Sashe 41
Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kallan Jalila yai rai a bace yace "Wai Habiba ba magana nake miki ba? Sai dai ki kalleni? Ko kema munafircin uwar taki zaki koya?"
Jalila cikin tsoro ta kalleshi, hannunya daga a zuciye zai kai mata mari.
Jiyai ance " da alama sararka kenan?"
Juyowa tai da sauri ya kalli mai maganar, Jalila ma kallansa tai kawai sai ji tai hawaye sun zubo mata.
Karasowa yai cikin tafiyarsa ta isa sannan ya kalleta yace " tashi."
Mikewa tai tana kallansa, yace "bakiji me nacemiki ba ne da zaki zo?"
Tace "me kace?"
Yace “sau nawa zan ce miki ki canza tone in zakiyi magana? Meyasa bakyayi da confidence?”
Kallan juna sukai, hawaye ya gangaro mata, juyawa yai ya kalli Dady wanda yai tsuru tsuru.
Hassan ya kalleshi yace “ gobe zanzo muje dakai asibiti inda aka kwantar da mahaifiyarta, a gabanka zakasa hannun sallama mu amsheta.”
Dady yace “me kake nufi?”
Yace “abinda zuciyarka ta baka, u don’t deserve to be a father nor a husband.”
Kallan Jalila yai yace “wuce mu tafi.”
Kallan Dady tai gabanta na ci gaba da faduwa, Hassan ya kalleta ya mata alama data fara fita, nan ta fita tana waiyaye.
Tana fitowa daga bangaren falon taga Sageer a tsaye a jikin bango.
Yana ganin ta fito ya matso da sauri yace “ Jalila”
Hawayenta ta share sannan ta kalleshi, yace “menene?”
Kallansa tai kamar zatai magana sai kuma ta fasa ta juya tai gaba, Sageer yace “Akwai abinda ya faru ko? Naga yaya ya shiga kuma shi bai fito ba.”
Juyowa tai ta kalleshi sannan ta juya kawai ta hau sama da gudu.
A falo kuwa
Hassan ya kalli Dady yace “me ka samu, na saida yarka dakai?”
Dady yace “me kake nufi?”
Hassan yace “yanda kai da manyanka iyayen gidannka kuke nunawa, kunayi ne kamar kun samu wani abu sosai wanda yasa kuka bada yarku.”
Dady ya kalleshi yace “Hassan ta ya zaka ce haka? Kana so kace rashin so ne yasa muka aurar da ita?”
Yace “sosai, inba rashin so ba kun taba tambayar ya mijin nata yake? Wasu halaye gareshi? Me nene aikinsa? Ya mu’amalarsa da jama’a take? Duk kunyi wannan tambayar? A matsayinka na uban yarinya?”
Dady ya kalleshi yace “Inna tayi bincike ita ce tasan mahai.......”
Ya katseshi rai a bace “wacece ita? Menene matsayinta agun Jalila?”
Dady yace “bangane ba?”
Hassan yamai wani kallo yace “ karka manta gobe zanzo in banzo ba jibi zanzo, in kuma har kukai tunanin yin abinda bai kamata ba, zan baku mamaki.”
Ya juya bai jira mai zai ce ba ya fita.
Dady haka ya fito gaba daya kansa yayi nauyi, Sageer ne kawai a falon yamai sallama ya fita, yana cemai ya gaida Taura.
Mota ya shiga yai gaba.
Sai daya je kofar gida sannan yai parking a gefen mota ya kashe motar ya fito yana tunanin abinda zai fi mai mahimmanci, danshi rayuwarsa itace gaba da komai, mai zaiyi dan cigaban sa?
Hassan kam yana haura beni kansa na wani juyawa da kyar ya kai kansa daki yana shiga ya kwanta.
Jalila na falo tana ganinsa ta taso dan dama ta kasa ko zama ne.
Yana shiga a shiga dakin itama, akwance ta ganshi akan gado, taje kusa dashi tana san mai magana sai dai ganin idanunsa a rufe tasan bayasan magana, balle ya juya mata baya.
Ta dan dade a tsaye kafin ta fito.
