← Book details Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 47 OF 53

Sashe 47

Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Tai alwala tazo tai sallah, jitai cikinta na karar yunwa, ta zo ta bude abinci zataci, gani tai ba alamar taba abincin, baici abincin dare ba kenan?

Kadan ta zuba a plate ta faraci.

Lomarta uku taji kakarinsa, wani sankamewa yakeyi, da sauri ta ajiye abincin ta matso inda yake.

  Gaba daya ya sai juye juye yake, yana girgiza kai alamar a'a, ga zufa tanata keto mai.

  Hannunsa ta riko tana tabashi, Yayah! Yayah!
Gaba daya ba alamun yanajinta, kansa ta kwantar a kan cinyarya dan murkususun dayake yasa kansa ya sauka daga kan pillow din, tasa hannu ta rike kansa dayan hannun kuma tasa a saman kirjinsa tana dan tabashi tare da kiran sunansa.

  Can kuma sai tadanyi kulhuwalahu da falaq da Nasi sai tadan tofa mai.

  A hankali taji ya daina motsumutson.

Idanunta na kansa ya ciciko saboda da tausayinsa, wannan wani irin abu ne ke damunshi? Me ya sameshi  abaya?

A hankali ya bude idanunsa, daidai lokacin kwalarta ta zubo ta zubu saiti idanunsa, wanda yana rufe ido ta zubo a bayan idansa.

  Idanunsa ya sake budewa ya kalleta, dayan hannun data rike kansa dashi ta saki ta share hawayenta sannan ta kalleshi tace "Yayah!"

Idanunsa ya lumshe yana kallanta kamar yanda take kallansa cikin sansanyiyar murya mai kamma da rada yace "sai yaushe ne zaki daina saurin kuka?"

Tace " kukan ne bakaso nayi?" Itama a hankali tai maganar tana kallansa.

Mamaki ne ya kamata dataga ya daga kai alamar eh, tace "meyasa?"
Ya dan girgiza kai kadan yace "ban sani ba nima, sai dai I don't like it."

  Kallansa tai tare da neman zare hannunta daga kan kirjinsa.

Hannu yasa ya tsayar da hannu yana kallanta yace " yanzu kukan me kikeyi?"

Tace "meyasa kakesan sani?"
Yace "Hmm kawai, saboda sai naji ne zansan abinda ya dace nai."

Hannunta ta nemi janyewa tana cewa "me ya faru dakai? Duk sanda kake abin nan kamar wani abu kake tunani."

  Shiru yai bai bata amsa ba, kafin can yace " izinki nawa?"
Tace "mene?"
Yace "tambayarki nai, so nake nasan karatunki, na kula kamar bakiyi nisa ba."

Tadan sosa wuyanta da dayan hannun tace "bankai izu ko daya ba, a gida Goggo tadan koyamin na sallah."

  Idanu ya kura mata, wanda yasatai saurin juya kai yace "bakyajin zafin mahaifinki?"

  Tai shiru kafin tace "inaji, inaji sosai da har wani sa'in ganinsa ma banaso."

Yace "kenan ko me ya faru bazakiji haushi ba?"
Tace "me zakamai?"

  Mikewa yai daga kan cinyarta sannan ya saki hannunta yahau kan gado....
Da sauri ta taso tace "me zakayi?"
Yace "bakomai, fada kawai nai."

Jalila ta kalleshi alamar rashin gamsuwa.........

********

Dady kuwa yana saukowa daga gun Inna ya shiga daki kawai ya hau hada kayansa, Mumy ta shigo da sauri zatai magana taga yana hada kaya, a rikice ta rike hannunsa tace "Dear menene?"

Ture ta yai yace " menene? Da alama karshen zamana dake yazo."

Da sauri ta rungumeshi tace "menene? Kafi kowa sanin bazan iya rabuwa dakai ba, Inna ce? Itace?"

Yai shiru wai shi a dole ransa ya baci.
Da sauri ta fito ta nufi dakin Inna da gudu rai a bace.........

