← Book details Jin Dadi Sabo Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 49 OF 59

Sashe 49

Jin Dadi Sabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ahleef kuwa ya gaji da jira har ya mike zai je ya daukota sai yaga ta banko kofa bata kulashi ba tace ga tea Nan Bari nayi wanka,ta fada toilet tayi wanka da brush,tana fitowa ta shirya tana zuba kamshi cikin kayan bacci masu daukan hankali, Ahleef tunda ya Shiga yaki fitowa daga wankan da wuri,dama shi wankansa sai ya Dade sosai,Shukura taje jikin kofar tace Ni zanyi baccina Kuma idan na kwanta bazan tashi na hada ma tea ba,karma ka tasheni,Wai wayo ta hada Nan,Ahleef Bai gane ba yace no karkiyi bacci pls shugo toilet din ki jira Ni, naki Ni bazan shugo ba ta furta da Shagwaba,Yana fitowa ta zuba Masa idonta tana Kare wa halittarsa kallo tana dauke Kai Dan kar ya gano ta,Yana shiryawa yace bini muyi nafeela,Shukura tace Ni dai yau Allah bazan iya ba,bacci nake ji,sai dai kayi Kai kadai Kuma bazan jiraka ba zanyi bacci na kana tayar da sallah zanyi bacci abina, yau Sallar ma baza ki Bari ayi ba.

Ni Bari nayi tawa Ni kadai,zai tayar kenan Shukura taje tayi tsalle ta bayansa ta daneshi du ta makalkaleshi tana dariya tace Allah baza kayi ba kaima kazo ka fini samun Lada,fafur taki sauka Dole ya hakura da sallar, tea ta hada Masa ta Mika masa Yana gefen Bed ya kunna tv ya kamo tashar ball Yana kallo Yana Shan tea dinsa Shukura tayi matashi da cinyarsa, yace Bari mu kallon match din Nan sai mu kwanta ko?

Shukura tace sam wannan tsinanniyar ball za a kalla Ni bana gane me sukeyi,a rasa abinda za a kalla sai ball,wancen Dan iskan Messi din me Ido kamar na tururuwa su zamu kalla ta Danna remote ta kashe tv,ta karbe tea din dake hannun Ahleef yasha rabi kawai ta kwankwade Rabin tare cewa sai yanga kake kwanta bacci to za ayi Kuma karka tasheni, ta kwanta abinta Ahleef Yana Murmushi ya kwanta suna facing din juna,Bai taba ta ba sabo da tunaninsa zata Hana ta kama kukan da ta Saba,sai ko hugging baiyi ba Yana tunanin Taya zai bullo Mata,Shukura ta kashe light tare da rufe Ido Wai tayi bacci ita, a hankali Ahleef ya dawo da ita jikinsa sai ko yaga ta Kara makaleshi Bata ce komai ba, gashinta me tsayi da santsi ya warware ya nutsa yatsunsa ciki Yana shafa Mata a hankali cikin salon kwarewa.

