← Book details Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 28 OF 53

Sashe 28

Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Mumy ta mike ta fita tana tunanin kalaman Inna, batagane wacece babbar ‘yarta ba, yo ai kowa yasan Safeena Qta fara haifa.
Hart takai matattakala uku sai ta tsaya cak tace “ba dai......?
Komawa tai da gudu saman ta bude dakin Inna, tace “Inna badai so kike ki cema mutane nice mahaifiyar Jalila ba?”
Inna bata kalleta ba sai shafa man zafin da takeyi a kafarta da takeyi, Mumy cikin mamaki ta karaso kusa da ita tace “Inna?”
Inna ta kalleta tace “ me? Kina tunanin is in possible?”
Mumy cikin tsoro tace “Inna me kike tunani? Taya zaki canzama yarinya mahaifiyarta? Bayan mahaifiyarta nanan da rai?”

Inna ta kalleta tace “ kina tunanin in Taura yasan gaskiyar al’amari akan ba yarinyarki bace zai yarda? Bakya tunanin zai ga yaudararsa mukai? In ya kwace kudin dayai investing a company dinmu fa saboda munyi betraying dinsa?”

Mumy tace “to ai bai fito filli yace ‘yata yakeso ba, shidai babbar yarinyar gidan nan yace, sannan in ta sanar dasu fa kafin kije? Ni Inna wannan karan ban amince da abinda kika tsara ba.”

Inna ta kalleta tace “shiyasa akoda yaushe nake ganin hankalinki da wayan ki na banza ne, ke wai haryanzu kina tunanin Abakar sanki yake?”
Tace “Inna zaki fara ko?”

Tufe maganin zafin tai tace “ kiyi gaggawar tashi daga baccin da kikeyi, kada ki kuskura kiyi relying akan kowa inba ni ba, sannan kada kiyi trusting din kowa inba ni ba.”

Mumy ta kalleta sannan ta mike kawai batace komai ba ta mike ta fito, itakam duk abinda Inna tace mata tana bi sai dai wannan karan hankalinta bai kwanta da hakan ba.

**********

Jalila kam da sutai sallar asuba falonsu na sama ta fito ta kwanta dan taga alamar baida niyyar mikewa daga gun.

Wajen karfe tara ta farka, jitai jikinta ya ware, saukowa tai daga kan kujerar data ke kwance sannan ta karaso jikin kofar, hannu tasa a hankali ta murda kofar, kanta ta zuro a hankali tana lekawa, bata ganshi akan gadon ba hakan yasa tai tunanin baya dakin, tura kofar tai shiga, tana shiga ta hangoshi a kwance akan sallaya inda yai sallah, baki tadan tabe tace “kamar gaske.”

Wucewa tai zata shiga toilet, gani tai ya fara wani abu harta je bakin toilet din, juyowa tai da sauri ta kalleshi, gani tai yana zufa sannan sai wani murkusus yake, idanunsa a rufe gam.

Kallansa ta sakeyi tace “mafarki yake?”
Kusa dashi taje tadan sa hannu tadan tabashi, hannunta ya rike da karfe yana wani irin numfashi, sankamewa taga yanayi, tsoro ne ya fara kamata, ga hannunta ya kankame da karfi wanda zafinshi ya isheta.

Cikin tsananin tsoro ta fara cewa “Yaya!” Dan abinda taji suna cemai kenan, Yaya! Yaya! A tsorace take kiran sunan nasa.

Ganin zufa tana keto mai ta ko ina ga sai kara kamewa yakeyi, yanzu kam hannunta ya saki yasa hannunsa a wuyansa yana kokarin jawo numfashinsa da yake mai wahalar shaka.

Jikinta ne ya fara rawa, ganin yanda yake sa hannu a wuyansa yasa tai saurin sa hannu ta rike nasa da karfi, a tsorace take cewa “Yaya! Yaya! Menene?”

Ganin abin karuwa yake yasa ta fara tofamai kulhuwallahu, falaqi da nasi, dan bata iya addo’oi ba.

Hannunta data rike nashi ya jawo hakan yasa ta fada jikinsa, da sauri ta mike, sannan ta shiga kiransa tana tabashi.