#OneLuv💕

🗯 *JALILAH* 🗯

Written By : *AYUSHER MUHD*
✔ote me on Wattpad : *Ayusher Mohd*

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)

*45*

Da karfi ta banko kofar dakin Inna, lokacin Inna na zaune tasa hannu tayi tagumi tana tunanin abinyi, yanda Mumy ta banko kofar ne yasa ta zabura ta kalleta tace "Lafiya?"

Mumy cikin bacin rai ta zauna a gaban Inna tace "Inna so kike kiyi ajalina?"

"Ajalinki kamar ya kenan?"
Tace "in ba so kike in mutu ba taya zaki nemi halakamin aure? Sanin kanki ne yanzu kinsan bazan iya rayuwar ba Abubakar ba, a da ma da 'ya'ya basu hadamu ba na kasa rabuwa dashi bare yanzu."

Inna ta katseta cikin fada tace "me ya fadamiki?"
Tace "ba damuwa ta bace da duk abinda kike tunani sai dai kiyi abinki ke kadai, dan wallahi bazan bari wani abu ya sameshi ba, in kuma so kike mu bar miki gidan to....."

Mamaki ya kama Inna ta kalleta cikin wani yanayi tace "Fatima ni kike fadama haka? Ni wacce ma sadaukar da komai dan ganin farincikin ki?"

Cikin masifa tace "kika sadaukar dame? Me kika sadaukar? Duk abinda kikeyi ba saboda kanki kikeyi ba? In har saboda nine ai da kin daraja Abakar kin bashi company din kamar........."
Marin data kifa mata ne yasa Mumy yin shiru, ta kalleta tare da rike kuncinta.

Inna ta kalli Hannunta dake rawa, dan ita kanta batasan ta mareta ba, cikin dana sani tace "Fatima......"

Mumy ta mike tsaye tana kallanta, hawaye sun cika mata ido tace " in har bakyasan in bar gidan nan ki ajiye duk abinda kike shirin yi." Ta juya tanaji tana kiranta bata amsa ba tai waje.

Inna ta bita da kallo jiki a sanyaye.....

Shikam Dady tana fita yai wata dariyar mugunta yace "Inna i am sry sai dai kin riga kin makaro akaina 'yarki da kikafiso a duniya zata iya juya miki baya."

Yanajin alamun bude kofar ya shiga kokarin zuge jaka, Mumy na shigowa ta sa hannu da karfi ta fincike jakar sannan ta rungumeshi tace "Dadyn Yasmeen me yasa baka tunani na in zaka aikata abu?"

Yace "tunanin naki ne yasani yanke wannan hukuncin, taya zan zubarma kaina mutunci? Bayan nasan ina zubar da mutunci na naki na zubar? Da ace kome zai faru zai tsaya akaina ni kadai bazai shafeki ko yaranmu ba wlh ba abinda bazan iya ba, amma ta yaya zan yarda in zubar da mutuncinki dana 'ya'yanmu."

Dagowa tai tana kallansa tace "to kamin alkawari ko me zai faru bazaka sake tunanin rabuwa dani ba."

Yace "na miki, yanzun ma ba'a san raina nake shirin tafiya ba."

Ta kara kankameshi tace "barni da Inna bazan kara bari ta wulakantamin kai ba"
Ya shafa kanta yana wani murmushin mugunta yace " taya zan yarda na zama sillan fada tsakaninki da mahaifiyarki?"

Tace " ba kaine silla ba dan dama na gaji da yanda take ma kamar wani bawanta."

Nan ya sumbaceta a kunci yace "i luv u Zarah."

Ta sakarmai murmushin so......
Nace ansha kauna😏

Inna kuwa Mumy na fita ta ture littatafan dake kan tabir din gabanta cikin takaici tace "Abakar how dare you!"

Kwafa tai tace " kana tunanin ka samu abinda kakeso? Inji wa?"

Ta sakeyin wata kwafa........

********

Zama tai a kusa dashi a kan gado yana kwance yana tunanin Zaliha, ji yake zuciyarsa kamar zata fashe da rashinta.

Ganin baimasan ta zo bane yasa tasa hannu ta tabashi.
Kallanta yai sannan ya kakaro murmushi yace "Yaushe kika shigo?"

