Sashe 7
Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Har ya gama sannan ta fita, yana fita Zarah fa miko mata sosan powder da madubi.
Jalila ta ture hannunta tace "banaso."
Sannan ta maida kanta kan desk ta kwanta, Zarah tace "tashi mu tafi."
Jalila tace " jeki ni sai anjima zan fita."
Zarah ta fita tai gaba, tana kwance har aka wa watse, idanu ma ta rufe kamar mai yin bacci, batasan sanda ya shigo class din ba.
Ya nemeta a waje bai ganta ba shiyasa yai tunanin ajin, kallanta ya tsaya yi yana murmushi, a hankali ta bude idanunta dan jin kamar ana kallanta.
Idanunta ne suka sauka akan fuskarsa shagwabe fuska tai dan ta tabbatar kila tunaninsa da takeyi ne yasa take ganin kamar shine.
Maida idanun tai zata rufe yace " fushi ake da ni ne?"
Da sauri ta bude idanunta tana kiftasu, sannan tai saurin komawa ta zauna, Sagir yace " me kike a class ke kadai?"
Batasan me ya sameta ba kawai ganintai ta wani hade rai wai ita a dole an mata laifi.
Sagir yace "Da alama wannan Malamin yayi laifi kenan?"
Kallansa tai fuska a hade tace " ba kai bane dazu ko kallan inda nake bakai ba?"
Tayi mamakin canzawar ta da kuma yanda take magana, a ranta tace "Lalai Jalila wato kin zama kwarariya."
FSagir samun kansa yai da darawa sannan yace " Nayi laifi, sai dai kin manta dazu Uncle Sagir ne malamin student a ajin?"
Tace "Yanzu fa?"
Yace "Yanzu kuwa Urs Sagir ne."
Da sauri ta sa hannu ta rufe fuskarta.
Kallanta ya sakeyi yace " ba haka bane?"
A hankali tace "Hakane."
Murmushin jin dadi yai sannan yace " tunda na ganki hankalina ya kwanta dan dama Abbana zan raka wani guri, nace bari nazo na ganki."
Kallansa tai tace "Okay, sai Monday kenan."
Yace "Kai! Har sai monday fa ko?"
Tace "ka manta yau friday?"
Fuska taga ya canza yace "gashi naga alama ke ko yar wayarnan baki dashi, anya zan iya jure missing dinki har sai monday?"
Kanta ta sunkuyar kasa tana murmushi, ajiyar zuciya yai sannan ya matso daf da ita yace "bari nai full charge yanda zan cancana battery dinA."
Kallansa tai sannan ta maida idanunta kasa tana murmushi.
Ido ya kura mata sosai sannan ya ce "Na tafi."
Sai dayaje kusa da kofa sannan tace "sai anjima."
Juyowa yai sannan ya juya ya tafi.
Ta window ta bishi da kallo, wani zazzafan so na ratsata.
Sam ta shagala da tunani kafin ta farga ta fito da sauri,
Tafi minti goma a tsaye taga dai ba alamar su Safeena, sannan ba alamar ma d'alibai suna wucewa, lalai ta tsaya soyayya antafi an barta, yau tana cikin wani hali dan tasan masifa kam ba'a magana.
Tana tafe tana dan mitocinta ita kadai..........
************
Inna ce ta kalli Sani sannan ta kalli takardar daya kawo mata dauke da sunan Taura da number sa.
Tace " da ka sake bincike ba wani abu game da rayuwarsa da ta kyalansa bayan matsalar yaran?"
Sani yace "eh gaskiya ba wani abu special, sai...."
sai kuma ye " ba ma dai komai."
Tace "da ke zaka fada?"
Yace dama kamar yaransa maza biyu ne, 'yan biyu babban Hassan sai kaninsa Husaini, sai dai jiya sai aka cemin wai Hassan ne da Sagir sai macen.
Inna tace " ko dai kaine ka manta ba?"
