Sashe 9
Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A hankali Ummy ta tura kofar d’akin, a kwance taganshi a kasan d’akin daga can gefen gado, yana kwance akan sallaya yana bacci, takan rasa inda zata sa kanta a koda yaushe in taganshi a kwance akasa, abinda ke damunta shine inhar bacci dare zaiyi bazaki taba ganinsa akan gado ba, sannan a kasan ma kwanciya kawai yake, amma in gari ya waye sai kiga ya kwanta akan gado.
Kusa dashi ta karasa ta dauko karamin bedsheets a gefen gadonsa sannan ta lulubamai, jiki a sanyaye ta juya ta fita.
Tana rufe kofar yana bude idanunsa, kofar ya kalla dan tun da ta shigo ya farka, idanunsa ne suka canza launi a hankali ya maidasu ya rufe saboda tsananin tausayin da yakeji na mahaifiyarsa.
Mikewa yai ya hau kan gado yai wata kwanciya a dukunkune, a hankali idanunsa suka zubo da wasu zafaffan hawaye.
Ummy tana fita ta sauka kasa, kitchen ta shiga inda Ameera da Aina’u suke girkin abincin safe.
Tace “wannan jagwalgwalo har mun gaji da jiransa, sai kace wanda ake mana abincin arziki.”
Ameera tace “Ummy kin dage sai munyi girki da weekend kinga kuwa kome muka dafa sai kuyi hakuri kuci.”
Ummy tace “ai na gama kula dake sam bakyasan yin girki, yanzu kuwa kinjama kanki duk asabar da lahadi ke zaki dinga yin girkin safe.”
Ameera tace “Shikenan Ummy sai mudingacin Indomie.”
Aina tai dariya tace “Lalai Ameera, Abban zaki ba indomie?”
Ummy ta juya tana murmushi, falo ta zauna sannan ta d’au waya ta kira Aunty Nana.
Bayan sun gama gaisawa tace “muna nan da Aina’u munatashan hutu.”
Aunty Nana tace “ ai gwara datazo dan nasan yanzu Ameera tafi kowa jin dadi.”
Ummy tai murmushi.
Aunty Nana tace “ Ya jikin Hassan?”
Tace “dama saboda shi na kiraki”
Aunty Nana tai shiru tana sauraranta.
Ummy tace “ Me kike tunanin akan yi masa aure?”
Aunty Nana tace “Aure? Wace irin magana kike yi Hafsa? Wa kike tunanin zai aureshi? Karfa san kanku ya muku yawa.”
Ummy mamaki ya kamata tace “ban gane san kai ba? Sai kace wani mahaukaci ko mai lalura mara warkewa ko fa nakasar jiki?”
Aunty Nana tace “ Ni dai dan bakwasan gaskiya ne, amma na tabbatar Hassan nada matsalar kwakwalwa, kardai ku aura masa yarinya yazo yana neman kasheta.”
Mikewa Ummy tai idanunta suka canza tace “mene?”
Aunty Nana tace “ Hafsa......”
Kashe wayarta Ummy tai sannan tai shiru tana kara maimaita kalaman Aunty Nana a ranta.
Aunty Nana irin matan nan ne da duk abinda ya fito musu a baki fada suke ba tare da sunyi nazari. Da yaya zaka fuskanci kalamansu ba.
Ummy ta shiga d’aki jiki a sanyaye, Abba ya gama shiryawa yana fesa turare ta shigo, yanda yaga ta zauna akan gado yasa ya juyo yace “Lafiya?”
Kallansa tai tace “ Alhaji ya zamuyi da Hassan?”
Ajiye kwalbar turaren yai yace “keda Yaya Nana ce?”
Kallansa tai cikin mamaki tace “ya akai ka sani?”
Yace “ me yasa haryanzu bakisan kanki ba? In dai har naganki a wannan yanayi to nasan matsalar Hassan ne ke damunki, to in har naga yanayin ya hada da dan baccin rai to inba Aunty Nana ba waye? Ni dai nasan ba ni bane, sannan Sagir banaji ya taba bata miki ran da har zaki shiga cikin wani hali, ita kuwa Ameera yarinta ce a kanta.”