Ahankali yai wani dogon numfashi, sannan ya bude idanunsa wanda sukai jaa.
Idanunsa ne suka sauka a kanta tayi tsuru tsuru kamar kace mata kyaa ta ruga a guje....

Kallanta yai cikin rashin jin dadi, dan shikam yasan abinda yake tsoro kenan, bayasan wani ya ganshi cikin wannan halin.
Jalila kam tana nan a zaune kamar abu mara motsi har ya mike zaune, ganin yanda ta kame yasa ya mike tsaye ya zaune a bakin gado sannan yasa hannu ya shafi fuskarsa cikin takaici.
Jalila a hankali ta juyo ta kalleshi bakinta na rawa tace “ hmm ka ka......”
Kallanta yai fuskarsa a hade ga idanunsa sunyi jaa, wani irin tsoronsa ne ya kamata, gabanta ya shiga faduwa.
Idanunsa na kanta yace “ ka me?”
Kai ta girgiza da sauri tace “hm ba komai.”
Ta juya da sauri gaban wardrobe taje ta bude ta rasama me zatayi a kai sannan ta matso gaban madubi shima ta tsaya, sannan ta bude bandaki da sauri ta shiga ciki.

Duk abinda takeyi idanunsa na kanta, idanunsa ya sake runstewa cikin takaici, gani nai ya bude idanunsa ya mike da sauri ya dau waya da key din motarsa.

Yana kokarin fita itakuma tana fitowa, kallan juna sukai da sauri ya dauke kansa sannan yai waje.

Kallan kofar daya rufo tai sannan ta zauna a bakin gado tana maida numfashi kai kace gudu tai, me ke nan? Me ya faru dazu? Aljanu ne dashi? Kansa kalau kuwa? Badai wannan bace matsalar da Ummy tai magana?

Ta dade a zaune sannan ta mike tai wanka, haka ta sa kaya jiki a sanyeye sam hankalinta ya kasa kwanciya.

Ameera ce ta kwankwasa kofa, Jalila ta bude mata.
Tiren abinci ta miko mata tace “ga abincin yaya, ke kuma ki sako muje kasa.”

Jalila ta kalleta cikin sanyin jiki tace “Bayanan, sannan ni banajin yunwa.”
Ameera ta kalleta tace “yaza’ai kice bakyajin yunwa?”

Jalila ta kalleta sannan ta koma ciki, gaba daya itakam abin duniya ya dameta, Ameera ta ajiye tiren sannan ta kalleta tace “ga na yaya nan sai kici anan, shi nasan ba yanzu zai dawo ba.”
Ajiye abincin tai ta fita.

Jalila kam a zaune kawai take akan gado tama rasa ta ina zata fara tunanin abinda ke faruwa.

Ganin ta rasa amsa kawai ta dauko hijab dinta ta sauko, su Ummy na cin abinci ta sauko kasa, kusa da Ummy taje ta gaisheta sannan ta gaida Sagir, Ummy tace “zauna muci abinci.”

Jalila wacce ta fito dan sanar da ita tana san zuwa gun Goggo tai shiru tana wasa a hannunta.
Ummy ta kalleta tace “Ya akai Jalila? Wani abin kikesan fadamin?”
Dagowa tai ta kalli Uncle sannan ta kalli Ummy.

Sagir ya kalli Ummy yace “ko jikin ne?
Ummy ta kalleta tace “Jikin ne?”

Jalila da sauri tace “bashi bane.”
Ummy tace “to menene?”

Jalila ta kalleta sannan ta sake yin shiru, Sagir ya yace “ asibitin zaki koma?”

Kallansa tai sannan ta kalli Ummy, Ummy tace “wai haka?”

Jalila ta daga kai, Ummy tai murmushi tace “menene to da kika kasa fada? Ki zauna kici abinci sai kuje da Sagir.”

Kallan Sagir tai da sauri, sai dai batace komai ba.
Ummy tace “in bakya san ci anan ki hau sama kici kafin ya gama.”
Jalila tace “nagode Ummy.” Sannan tajuya tai ta hau sama.

Zama tai a falon tai shiru Hassan take hangowa abinda yai dazu.