Yace "zai ita yiwuwa inaji Husainin tun yana karami ya rasu."
Tace " Dama ai maza biyu mace d'aya kacemin."
Yace "hakan na sani amma nadauka 'yan biyun ne ashe wa da kani ne."
Inna ta jinjina kai cikin rashin damuwa tace " ba wani abu bayan nan?"
Yace "babu."
Nan ta saka number a wayarta sannan ta anna dialing.
Sai atai ringing hudu sannan ya d'aga.
A banngarensa yana zaune a bayan mota shi da Ummy, sai Sagir dake zaune a mazaunin driver shi kuma hassan na gefe, suna hanyar zuwa asibiti.
Yana daga wa Inna tai sallama,Abba ya amsa sannan yace "ban gane ba."
Inna tace " Taura nice Hajiyar grain."
Sai daya danyi nazari na wasu dakiku kadan sannan yace "Hajiya ina wuni?" Yai magana tare da canza yanayin maganarsa zuwa girmamawa."
Inna ta amsa sannan tace " Taura ganinka nake san yi ina fatan zaka bani lokaci."
Yace " Haba Hajiya, kina wani gari ne?"
Tace ina kano, ina neman alfarma ganinka sanda kake da lokaci.
Yace " yau dai inada abinyi, sai dai banaji gobe akwai abinda zanyi, a ina zamu hadu?"
Ya fada yana kallan Ummy, tace " gida na zakazo ko nice zanzo ko kuwa a wani gurin zamu hadu?"
Yace " a'a ba matsala ni zan zo."
Tace "Nagode Taura zan turoma da address din gidan."
Ya amsa da to sannan ya kashe wayar, Hassan ya kalla wanda idanunsa ke rufe kamar me bacci sai dai kowa na cikin motar yasan ba bacci yake ba, Ummy ya kalla ya shiga fada mata wacce ta kira.
Gate din wani katon asibiti naga an bude musu, Sagir ya shiga da motar.
*************
Jalila kam taci uwar tafiya kafin ta isa gida, duk ta gaji tayi ligib.
Tana shiga ta tadda Mumy a bangarensu, gabanta ne ya fadi sannan ta kalli Goggo wanda kuka ne kawai batai ba amma da alama daurewa kawai takeyi.
Mumy na ganinta tace "kin dawo daga yawon iskancin?"
Jalila fuska ta canza sannan ta kalli Goggo wacce ta tabbatar an kare mata cin mutunci ne, tace " Mumy ban gane b....."
Marin data kifa mata ne yasa ta kasa karasawa sannan ta rike kuncinta, Mumy tace " ce miki akai nan gidan karuwai ne? Ko me?"
Mamaki ya kama Jalila tace " Mumy ban ga........."
Wani marin ta kara kifa mata tace "a gidan ubanwa kika tsaya? Kungurmar munafuka? Dama kwanakin nan na kula bakyasan dawowa tare dasu Safeena saboda kina yawon bin maza."
Cikin wata irin kakkausar murya Goggo tace " RAMLATU!"
Kallan Goggo sukai a tare, dan Jalila bata taba ganin ran Mumy ya baci ba haka.
#ONELUV💕
[08/10, 19:18] +234 816 365 0557: 🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *AyusherMohd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
*NO 7*
Goggo cikin jin zafin kalaman Mumy tace "Ta ya zaki kira yarinya ta da haka? Kina tunanin 'ya'yanki sunfi na wa ne? A koda yaushe ina jure komai ne badan banajin zafin abinda akema Jalila ba sai dan ina tunanin kila hakan shine zai kawo salama a zuciyarta, komai da kika gani inayi inayinsa ne domin ta, taya ma zaki kalli 'ya a gaban uwarta ki kirata da wadan nan munanan kalaman?"
Mumy ba shakka ta dan tsorata, ta daure tace " ni kike yima fada? Kijira ni."