Ummy ta kalleshi tace “jiya naji yanda kukai da Dr Ahmad, shiyasa......”
Yace “kike tunanin hadashi da Aina’u?”
Tai shiru, kusa da ita ya zauna yace “Hafsa!”
Kallansa tai yace “ shi aure da kike gani nufine na Allah, sannan wani baya auran matar wani, Allah ne kadai yasan abinda ya shirya akan rayuwar yaran nan, mudai abinda zamumai kawai shine mu dinga mai addu’a kamar yanda muka saba.”
Kai ta jinjina alamar gamsuws sannan tace “yanzu zaka wuce ne? Naga bakai break ba.”
Yace “ In naje naci acan, dan nasan thnda dai gida ta gayyacen ta shiryamin abinci, sannan ba dadi taga naje banci ba, kuma kinsan halina inhar naci abinci yanzu 11 banaji akwai abinda zan iya ci nan da awa d’aya.”
Tace “Hakane, kai kadai zaka ne?”
Yace “a’a da ina tunanin tafiya da Sagir to kuma ina tunanin kar taji nauyin fadar bukatun ta a gabansa, shiyasa zan tafi daga ni sai Ibrahim.”
Tace “to sai kun dawo.”
Ya dau hularsa ya saka sannan suka fito tare.
Sagir na falo ana masu Ameera tsiya akan sun gaji da jiran abincin safe ya hangosu, mikewa yai yana dariya yace “Ummy zaku fita yawon shakatawa ne?”
Harararsa tai tace “a haka ake fita ba ko mayafi?”
Yace “ai ba komai tunda mota zaki shiga.”
Abba ya kalleshi yace “Wato Sagir in baka zolayi mahaifiyarka ba na kula sam bakajin dadi.”
Keyarsa ya sosa yana murmushi yace “Abba kasan nafisan kullum naga tana murmushi ne.”
Ummy ta kalleshi tace “ Muje muga masu abinci tunda Abbanka ya mana yajin aiki yau.”
A tare suka fara takawa suna hira, Abba ya bisu da kalli cikin jin dadi sannan ya juya ya fita.
************
Jalila anci uban aiki duk tai wujiga wujiga ga ko abinci ba wanda ya damu taci, sai data gama jera komai sannan ta fito, bangarensu ta nufa cikin tsantsar gajiya.
Goggo na zaune hankalinta duk yana kofa tana jiran yar tata ta shigo, ko abincin ma ta kasa ci, Jalila na shigo ta zube tare da kwanciya akan cinyarta.
Goggo tace “zauna ki danci abinci.”
Da kyar ta mike ta sha shayi da bread sannan ta fara kokarin kwanciya, Goggo tace “Jalila kidan jira ya tsirga miki.”
Tace “Goggo wlh nikadai nasan me nakeji.”
Tafada tare da kwantawa.
Abba ya iso batare da shan wahala ba, saboda kowa yasan Hajiya, Sun shiga babban falo inda ake sauke manyan baki.
Dady ne ya fara tarbarsu, ya zauna suka gaisa, sannan mumy ta shigo.
Bayan sun gaisa ne sai Hajiya ta shigo.
Taura yana ganinta ya mike, sai data zauna sannan ya gaidata.
Mumy ta mike ta fito, d’akin Safeena ta shiga taga bata nan, na ta fito ta bude dakin Sultan, yana zaune akan computer da alama game yakeyi. Tace “Safeena fa?”
Yace “Safeena? Ba jiya take cewa akwai inda zasuba yau da friends dinta? Inaji sun tafi ai.”
Mumy tace “dama yau ne? Ni na dauka sai gobe ai, to kai taso ku gaisa da bakon.”
Mikewa yai ya fito, yana gaishesu ya koma d’aki.
Mumy tace “Inna bata nan kinsan tace yau akwai inda zasuje.”
Inna ta kalli Taura tace” babbar yarinyar bata nan sun fita.”