Tace "me kake tunani?"
Kallanta yai jiki a sanyaye, murmushi tamai sannan ta kauda kai, a hankali yace "I am sry, i am really sry."

Kallansa ta sakeyi tace "me kake tunani game da mutanen nan?"

Ya mike ya zauna yace "amsar kudinmu zamuyi, inyaso company din nasu ya nukushe."

Tace "ayi haka kuwa?"

Yace " baki kula da rainin hankalin da suka mana ba? Sannan yarinyar nan da mahaifiyarta, gaba daya ba tausayi a harkarsu, Hajiya taban mamaki duk da nasan macece wace kanta yake a waye amma i didn't expect that from her."

Tace "na sani sai dai in muka duba abin ta wata fuska zamuga mu taimakonmu sukai, da farko dabadan sun yaudaremu ba da bamu san wacce zamu aurana Hassan ba, in muka duba saukin da muka dade muna nema akansa yanzu gashi abinda likitoci da dama suka kasa yi yarinyarnan a ciki wata daya ta mana, duk da bawai ya warke ne ba sai dai canjin daya samu nada yawa."

Abba yai shiru yana kallanta zuciyarshi na dana sanin abinda ya aikata mata, yace "yanzu me kike tunani?"
Tace "just live them."
Yace "kina nufin duk abinda sukai ya tashi a banza?"
Tace "ko daya sai dai ina tunanin mu barma Allah, yanda suka cutar da Jalila da mahaifiyarta Allah bazai barsu ba, mu murikesu, gatan da basu samu ba mu basu, mu jira hukunci Allah akan su."

Abba yai shiru sai kallanta kawai da yakeyi, tace "kallan fa? Shawarar batai ba?"
Yace "akoda yaushe in kina abu sai na dinga yin wani tunani, sau dayawa akance mata basukai maza zurfin tunani ba, sannan sai kaji namiji na ta aibata mace, in naji haka a koda yaushe sai insan Allah yamin baiwar da ba ko wani namiji yama ba, samunki a matsayin matata yana daya daga cikin abubuwan da nake alfahari dasu a rayuwata."

  Kallansa tai sannan tai murmushi tace " Kasan abinda yaban mamaki? Ban taba tunanin Hassan zai sauko kasa ba wlh, kasan kawai nama Jalila zancen ne amma a raina nasan bamai yiwuwa bane?"

  Abba ya kalli yanda taketa farinciki yace "ni kaina nayi mamaki, kinsan rabon da Hassan ya shigo falona kuwa harya zauna ya dade haka?"

Tace " kasan ya sauko ya gaida baban Jalila ran nan?"

Abba yai murmushi yace "da alama yanda nai dace da mata haka Hassan yai dace, sai muyi addu'a Allah yaba Sageer mace shima ta gari."

Tace "insha Allah."

Washegari.

Dakin Sageer ta nufa tasa hannu tai knocking.

Yana kwance akan gado ya taso ya bude mata.

Kallansa tai cikin kulawa tace "Sageer lafiya? Naga baka fito ba."

Ya kalleta yace "Ummy...."

  A rikice ta kalleshi tace "menene? Bakajin dadi ne?"

Yace "a'a kawai dai..."
Tace "na kula ma gaba daya yanzu kadan canza, Sageer menene ke faruwa?"
Yace "kai Ummy wacce canzawa?"

Tura kofar tai ta shiga dakin, binta yai ciki da sauri yana cewa "Ummy."

Hannu tasa ta zuge labulen dakin ta zauna akan kujera.

Ya matso yana cewa "Ummy!!!"
Cikin shagwaba ya kirata, ta harareshi tare da hard'e hannayenta tace " In baka fadaminba ba inda zani."

Dariya ya saka sannan ya zauna a kasa kusa da ita yace "shikenan sai muyi hira."
Tace "Sageer dan Allah meke damunka? Sai yanzu na fahimta sam da yake banda nutsuwa ban kula da canzawar dakai ba."

Yace "Ummy wlh ba komai, muje na tayaki aikin kitchen kafin sirikarki ta sauko."

Kallansa tai sannan tai murmushi ta mike ta fito, yabiyo ta.
Chapter 47 · 0% Book details