Tafada tare dayin waje da sauri, tana fita Goggo ta rike kirjinta wanda ya mata wani irin nauyi, ga wani irin dum na tsananin ciwon kai daya fara sara mata, Jalila ta karasa kusa da ita tare da rungumeta tace "Goggo na."
Cikin shagwaba tai maganar, Goggo ta daure dan batasan Jalila ta gane batada lafiya tace " Karki damu, ko me za'amin indai har akanki ne zan ita jure komai."
Jalila ta kwantar da kanta akan kafad'ar Goggo cikin tausayama kansu.
Banko kofar da akai ne yasa ta d'ago da sauri cikin tsoro, Dady ta gani bayansa Mumy ce.
Jalila da sauri ta mike ta tsaya a gaban mahaifiyarta alamar kareta tace "Dady kome ya faru laifi......."
Wani wawan mari daya kifa mata sai data fadi kasa, Goggo ta d'agota da sauri tana tambayarta.
Dady cikin tsananin bacin rai ya kalli Goggo yace "uban wa ya baki dama ki cima matata mutumci?"
Goggo ta kalleshi tace " ni duk mutuncin data cimin bai zama laifi ba kenan?"
Yace " Me yasa bakya abu da tunani? Ko kuwa kwakwalwarki ce bata aiki? Gidan da kike zaune,abincin da kike ci, kayan da kike sakawa, karatun 'yarki duk a cikin arzikin wa kike ci?"
Goggo tai shiru tare da maida kanta kasa, sannan tace " duk da haka banaji tanada damar cima 'yata mutunci...."
"Yanzu yarinya tayi laifi kina nufin tafi karfin a hukuntata ne ko me?"
Jalila ta mike da sauri ta rike kafafun Dady tace "Dady na tuba, dan Allah kayi hakuri laifinane."
Kafa yasa ya hankadata yace " gayyar tsiya."
Sannan ya juya ya kalli Mumy ya dafa kafadarta yace "muje ciki ko?"
Yi tai kamar me share kuka tace "Ba sai danace kayi hakuri ba?"
Juyowa yai ya bugama Jalila wani kallo na takaici daga ita har Goggon sannan ya juya shida Mumy, har sun kai kofa Jalila tace " Dady me kake nufi da gayyar tsiya?"
Wani banzan kallo ya buga mata sannan yace " idan kika sake min magana da wannan vibe din wlh sai jikinki ya gaya miki, sannan kiyi gagawar tasowa kiyi aikin daya kamata kiyi."
Ya juya shida Mumy sukai gaba, Jalila da kallo kawai ta bisu idanunta na zubar da hawaye, kallan Goggo tai kamar zatai magana sai ta fasa, hawayenta ta share sannan ta mike ta daukoma Goggo maganinta ta mika mata tace "Goggo share kinsan halin Dady akwai saurin hawa kamar farashi, amma na tabbatar ba duk abinda ya fada yake nufi na, ai uba ubane ko?"
Goggo ta tabbatar tannayi dan hankalinta ya kwanta ne shiyasa itama ta daure ta daga kai tace "haka ne."
Jalila ta cire kayan makarantarta sannan ta fita.
Yau kam tana aiki tana zubar da kwalla, itakam dole me gaskiya tana gama makaranta tace Sagir ya fito suyi aure ta d'auke Goggonfa subar wannan dan iskan gidan.
************
A asibiti kuwa bayan sun shiga cikin office din wanda a saman kofar naga an rubuta Neurologist, suna shiga ya mike daga zaman da yake sannan ya saki fuskarsa yana cewa Welcome Taura.
Abba ya karasa kusa dashi ya mika mai hannu suka gaisa, sannan suka gaisa da Sagir, Ummy tace "Dr Ahmad mun sameka lafiya."
Yace "Lafiya kalau Hajiya ya mai jikin?"
Kallan Hassan tai sannan tai murmushi kawai.
Guri suka samu suka zauna ita da Sagir, shi kuma ya shiga wani dan d'aki shida Hassan da Abba.