Shukura idonta ta lumshe da kanta ta fara kissing dinsa tun tanayin kadan ta koma so Deep,sai Rada take Masa a kunne tana Masa wasanni a kunne da harshenta,Ahleef ya rude Basu San sanda suka zarewa juna Kaya ba,kowannensu cikin kwarewa da salon bajinta yake sarrafa Dan uwansa suna jiyar da juna dadi,sosai Shukura ta ba da hadin Kai duk da yauma taji zafi Amma ba sosai ba, Ahleef yau sabo da sweet din Shukura sai da yayi hawayen dadi,Hawaye sosai, Bayan sun tsarkake jikinsu bacci me karfi ya kwashesu, 2:30am Ahleef ya farka da Jarabarsa sallar dare ya Saba Yana yi tare da Shukura Amma wannan karon Yana tashinta yace yau ba sunnar Nafeela za ayi ba, Shukura da Tasha tsumin Umma Haka ta bada hadin Kai suka Kara darje juna, da Asuba ma Haka suka sake sabo Shukura tana Jin zafi Amma sabo da maita mukus takeyi Bata kin yarda sai dai tana cin uban gashi kamar zata Kone wajen da ruwan zafi,Ahleef kuwa kawai kwasar harkoki yake abinsa, ranar ko schl Shukura Bata je ba,Kuma tunda suka fito suka gaida Umma da Baba suka koma dakinsu abinci ma sai dai Ahleef yaje ya ebo musu ya dawo, a room suka yini sai yamma Bayan Sallar laasar suka fito,Baba sai fada yakewa Ahleef yau Bai samu jam'i ba ko daya, Shukura tace ai yanzu Baba zaije Magrib da Isha dazu ma kansa ne yake ta ciwo tun jiya sai yanzu yaji sauki,Baba yace Kash Allah ya sawwake kasha magani ko asibiti zaka je? Ido suka hada da Shukura suka yiwa juna signa sannan yace ai dazu Naga maganin a jakata na Sha shine ma na Samu sauki, Shukura tace da har zanzo na fada muku Baba yace Wai kar na fada tun jiya yasha wahala gaskiya,Umma ita kanta ta yarda da Shukura tace idan ba sakarci irin naku ba mutum ya kwana Yana ciwon Kai baza ki fada ba,Dazu kazo ka ebi abinci safe da Rana wa yaci?

Ahleef yace tun jiya take ta faman kuka sabo da ina ciwon Kai taki cin komai shine Dana ji sauki sauki nazo na ebar mata, Umma tace eyya to Allah bada lfy, Suka ce Ameen,Ahleef yace Bari zanje wurin Farhan anjima zan dawo,Hannun Shukura ya kamo yace ko Zaki je? Umma tace ba inda zata je jiya kunce bakuyi bacci ba kana cuta yanzu ai gwara ta huta,Shukura tace Umma Dan Allah zanje pls Kinga fa na Dade ban fita ba,Ke da idonki tunda Zaki iya sai kuje,da sauri taje ta shirya cikin wani arnen lace dinta milk da ratsin Orange takalmi da jaka tare da mayafi Orange tayi Masifar kyau, Ahleef kuwa cikin Milk shadda me tsada Tasha dinkin zamani na Matasa Yan gayu, sai kamshi sukeyi suka yiwa su Baba sallama suka fita hannunsu rike da juna,Ahleef yace dama ba wajen Farhan zanje bafa yawo zamuyi a kafa muga unguwar Nan, Umma idan ta sani maybe tace baza kije ba,Shukura tace Amma naji dadi, weather me dadi suna tafiya a hankali suna hirarsu ta masoya suna kwasar fresh air abinsu dake Abuja ne ba ruwan wani da wani kowa ya gansu sai sun birge, suna shaukinsu Sai ga Farhan da mota zaije gidansu ya wuce ya dawo baya tare da sauke Glass kasa Yana dariya yace Allah ya shiryeka Dan Iska, hannu Ahleef ya Mika Masa suka tafa,Shukura ma ta gaidashi,yace to kuzo mu koma dama gidanku zanje,Ahleef yace wlh baza mu koma ba sai dai kaje ka jira mu a gida sai sanda muka dawo ko ka tafi gobe ka dawo ko Nazo amma baka Isa mun koma ba,yawo muka fito da Honey,Farhan yace zaka sani ne Nima wlh indai nayi aure sai na Rama suna dariya yaja mota ya tafi gidan su Ahleef,Umma da Baba basusan a kafa suka fita yawo ba sai Farhan ne ya tona su.

