ahleef ya dan jima sannan ya dawo direct wurin Shukura ya nufa,a Zaune ya isketa,tana ganin ya shigo tace Yaya yunwa,ba tare da yayi magana ba ya nuna mata ledar abunci,a nutse ta zauna taci abinta a hankali har ta gama yana kallonta kasa kasa,Toilet ta shiga tare da wanke hannayenta ta gyara kwalliyarta sannan ta fito,muje na kaiki wurin kawayenki can Wurin Umma suke,bata yi musu ba suka jera kamar ka sace su, kayan jikinsu kamar anko sukayi dama,Escort dinsa ne da motoci Sun kai takwas suka shiga,Ango da Amarya suna Bayan mota Sun lafe abinsu,Sauran Frnds nasa da suka ga Shukura sai mamaki suke dama haka take me kyau,lallai Ahleef yayi dace.
Chapter 30 · 0% Book details