Jalila ta ture hannunta tace "banaso."
Sannan ta maida kanta kan desk ta kwanta, Zarah tace "tashi mu tafi."
Jalila tace " jeki ni sai anjima zan fita."
Zarah ta fita tai gaba, tana kwance har aka wa watse, idanu ma ta rufe kamar mai yin bacci, batasan sanda ya shigo class din ba.
Ya nemeta a waje bai ganta ba shiyasa yai tunanin ajin, kallanta ya tsaya yi yana murmushi, a hankali ta bude idanunta dan jin kamar ana kallanta.
Idanunta ne suka sauka akan fuskarsa shagwabe fuska tai dan ta tabbatar kila tunaninsa da takeyi ne yasa take ganin kamar shine.
Maida idanun tai zata rufe yace " fushi ake da ni ne?"
Da sauri ta bude idanunta tana kiftasu, sannan tai saurin komawa ta zauna, Sagir yace " me kike a class ke kadai?"
Batasan me ya sameta ba kawai ganintai ta wani hade rai wai ita a dole an mata laifi.
Sagir yace "Da alama wannan Malamin yayi laifi kenan?"
Kallansa tai fuska a hade tace " ba kai bane dazu ko kallan inda nake bakai ba?"
Tayi mamakin canzawar ta da kuma yanda take magana, a ranta tace "Lalai Jalila wato kin zama kwarariya."
FSagir samun kansa yai da darawa sannan yace " Nayi laifi, sai dai kin manta dazu Uncle Sagir ne malamin student a ajin?"
Tace "Yanzu fa?"
Yace "Yanzu kuwa Urs Sagir ne."
Da sauri ta sa hannu ta rufe fuskarta.
Kallanta ya sakeyi yace " ba haka bane?"
A hankali tace "Hakane."
Murmushin jin dadi yai sannan yace " tunda na ganki hankalina ya kwanta dan dama Abbana zan raka wani guri, nace bari nazo na ganki."
Kallansa tai tace "Okay, sai Monday kenan."
Yace "Kai! Har sai monday fa ko?"
Tace "ka manta yau friday?"
Fuska taga ya canza yace "gashi naga alama ke ko yar wayarnan baki dashi, anya zan iya jure missing dinki har sai monday?"
Kanta ta sunkuyar kasa tana murmushi, ajiyar zuciya yai sannan ya matso daf da ita yace "bari nai full charge yanda zan cancana battery dinA."
Kallansa tai sannan ta maida idanunta kasa tana murmushi.
Ido ya kura mata sosai sannan ya ce "Na tafi."
Sai dayaje kusa da kofa sannan tace "sai anjima."
Juyowa yai sannan ya juya ya tafi.
Ta window ta bishi da kallo, wani zazzafan so na ratsata.
Sam ta shagala da tunani kafin ta farga ta fito da sauri,
Tafi minti goma a tsaye taga dai ba alamar su Safeena, sannan ba alamar ma d'alibai suna wucewa, lalai ta tsaya soyayya antafi an barta, yau tana cikin wani hali dan tasan masifa kam ba'a magana.
Tana tafe tana dan mitocinta ita kadai..........
************
Inna ce ta kalli Sani sannan ta kalli takardar daya kawo mata dauke da sunan Taura da number sa.
Tace " da ka sake bincike ba wani abu game da rayuwarsa da ta kyalansa bayan matsalar yaran?"
Sani yace "eh gaskiya ba wani abu special, sai...."
sai kuma ye " ba ma dai komai."
Tace "da ke zaka fada?"
Yace dama kamar yaransa maza biyu ne, 'yan biyu babban Hassan sai kaninsa Husaini, sai dai jiya sai aka cemin wai Hassan ne da Sagir sai macen.
Inna tace " ko dai kaine ka manta ba?"
Yace "zai ita yiwuwa inaji Husainin tun yana karami ya rasu."