Yace “bakomai Hajiya,ni ai ban masan kinada jika babba haka ba.” Yana nufin Sultan.
Tai murmushi tace “Sultan ai na biyu ne, babbar mace ce ajinta shida a secondary.”
Yace “Masha Allah, Allah ya raya.”
Tace “Ameen.
Sun d’an bar musu falon na sama da minti talatin saboda su ci abinci.
Sai da suka gama sannan Inna da Dady suka shiga.
Sun d’anyi shiru kafin Inna tace “Taura kayi hakuri rashin nemanka danai har sai damatsala ta tasomin.”
Yace” bakomai Hajiya.”
Tace “Taura muna cikin matsala wanda company dinku ke neman fuskantar durkushewa...........”
Nan ta zayyane masa duk yanda matsalolin ke faruwa,shima Dady na kara mai jawabi.
Sai da sukka gama, Ta daura da cewa “shine nake neman taimakon ka.”
Taura yai shiru kafin can yace “ba matsala indai, sai dai nima sai kun bani zuwa gobe na duba yanayin abin sannan sai musan yanda za’ai.
Taji dadi sosai, dady yace “mungode kwarai.”
Taura ya dau takardar ya shiga kara dubawa, yana nazari, kudi sukeso sosai dole dai ya nutsu kafin yasan abinyi, dan business ne.”
Inna ta kara godiya, Dady ma haka.
Bayan sun gama ne suka mike dan tafiya.
Jalila bayan tayi wanka Goggo ta bata mafici dan takai makotansu akwai wata tsohuwa agidan da ta sa a mata.
A gun ajiye motoci ta hango su a tsaye, da alama bakon ne, ta gabansu dole zata wuce shiyasa tana zuwa inda suke ta tsugunna har kasa ta gaishesu.
Kallanta Taura yai ya kura mata ido, har ibrahim ya amsa gaisuwar shi bai ce komai ba.
Ta kara kallan Taura wanda kallan da yake mata yasata yin kasa dakai tace “Ina wuni?”
Taura yace”lafiya kalau, kece babbar yarinyar gidan?”
Cikin halin ko in kula tace “Eh!”
Yace “Masha Allah, aji shida akace kike ko?”
Takara cewa eh.
Yace “Alhamdulila.”
Mikewa tai tace “Sai anjima.”
Taura yasa hannu a aljihu ya zaro dubu biyar, yace “gashi!”
Idanu ta zaro tai saurin cewa “A’a kabarshi nagode.”
Kallanta yai sannan yai murmushi yace “kyauta na miki fa?”
Tace “wlh ka barshi, na gode.”
Kai ya daga sannan ya bita da kallo, Ibrahim ya kalla bayan sun shiga mota, yace “me zakace game da yarinyar nan?”
Ibrahim yace “ban fahimceka ba.”
Taura yai murmushi sannan yace a ransa Alhamdulila ala kuli hal......
#Oneluv💕
: 🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *AyusherMohd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
*NO 9*
Taura yayi shiru a d’aki yana nazari, Ummy ce ta turo kofar tare da sallama.
Bai jita ba dan ya nustu sosai, kusa dashi ta tsaya tace “Lafiya?”
Kallanta yai sannan yadan murmusa yace “ tsi wlh hankalina ya tafi tunani ne.”
Tace “abinda kajeyi bai yiwu bane?”
Yace “Hafsa dan zauna.”
Zama tai kusa dashi tana kallansa, yace “ yau naga wata yarinya a gidan danaje, ban san meyasa ba naji yarinyar ta kwantamin sosai wanda nakema Hassan sha’awarta, tarbiyarta yasa nake tunanin zata kula da shi fiye da tunanin mu.”
Ummy tace “ yarinyar gidan dakaje ne?”
Yace “eh.”
Zata sake magana Ameera ta bude kofar da gudu tace “Ummy yaya ne.......”
Da gudu suka mike suka hau sama, yana kwance a kasa da alama fadowa ma yai ya kankame jikinsa yasa hannunsa a yuwansa wanda ya kasa jan numfashi.
