← Book details Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 21 OF 53

Sashe 21

Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kallan Mumy tai sannan ta amsa, ta kalli Adama kafin tai magana ma tace "tashi kije ana kiranki."
Jalila ta mike ta wuce.
Tana shiga d'akin Mumy ta rufe kofa sannan ta riko hannunta.
Gefen gado ta zaunar da ita ta rike hannunta duka biyun tace "Jalila? Kinji abu kwatsam ko?"
Jalila ta kalleta idanunta sun canza kala tace "Mumy ban fahimci abinda ke faruwa ba."
Mumy ta rungumeta cikin murya mai rauni tace "Jalila nikaina abin nan na rasa ta ina zan fara sanar miki, dangin mijin ne suka ce suna san auran cikin gaggawa, yanzu nan da kwana uku za'a........."
Yanda ta ture Mumyn daga jikinta ne yasa Mumyn yin shiru, Jalila bakinta na rawa tace "kwana uku?"
Mumy tace "kiyi hakuri Jalila, sadaukarwa ce kikayi don ceto mahaifiyarki, kinfi kowa sanin Inna inhar bakiyi abinda tace ba, tabbas zata daina biya ma Goggo kudin asibiti ne, sannan zata iya korarku daga gidan nan, kinsan dai ba lafiya ne da ita ba, kar kuje garin wahala ciwon ya cita har azo ana dana sani...."

  Wasu zafaffan hawaye ne suka zuboma Jalila, ta kara maimaitawa kwana uku?
Mumy tace " karki damu, mahaifinki ya yanke hukunci inhar akai auran kikaga ana cutar dake to ki sanar dashi shidakansa zai sa a raba auran."
  Wayyo yarinta da rashin tunani mai zurfi yasa Jalila tace "Haka yace ?"

Mumy tace "sosai, kina tunanin zai bari a cutar dake ne?"
Shiru tai tana kallan Mumy, Mumy ta mike ta bude drawer ta d'auko mata wani dankararen material mai duwatsu, tace " ki tashi ki shirya, kaninsa zaizo yanzu, insha Allah Jalila ba abinda zai faru dake, kidinga sa mahaifiyarki agaban komai."

  Jalila bakinta ma rawa tama kasa magana, Mumy ta mikar da ita tace "kiyi hakuri ki saka Jalila, dan tundazu akace ya taho."

Haka ta hau saka kaya tana kuka, tana gamawa Mumy ta mata kwalliya da kanta, ta fesa mata turare sannan ta d'aura mata d'ankwali.

Jalila tana zaune agaban madubi akai knocking, mai aikinsu ce tace mata wai yana falon baki.
Mumy ta kalleta tace "Jalila!"
Kallanta tai sannan tace "Mumy?"
Mumy ta kara rungumeta tace "Jalila ki yafemin wahalar da na baki a da, ni kaina ina dana sanin yin hakan, kishi ne yasani yin komai."

  Da yake yarinyace mai kishiriwar nuna mata kulawa, jitai gaba daya jikinta yayi sanyi balle dataga Mumy na matse kwalla.
Haka Jalila ta fito daga d'akin fa nufi falon bakin.

********

  Sagir na zaune yana waya da Abba, yace "Abba nifa kasan bansan me ake cewa ba?"
Abba yace "kai dai Sagir sai a hankali, to inkungaisa sai kai introducing din kanka, inkundan yi hira kadan sai ka bata kudin kace na kwalliya ne da wasu hidindimo, dama ai laifinkune da baku bata ba da wuri, sannan laifin yayanka ne da bashida aboki ko d'aya a duniyar nan."

Sagir yai murmushi yace "Abba bye na fara jiyo kamshin Amaryar mu."
Dariya sukai a tare ya juyo yana cewa "Abba sai.........."
Kallan da yake mata ne yasa ya kasa karasawa, Abba ya kashe waya yana murmushi.
A hankali ta shigo falon kanta a kasa, kusa dashi taje ta ajiye tiren dake hannunta.
Sannan ta dago dan gaidashi.