Tace " Dama ai maza biyu mace d'aya kacemin."
Yace "hakan na sani amma nadauka 'yan biyun ne ashe wa da kani ne."
Inna ta jinjina kai cikin rashin damuwa tace " ba wani abu bayan nan?"
Yace "babu."
Nan ta saka number a wayarta sannan ta anna dialing.
Sai atai ringing hudu sannan ya d'aga.
A banngarensa yana zaune a bayan mota shi da Ummy, sai Sagir dake zaune a mazaunin driver shi kuma hassan na gefe, suna hanyar zuwa asibiti.
Yana daga wa Inna tai sallama,Abba ya amsa sannan yace "ban gane ba."
Inna tace " Taura nice Hajiyar grain."
Sai daya danyi nazari na wasu dakiku kadan sannan yace "Hajiya ina wuni?" Yai magana tare da canza yanayin maganarsa zuwa girmamawa."
Inna ta amsa sannan tace " Taura ganinka nake san yi ina fatan zaka bani lokaci."
Yace " Haba Hajiya, kina wani gari ne?"
Tace ina kano, ina neman alfarma ganinka sanda kake da lokaci.
Yace " yau dai inada abinyi, sai dai banaji gobe akwai abinda zanyi, a ina zamu hadu?"
Ya fada yana kallan Ummy, tace " gida na zakazo ko nice zanzo ko kuwa a wani gurin zamu hadu?"
Yace " a'a ba matsala ni zan zo."
Tace "Nagode Taura zan turoma da address din gidan."
Ya amsa da to sannan ya kashe wayar, Hassan ya kalla wanda idanunsa ke rufe kamar me bacci sai dai kowa na cikin motar yasan ba bacci yake ba, Ummy ya kalla ya shiga fada mata wacce ta kira.
Gate din wani katon asibiti naga an bude musu, Sagir ya shiga da motar.
*************
Jalila kam taci uwar tafiya kafin ta isa gida, duk ta gaji tayi ligib.
Tana shiga ta tadda Mumy a bangarensu, gabanta ne ya fadi sannan ta kalli Goggo wanda kuka ne kawai batai ba amma da alama daurewa kawai takeyi.
Mumy na ganinta tace "kin dawo daga yawon iskancin?"
Jalila fuska ta canza sannan ta kalli Goggo wacce ta tabbatar an kare mata cin mutunci ne, tace " Mumy ban gane b....."
Marin data kifa mata ne yasa ta kasa karasawa sannan ta rike kuncinta, Mumy tace " ce miki akai nan gidan karuwai ne? Ko me?"
Mamaki ya kama Jalila tace " Mumy ban ga........."
Wani marin ta kara kifa mata tace "a gidan ubanwa kika tsaya? Kungurmar munafuka? Dama kwanakin nan na kula bakyasan dawowa tare dasu Safeena saboda kina yawon bin maza."
Cikin wata irin kakkausar murya Goggo tace " RAMLATU!"
Kallan Goggo sukai a tare, dan Jalila bata taba ganin ran Mumy ya baci ba haka.
#ONELUV💕
[08/10, 19:18] +234 816 365 0557: 🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *AyusherMohd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
*NO 7*
Goggo cikin jin zafin kalaman Mumy tace "Ta ya zaki kira yarinya ta da haka? Kina tunanin 'ya'yanki sunfi na wa ne? A koda yaushe ina jure komai ne badan banajin zafin abinda akema Jalila ba sai dan ina tunanin kila hakan shine zai kawo salama a zuciyarta, komai da kika gani inayi inayinsa ne domin ta, taya ma zaki kalli 'ya a gaban uwarta ki kirata da wadan nan munanan kalaman?"
Mumy ba shakka ta dan tsorata, ta daure tace " ni kike yima fada? Kijira ni."