Sagir sai kokari yake gun taimaka mai, Ummy kasa karasawa tai sai kuka da take yi, Abba ya karasa da sauki yana danna mai kirjinsa, Aina’u da Ameera sai kuka sukeyi.
Kusa dashi ta karasa ta dauko karamin bedsheets a gefen gadonsa sannan ta lulubamai, jiki a sanyaye ta juya ta fita.
Tana rufe kofar yana bude idanunsa, kofar ya kalla dan tun da ta shigo ya farka, idanunsa ne suka canza launi a hankali ya maidasu ya rufe saboda tsananin tausayin da yakeji na mahaifiyarsa.
Mikewa yai ya hau kan gado yai wata kwanciya a dukunkune, a hankali idanunsa suka zubo da wasu zafaffan hawaye.
Ummy tana fita ta sauka kasa, kitchen ta shiga inda Ameera da Aina’u suke girkin abincin safe.
Tace “wannan jagwalgwalo har mun gaji da jiransa, sai kace wanda ake mana abincin arziki.”
Ameera tace “Ummy kin dage sai munyi girki da weekend kinga kuwa kome muka dafa sai kuyi hakuri kuci.”
Ummy tace “ai na gama kula dake sam bakyasan yin girki, yanzu kuwa kinjama kanki duk asabar da lahadi ke zaki dinga yin girkin safe.”
Ameera tace “Shikenan Ummy sai mudingacin Indomie.”
Aina tai dariya tace “Lalai Ameera, Abban zaki ba indomie?”
Ummy ta juya tana murmushi, falo ta zauna sannan ta d’au waya ta kira Aunty Nana.
Bayan sun gama gaisawa tace “muna nan da Aina’u munatashan hutu.”
Aunty Nana tace “ ai gwara datazo dan nasan yanzu Ameera tafi kowa jin dadi.”
Ummy tai murmushi.
Aunty Nana tace “ Ya jikin Hassan?”
Tace “dama saboda shi na kiraki”
Aunty Nana tai shiru tana sauraranta.
Ummy tace “ Me kike tunanin akan yi masa aure?”
Aunty Nana tace “Aure? Wace irin magana kike yi Hafsa? Wa kike tunanin zai aureshi? Karfa san kanku ya muku yawa.”
Ummy mamaki ya kamata tace “ban gane san kai ba? Sai kace wani mahaukaci ko mai lalura mara warkewa ko fa nakasar jiki?”
Aunty Nana tace “ Ni dai dan bakwasan gaskiya ne, amma na tabbatar Hassan nada matsalar kwakwalwa, kardai ku aura masa yarinya yazo yana neman kasheta.”
Mikewa Ummy tai idanunta suka canza tace “mene?”
Aunty Nana tace “ Hafsa......”
Kashe wayarta Ummy tai sannan tai shiru tana kara maimaita kalaman Aunty Nana a ranta.
Aunty Nana irin matan nan ne da duk abinda ya fito musu a baki fada suke ba tare da sunyi nazari. Da yaya zaka fuskanci kalamansu ba.
Ummy ta shiga d’aki jiki a sanyaye, Abba ya gama shiryawa yana fesa turare ta shigo, yanda yaga ta zauna akan gado yasa ya juyo yace “Lafiya?”
Kallansa tai tace “ Alhaji ya zamuyi da Hassan?”
Ajiye kwalbar turaren yai yace “keda Yaya Nana ce?”
Kallansa tai cikin mamaki tace “ya akai ka sani?”
Yace “ me yasa haryanzu bakisan kanki ba? In dai har naganki a wannan yanayi to nasan matsalar Hassan ne ke damunki, to in har naga yanayin ya hada da dan baccin rai to inba Aunty Nana ba waye? Ni dai nasan ba ni bane, sannan Sagir banaji ya taba bata miki ran da har zaki shiga cikin wani hali, ita kuwa Ameera yarinta ce a kanta.”
Ummy ta kalleshi tace “jiya naji yanda kukai da Dr Ahmad, shiyasa......”