Sagir cikin mamaki yace "Jalila?"
Da sauri ta karasa dago da fuskarta tace "Uncle?"
Kallan juna sukai kawai sai sukai dariya a tare, yace "Jalila ta!"
Kanta ta sunkuyar sannan ta kalleshi tana murmushi tace "Uncle kaine dama? Ya akai kasan gidanmu?"

Yace "woah da alama we are made for each other, kinsan ban taba tunanin ganinki ba?"
  Samun kanta tai da zama a kasan gun, fuskarta dauke da tsantsar farinciki tace "Uncle ni kaina nayi mamakin ganinka."

Yace "wai ina kika shiga ne? Ko fishin ne yasa aka kashemin waya?"

Tace "Uncle wata matsala ce ta hanani magana dakai."
Shiru yai yana kallanta, yanayin fuskarsa ne ya canza, ido ya kura mata wanda haryasata tsarguwa, tace " ka ganni kamar bani ba ko?"
Idanunsa na kanta sai yanayin fuskarsa dake kara canzawa, a hankali yace "Jalila nan ina ne?"
Tace "Gidanmu ne mana."

Wani mugun faduwa gabansa yai ya kara kallanta, itama yanzu jikinta yayi wani irin sanyi a hankali tace "bakasani ba?"
Bakinsa na rawa yace " ina Amar Amaryar?"

Jalila gabanta ne yai wani faduwa hannu tasa tadan tura jikinta tai baya kadan sannan ta kalleshi idanunta sun ciciko.

Sagir ya fara girgiza kai yana cewa "U are not the one ko? Na tabbatar ba ke bace ba ko?"

Hawaye ne suka fara zubo mata, idanunta na kansa, gaba d'aya jiyai wani irin zufa na keto mai yace "will you please tell me?"
Jalila ta runtse ido wasu hawaye suka zubo mata tace "Uncle i am sorry."

Sauko wa yai ya zauna a kasa sannan ya sa hannayensa ya shafi fuskarsa, kallanta yai cikin wani yanayi mai wuyar fassarawa yace "Jalila kinsan waye Angon?"

Kai ta girgiza tana hawaye tace "bansashi ba kuma bana sha'awar saninsa Uncle, kai nake so kai kadai nakeso Uncle na rasa yanda zanyi, rayuwar........."
Tana kokarin sanar dashi rayuwar Goggonta, sai jitai yace "Yayana ne fa."

A firgice ta bude idanunta, tace "me kace?"
Idanunsa ya rufe sannan ya bude yace "Jalila he is my brother."

Mikewa tai tana kallansa tace "brother? Ha kana nufin yayanka ne gidanku d'aya? Kenan zuwanka gidan nan a matsayin kaninsa kazo?"

Sagir ya rufe idanunsa cikin takaicin abinda ke faruwa?
Meke faruwa?
Yau me takeji haka?

Mikewa tai da sauri zata fita.

Jitai yace "He is someone whom i love alot."
Tsayawa tai cak ba tare da ta juyo ba, idanunsa ne suka zubo da wasu kwalla yace "He is someone whom I respect alot."

Yacigaba "He is someone whom I can't compare to anyone, i can sacrifice everything for his happiness."

Jalila ta juyo da sauri tace "me kake so kace?"
Idanu ya rufe wasu hawaye suka zubomai yace "Jalila bazan iya fad'a miko komai ba ayanzu, sai dai a hankali zaki fahimci abinda nake nufi ba sai dai bazan taba zama dalilin da zai zama silar bakincikin zuri'ar mu ba."

Kallan mamaki Jalila takemai, sai hawaye dake ta gudu a idanunta tace " Kana san kaima kace inyi hakuri da auran kenan?"

Sagir ya taso a hankali yazo inda take, kallanta ya shiga yi hakan yasa ta rufe idanunta tana hawaye.

Jin batajin motsinsa ne yasa ta bude idanunta a hankali, me zata gani? Sagir ta gani gwiwowinsa a kasa.

Da sauri ta ja baya tace "Uncle me kenan?"

Sagir yace "That is how much he means to me."

Jalila kallan tsoro ta fara mai, tama kasa magana sam, sai kai da take girgizawa a ranta tana cewa "banda kai Uncle, Please banda kai, ko kowa zai fada Please banda kai, Please ku tasheni daga baccin da nakeyi."