Tafada tare dayin waje da sauri, tana fita Goggo ta rike kirjinta wanda ya mata wani irin nauyi, ga wani irin dum na tsananin ciwon kai daya fara sara mata, Jalila ta karasa kusa da ita tare da rungumeta tace "Goggo na."
Cikin shagwaba tai maganar, Goggo ta daure dan batasan Jalila ta gane batada lafiya tace " Karki damu, ko me za'amin indai har akanki ne zan ita jure komai."
Jalila ta kwantar da kanta akan kafad'ar Goggo cikin tausayama kansu.
Banko kofar da akai ne yasa ta d'ago da sauri cikin tsoro, Dady ta gani bayansa Mumy ce.
Jalila da sauri ta mike ta tsaya a gaban mahaifiyarta alamar kareta tace "Dady kome ya faru laifi......."
Wani wawan mari daya kifa mata sai data fadi kasa, Goggo ta d'agota da sauri tana tambayarta.
Dady cikin tsananin bacin rai ya kalli Goggo yace "uban wa ya baki dama ki cima matata mutumci?"
Goggo ta kalleshi tace " ni duk mutuncin data cimin bai zama laifi ba kenan?"
Yace " Me yasa bakya abu da tunani? Ko kuwa kwakwalwarki ce bata aiki? Gidan da kike zaune,abincin da kike ci, kayan da kike sakawa, karatun 'yarki duk a cikin arzikin wa kike ci?"
Goggo tai shiru tare da maida kanta kasa, sannan tace " duk da haka banaji tanada damar cima 'yata mutunci...."
"Yanzu yarinya tayi laifi kina nufin tafi karfin a hukuntata ne ko me?"
Jalila ta mike da sauri ta rike kafafun Dady tace "Dady na tuba, dan Allah kayi hakuri laifinane."
Kafa yasa ya hankadata yace " gayyar tsiya."
Sannan ya juya ya kalli Mumy ya dafa kafadarta yace "muje ciki ko?"
Yi tai kamar me share kuka tace "Ba sai danace kayi hakuri ba?"
Juyowa yai ya bugama Jalila wani kallo na takaici daga ita har Goggon sannan ya juya shida Mumy, har sun kai kofa Jalila tace " Dady me kake nufi da gayyar tsiya?"
Wani banzan kallo ya buga mata sannan yace " idan kika sake min magana da wannan vibe din wlh sai jikinki ya gaya miki, sannan kiyi gagawar tasowa kiyi aikin daya kamata kiyi."
Ya juya shida Mumy sukai gaba, Jalila da kallo kawai ta bisu idanunta na zubar da hawaye, kallan Goggo tai kamar zatai magana sai ta fasa, hawayenta ta share sannan ta mike ta daukoma Goggo maganinta ta mika mata tace "Goggo share kinsan halin Dady akwai saurin hawa kamar farashi, amma na tabbatar ba duk abinda ya fada yake nufi na, ai uba ubane ko?"
Goggo ta tabbatar tannayi dan hankalinta ya kwanta ne shiyasa itama ta daure ta daga kai tace "haka ne."
Jalila ta cire kayan makarantarta sannan ta fita.
Yau kam tana aiki tana zubar da kwalla, itakam dole me gaskiya tana gama makaranta tace Sagir ya fito suyi aure ta d'auke Goggonfa subar wannan dan iskan gidan.
************
A asibiti kuwa bayan sun shiga cikin office din wanda a saman kofar naga an rubuta Neurologist, suna shiga ya mike daga zaman da yake sannan ya saki fuskarsa yana cewa Welcome Taura.
Abba ya karasa kusa dashi ya mika mai hannu suka gaisa, sannan suka gaisa da Sagir, Ummy tace "Dr Ahmad mun sameka lafiya."
Yace "Lafiya kalau Hajiya ya mai jikin?"
Kallan Hassan tai sannan tai murmushi kawai.
Guri suka samu suka zauna ita da Sagir, shi kuma ya shiga wani dan d'aki shida Hassan da Abba.