Yace “kike tunanin hadashi da Aina’u?”
Tai shiru, kusa da ita ya zauna yace “Hafsa!”
Kallansa tai yace “ shi aure da kike gani nufine na Allah, sannan wani baya auran matar wani, Allah ne kadai yasan abinda ya shirya akan rayuwar yaran nan, mudai abinda zamumai kawai shine mu dinga mai addu’a kamar yanda muka saba.”
Kai ta jinjina alamar gamsuws sannan tace “yanzu zaka wuce ne? Naga bakai break ba.”
Yace “ In naje naci acan, dan nasan thnda dai gida ta gayyacen ta shiryamin abinci, sannan ba dadi taga naje banci ba, kuma kinsan halina inhar naci abinci yanzu 11 banaji akwai abinda zan iya ci nan da awa d’aya.”
Tace “Hakane, kai kadai zaka ne?”
Yace “a’a da ina tunanin tafiya da Sagir to kuma ina tunanin kar taji nauyin fadar bukatun ta a gabansa, shiyasa zan tafi daga ni sai Ibrahim.”
Tace “to sai kun dawo.”
Ya dau hularsa ya saka sannan suka fito tare.
Sagir na falo ana masu Ameera tsiya akan sun gaji da jiran abincin safe ya hangosu, mikewa yai yana dariya yace “Ummy zaku fita yawon shakatawa ne?”
Harararsa tai tace “a haka ake fita ba ko mayafi?”
Yace “ai ba komai tunda mota zaki shiga.”
Abba ya kalleshi yace “Wato Sagir in baka zolayi mahaifiyarka ba na kula sam bakajin dadi.”
Keyarsa ya sosa yana murmushi yace “Abba kasan nafisan kullum naga tana murmushi ne.”
Ummy ta kalleshi tace “ Muje muga masu abinci tunda Abbanka ya mana yajin aiki yau.”
A tare suka fara takawa suna hira, Abba ya bisu da kalli cikin jin dadi sannan ya juya ya fita.
************
Jalila anci uban aiki duk tai wujiga wujiga ga ko abinci ba wanda ya damu taci, sai data gama jera komai sannan ta fito, bangarensu ta nufa cikin tsantsar gajiya.
Goggo na zaune hankalinta duk yana kofa tana jiran yar tata ta shigo, ko abincin ma ta kasa ci, Jalila na shigo ta zube tare da kwanciya akan cinyarta.
Goggo tace “zauna ki danci abinci.”
Da kyar ta mike ta sha shayi da bread sannan ta fara kokarin kwanciya, Goggo tace “Jalila kidan jira ya tsirga miki.”
Tace “Goggo wlh nikadai nasan me nakeji.”
Tafada tare da kwantawa.
Abba ya iso batare da shan wahala ba, saboda kowa yasan Hajiya, Sun shiga babban falo inda ake sauke manyan baki.
Dady ne ya fara tarbarsu, ya zauna suka gaisa, sannan mumy ta shigo.
Bayan sun gaisa ne sai Hajiya ta shigo.
Taura yana ganinta ya mike, sai data zauna sannan ya gaidata.
Mumy ta mike ta fito, d’akin Safeena ta shiga taga bata nan, na ta fito ta bude dakin Sultan, yana zaune akan computer da alama game yakeyi. Tace “Safeena fa?”
Yace “Safeena? Ba jiya take cewa akwai inda zasuba yau da friends dinta? Inaji sun tafi ai.”
Mumy tace “dama yau ne? Ni na dauka sai gobe ai, to kai taso ku gaisa da bakon.”
Mikewa yai ya fito, yana gaishesu ya koma d’aki.
Mumy tace “Inna bata nan kinsan tace yau akwai inda zasuje.”
Inna ta kalli Taura tace” babbar yarinyar bata nan sun fita.”
Yace “bakomai Hajiya,ni ai ban masan kinada jika babba haka ba.” Yana nufin Sultan.
Tai murmushi tace “Sultan ai na biyu ne, babbar mace ce ajinta shida a secondary.”