Kanta ta kwantar akan kujera, Muryar Ameera taji tana kiranta, nan ta mike ta sauko ko dakin bata koma ba.

Da zata fita Ummy ta kirata, Jalila ta juya taje gunta, Ummy ta miko mata leda sannan tace ki gaisheta, dan gwarama da kika tuna min yau kije, dan Abban Ameera inya dawo ba lalai ya barki ki fita ba, bayasan fita.”
Jalila ta amshi ledar tana godiya.

A bakin mota ta hangoshi a tsaye, nan ta karasa kusa dashi, gani tai ya bude mata bayan motar sannan ya juya ya shiga gun zaman driver tare da kunna motar.

Rufe kofar motar tai yaja suka fara tafiya, Motar tayi shiru sai karar redio dake tashi a cikin motar.

Sunyi tafiya mai dan tsayi kafin can yace “Jalila.”
Idanunta na jikin window tace “naam.”
Yace “Jalila nasan na miki laifi sai dai nan gaba zaki fahimci dalili na nayin hakka sannan na tabbatar a lokacin zaki san abinda nake nufi da kalamai na.”

Kallansa tai sannan ta daure tace “ magana ta wuce, sai dai meke damun Yayan naka?”
Shiru yai kafin yace “Ni kaina ban sani ba, dukanmu yan gidan ba wanda yasan meke damunshi, shikadai yasan abinda ya faru a lokacin.”
Lokacin?
Yace “ eh lokacin da su Husain da Nazir dan kanin Abba.”

Jalila tai shiru batace komai ba, Sagir ya kalleta ta madubin gaban motar, yana tsananin san yarinyar nan haka kuma yana tsananin tausayinta sai dai duk yanda yaso da so da kaunar ta bai isa ba.....bai isa ba.”

Dagowa tai ta kalli madubin suka hada ido, kanta ta kawar sannan a hankali tace “Uncle!”
Yace “naam.”
Har zata cemai Goggo mahaifiyarta ce sai ta fasa, tace “shikenan ma.”
Yace “menene? Dan Allah ki fadamin.”

Shiru tai kafin can tace “Goggo nace a asibitin.”

Yace “nayi tunanin Goggon da kike maganar ta ne amma ya kuke?ni da nadauka ai Goggon mahaifiyarki ce.”

Zatai magana ya taka burki da karfi, juyowa yai ya kalleta yace “Jalila are u okay?”
Tace “eh menene?”
Yaran da suka tsallaka titin ya kalla yace “ yara ne wlh saura kiris su ja mana.”

Shiru tai batace komai ba, gangarawa asibitin yai, parking yai sannan yace “Jalila ki yi hakuri dan Allah.”

Kallansa tai tace “zancen hakuri da rashinsa ai ya kare, kafin ai abu ne ake neman canzashi ba bayan anyi ba.”
Ta bude motar sannan tace “nagode.”

So yake ya shiga amma bayasan ya kara bata mata rai.

Bata dade da shiga ba sai gatanan hankali a tashe tace “Uncle na rasa Goggo na.”
Sagir yace “ban gane ba?”

Kuka ta saka hankalinta a tashe take cewa sunce an mata transfer zuwa wani asibitin kuma basusan sunan asibitin.”
Yace “ban gane ba?”

Tana kuka tace “wai basu sani ba......”

********

Abba kam dakyar ya samu bacci jiya, ya rasa meyasa gaba daya tunanin yarinyar da bata fi sa’an dansa ba ya dameshi.
Ai kuwa da sassafe ya fada mota da driver dinsa suka nufo kano, ko kara bi ta contracts din baiyi ba.

Me ya sameshi? Me ke faruwa dashi?

*£**********

Mumy ce ta kalli Sultan tace “Sultan bari muje gidan Jalila, ko zakaje?”
Inna ce tai kakari wanda yake nuna mata ta daina, Mumy ta kalleshi tace “bari muje.”

Nan suka fito daga gidan suka shiga mota.

#OneLuv💕

🗯 *JALILAH* 🗯

Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*

(_D home of expert and perfect writer's_💡)

*28*
Chapter 28 · 0% Book details