Sagir a ransa yana hango abinda zai faru inhar ya nemi bin zuciyarsa, yanzu ma da ya ya yayan nasa ya yarda? Sannan inya tuno da tashin hankalin da iyayensa ke ciki da abinda Hassan yamai a rayuwa bayaji akwai wani abu a cikin duniyar nan da zai kasa barmai, inya tuno da rashin lafiyarsa kuwa tabbas mace kamar Jalila itace best choice, sai dai kai fa?"

Abinda zuciyarsa ke fadamai kenan, muryar Jalila yaji tace "Uncle have you ever love me?"

Kallanta yai yana murmushin takaici, tace " me yasa kowa baya tunani na? Me yasa kowa yake san tsaramin rayuwata? Me yasa kowa yakesan ya zama nice mai sadaukarwa? Me yasa kowa yakesan yin amfani da ni?"

Tsugunawa tai a gun kawai tasa kuka.

Gana daya ya rasa yanda zaiyi, harcikin zuciyarsa yakejin kukanta.

Baice mata komai ba sai tafasa da tasa zuciyar takeyi.

D'agowa tai ta share hawayenta kawai ta meke zata fita.
Sagir har ya kai hannu zai riko mayafinta sai ya fasa.
Cewa yai "Jalila!"
Kallansa tai sannan tace "zan shiga ciki."
Yace " bamu gama magana ba."
Tace " na fahimci me kakeso kacemin."

Yace "Akwai sakon dana kawo miki."

Cikin mamaki ta kalleshi, tana kallansa ya mike yaje inda yake a zaune dazu ya d'auko wata yar karamai jaka ta kwali sannan ya mika mata.
Hannu tasa ta amsa sannan ta kalleshi, bai saki jakar ba yace "Jalila Please."
Kallansa tai bakinta na rawa tace " zan shiga ciki."
Sakin jakar tai, hakan yasa yai saurin mika mata yace "Yaya yace inkawo miki na hidindimo sannan yace kiyi hakuri bai samu zuwa ba rannan, da kuma yau."
Jalila ta kalleshi kawai dan tama kasa magana.
Juyawa yai da sauri, kallan bayansa tai sannan ta fita.

#OneLuv💕
[08/10, 02:13] ‪+234 803 222 1758‬: 🗯 *JALILAH* 🗯

Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*

(_D home of expert and perfect writer's_💡)

*No 21*

   Tana tsaye har ya fita daga falon, jitai kanta yayi wani irin sarawa kawai ta zube agun ta zauna, yanzu kam hawayen ma sun kame, sam ta kasa yinkukan, batasan sanda Mumy ta shigo falon ba.
Sai jinta tai tana cewa "Dubu d'ari da Hamsin!"
Lalai mutanen nan.
Kallanta tai sannan ta kalli kudin hannunta, jakar da Uncle ya mika mata ne, har yaushe Mumy ta shigo ta amshi jakar?
Mikewa tai dakyar sannan ta fita itama ta baya tana layi, Mumy ko ta kanta batai ba ta fita falo, ta haura sama.

Bangarensu ta nufa kawai ta zube a kasa ta kwanta, me ke faruwa da ita? Uncle? Dady? Mumy? Inna? Me yasa kowa yake san tsara mata abinda yaga dama? Me yas ba wanda yake tunanin farincikin ta?"

Wasu zafaffan kwalla ne suka gangaro mata, tana nan azaune sam batasan sanda bacci yai gaba da ita ba.

**********

  Sagir kam tana fita daya shiga mota ya ja ta da gudu, gaba daya ya rasa tunanin me ya kamata yai, ta ina zai fara iya zama gida d'aya da Jalila? Sannan amatsayin matar yayansa?

Wani irin burki yaja, ya gangara gefen titi sannan ya kashe motar.
Kansa ya kifa akan sityarin motar yana tunano kalaman Jalila, idanunsa ya runtse cikin tsananin damuwa, yace a fili "Am sorry, i am really sorry Jalilah."
Chapter 21 · 0% Book details