Yace “Masha Allah, Allah ya raya.”
Tace “Ameen.
Sun d’an bar musu falon na sama da minti talatin saboda su ci abinci.
Sai da suka gama sannan Inna da Dady suka shiga.
Sun d’anyi shiru kafin Inna tace “Taura kayi hakuri rashin nemanka danai har sai damatsala ta tasomin.”
Yace” bakomai Hajiya.”
Tace “Taura muna cikin matsala wanda company dinku ke neman fuskantar durkushewa...........”
Nan ta zayyane masa duk yanda matsalolin ke faruwa,shima Dady na kara mai jawabi.
Sai da sukka gama, Ta daura da cewa “shine nake neman taimakon ka.”
Taura yai shiru kafin can yace “ba matsala indai, sai dai nima sai kun bani zuwa gobe na duba yanayin abin sannan sai musan yanda za’ai.
Taji dadi sosai, dady yace “mungode kwarai.”
Taura ya dau takardar ya shiga kara dubawa, yana nazari, kudi sukeso sosai dole dai ya nutsu kafin yasan abinyi, dan business ne.”
Inna ta kara godiya, Dady ma haka.
Bayan sun gama ne suka mike dan tafiya.
Jalila bayan tayi wanka Goggo ta bata mafici dan takai makotansu akwai wata tsohuwa agidan da ta sa a mata.
A gun ajiye motoci ta hango su a tsaye, da alama bakon ne, ta gabansu dole zata wuce shiyasa tana zuwa inda suke ta tsugunna har kasa ta gaishesu.
Kallanta Taura yai ya kura mata ido, har ibrahim ya amsa gaisuwar shi bai ce komai ba.
Ta kara kallan Taura wanda kallan da yake mata yasata yin kasa dakai tace “Ina wuni?”
Taura yace”lafiya kalau, kece babbar yarinyar gidan?”
Cikin halin ko in kula tace “Eh!”
Yace “Masha Allah, aji shida akace kike ko?”
Takara cewa eh.
Yace “Alhamdulila.”
Mikewa tai tace “Sai anjima.”
Taura yasa hannu a aljihu ya zaro dubu biyar, yace “gashi!”
Idanu ta zaro tai saurin cewa “A’a kabarshi nagode.”
Kallanta yai sannan yai murmushi yace “kyauta na miki fa?”
Tace “wlh ka barshi, na gode.”
Kai ya daga sannan ya bita da kallo, Ibrahim ya kalla bayan sun shiga mota, yace “me zakace game da yarinyar nan?”
Ibrahim yace “ban fahimceka ba.”
Taura yai murmushi sannan yace a ransa Alhamdulila ala kuli hal......
#Oneluv💕
: 🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *AyusherMohd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
*NO 9*
Taura yayi shiru a d’aki yana nazari, Ummy ce ta turo kofar tare da sallama.
Bai jita ba dan ya nustu sosai, kusa dashi ta tsaya tace “Lafiya?”
Kallanta yai sannan yadan murmusa yace “ tsi wlh hankalina ya tafi tunani ne.”
Tace “abinda kajeyi bai yiwu bane?”
Yace “Hafsa dan zauna.”
Zama tai kusa dashi tana kallansa, yace “ yau naga wata yarinya a gidan danaje, ban san meyasa ba naji yarinyar ta kwantamin sosai wanda nakema Hassan sha’awarta, tarbiyarta yasa nake tunanin zata kula da shi fiye da tunanin mu.”
Ummy tace “ yarinyar gidan dakaje ne?”
Yace “eh.”
Zata sake magana Ameera ta bude kofar da gudu tace “Ummy yaya ne.......”
Da gudu suka mike suka hau sama, yana kwance a kasa da alama fadowa ma yai ya kankame jikinsa yasa hannunsa a yuwansa wanda ya kasa jan numfashi.
Sagir sai kokari yake gun taimaka mai, Ummy kasa karasawa tai sai kuka da take yi, Abba ya karasa da sauki yana danna mai kirjinsa, Aina’u da Ameera sai kuka sukeyi.