Wata sabuwa Bayan kwananki kadan Ciwon Koda me tsanani ya kama Momee,kullum suna hanyar asibiti Ana cinye wannan dukiya,samari da wasu Yan film tare da karuwai sunga Momee kudi Babu ga ciwo ya kamata suka zare jikinsu ko dubiya ba wacce ta leko,Haka dangin Momee sunji labari Amma ko leke,Niima tayi kuka har ta godewa Allah,Latifa kuwa ba ruwanta kullum tana yawonta,Niima da katon ciki Haka take kula da Momee,Yan aiki duk Babu sun arce, Ahleef kuwa bai da labari sabo da tunda ya tafi bai sake leko su ba

Bayan wasu watanni Ahleef Alhmdllh ya sake Zama wani Hamshakin me kudi na gasken gaske,Haka Allah yayi shi komai ya taba sai yayi albarka, tuni ya Gina musu rantsatsen gidan da Babu irinsa, Kuma gidan da Farhan ya siyar ya bashi tuni yaje ya siyawa Farhan Wanda ya fishi kyauta, yanzu duk inda Ahleef yake sai kaga Shukura a gefensa yawancin meeting ko wani abu da ita yake zuwa,Kuma duk takardun da zai cike Yana rubuta ta a Itace magajiyarsa Next of kin, Shukura ta Kara wani wayewa ta goge sosai,sun kusa zana waec da Neco, Ana yawan Nuna Ahleef a gidan Tv ko radio yanda yake bawa kasa gudun mawa Yana taimakawa Marasa karfi.

Bayan Shukura sun gama ssce exam Visa Ahleef yayiwa Shukura tare da shi zuwa London,Umma da Baba Kuma ya biya misu Saudiya, Bai San wanne Hali su Momee ke ciki ba suka dage zuwa London,Suna cikin jirgi Shukura ta lafe a jikinsa tana bacci abinta cikin kwanciyar hankali sai wani lallabata Ahleef keyi,da dare misalin 8pm suka Isa London,mota suka shiga zuwa masaukinsu wani katafaren Hotel,tun a taxi Ahleef ya tsaya yasiyawa Shukura Lemo me shegen dadi da wani snacks, Shukura tunda suka sauka taji Niima a garin ga wani dadin sanyi,kasa kamar aljannar duniya,tana kora lemo tace My Hero Allah wadai da halin shugabanninmu ,dariya Ahleef ya dingayi yace Babu kyau fa zagin shugaba kin sani,me suka Miki? Shukura ta Kara daga lemo ta zuka sannan tace Nigeria baza mu taba ci gaba ba har Kiyama ta tsaya,gamu da kudi Amma gaba daya da shugaban nin da mu Yan kasar Babu na gari sai dai dai,yanzu jibi kasar Nan kamshinta ma daban ne,kalli Amma mu sai dai a sace kudin kasar,na kasa ma ko tallafi shugaba ya bada a raba kafin yazo hannun talakawa duk sun cinye kudin.

Ahleef ya kafeta da kallo tana ta ciye ciyenta Yana Kara Jin wani sonta da shaawarta na ratsashi, ba tare da ta kalleshi ba tace kallonfa na mene,rungumeta yayi a jikinsa gaba daya tare da Rada Mata I Love u Honey, Murmushi ta saki tace me too Sweety.
Suna zuwa Hotel dama tuni ya musu booking da karamar trolley dinsu suka wuce ciki.

Momee kwance a gadon asibiti Niima da Dan karamin cikinta tana aikin jinya sai masifa take zazzagawa Momee, Dan Allah Momee Ni ki karbi magani Kisha sai wahalar Dani kike duk kokarin da nake Bakya gani,Hawaye ya zubowa Momee tace Wai Ni kikewa tsawa Haka Niima? Cikin radadin ciwo Hawaye ya zubo wa Momee,da kyar tace Ina...na...na....Latifa?
Tsaki Niima taja kadan sannan tace tana yawon iskancinta can ai kin sani, Momee da kyar tace Ina zamana lfy na lalata halina,na dauki mutanen banza na cusasu a jikina,gashi yanzu ko arzikin dubiya ban samu ba,Maman su Hafcy ma Wai itace ta kasa ko leko Ni sabo da yanzu bamu da kudi,Niima tace sai yanzu nake Nadama Momee Dana ki aurar Ahleef,ga kyau,ga Kudi,ga kyan Hali,karshe naje naso Mubaraq Wanda shine ya lalata min rayuwata Niima ta fashe da kuka tare da durkushewa a kasa tana na cuci kaina,kema Momee duk ke kika jawo mana.
Chapter 49 · 0% Book details