Karfe tara tai shimfida ta kwanta, shikam tunda yai sallah ya sake kwanciya bai sake ko motsawa ba balle ta samu damar magana.
Shikam takaicin abinda ke faruwa a gidansu ne yake damunshi, meke damun Abba? Meyasa ita wannan rayuwarta take a cude? Meyasa abubuwa ke faruwa haka? Yau ce rana ta farko dayai fada da magana mai tsayi haka, gaba daya kansa wani irin sarawa hakeyi, ya dade sosai kafin bacci ya daukeshi.
Jalila kam ta dade a kwance kamar tana bacci, me suka fada da bata nan? Taya uba wanda ya haifeta zai dinga mata haka? Hawayenta ta share data tuno rayuwar da mahaifiyarta tai, lalai bazata bari Goggo ta cigaba da zama dasu ba.
Juyawa tai saitin da Hassan yake, ta haska wayarta, ganinsa tai a dukunkune ta mike ta dan rage A.C din dakin sannan ta matso inda yake, kansa baya kan pillow din, in dagashi? Ganin yanda ya kwanta a takure.
Hannu tasa a hankali ta daga kansa ta daura akan pillow din sannan ta juya ta kwanta.
Shikam tana tabashi yaji ta, har sai data kwanta idanunsa na bude juyawa yai shima saitin da take kwance, duk da ta kashe hasken dakin ba ganinta yakeyi ba, sai dai ya samu kansa da tsurawa gun ido kafin ya maida idanunsa ya rufe.
*************
A kasa kuwa, Ummy ce tasa kayan baccinta ta sa hijab tana neman fita daga dakin.
Abba ya kalleta yace “ina zaki?”
Tace “Dakin Ameera, ni kam kamar munyi kuskure da mun sani dakin can mun gyarashi.”
Kallanta yai yanda take mai magana kamar bawani abu na sabani a tsakaninsu.
Abba ya kalleta zaiyi magana wayarsa tai kara.
Kallansa tai tace anama waya, ta juya ta fita.
Zaliha ce, kashe wayar yai gaba daya sannan ya mike ya fito daga dakin.
Dakin Ameera ya shiga, Ummy tana kade gadon ya bude kofar, kallansa tai tace “ya akai? Ko akwai abinda kakeso?”
Abba ya kalleta sannan ya shigo ciki ya zauna akan gadon yace “ Kinsan gwara kiyi fada?”
Tace “fada kamar yaya?”
Yace “wannan abinda kikeyi it really scared me, gwara ki nunamin ranki ya baci in ma hakuri ne na baki.”
Tace “ munyi fada dakai ne?”
Kallanta yai, tace “ kai da Hassan ne kukai fada akai na wanda ni banaso, sai dai ya zanyi? Banaso naga kuna irin wannan akaina, tunda nake dakai na taba hanaka aure?”
Yace “ kece kuwa kike da yanda zakiyi tunda akanki akeyi, ke kadaice kike da dama hana fadan, sannan maganar aure nasan tunda nake dake ban taba sha’awar kawo wata mace gidana ba, yanzun ma ni kaina bansan meke damuna ba.”
Ummy ta kalleshi tace “ saboda kanasan ta shine ka hauni da fada waccan zuwa akan zaka koma Abuja, sannan yanzu kace bakasan meke damunka ba? Ni mubar wannan maganar, ni matsalata da damuwa ta akan Hassan ne, dan Allah ka daina barin yana sanin abinda ke faruwa a tsakaninmu, kafi kowa sanin halinsa in har yasan ina cikin damuwa, banaso Sageer ko Ameera ma susan wannan maganar, na rokeka da Allah, in aure zakayi kayi, wannan ra’ayinka ne sannan rayuwarka ce amma Please karka bari yarana su shiga wani hali a dalilin abinda kakeso.”
Abba ya runtse idanu cikin takaicin abinda ya dade yana ginawa, wato farin cikin gidansa na neman wargajewa a dalilinsa.
Ummy ya kalla cikin wani yanayi na tausayawa sannan yace “Maimuna ina cikin wani hali........”
Yanda yai maganar ne yasa ta tsaya tana kallansa sai dai tausayinsa ne ya kamata, dan bazata taba manta irin wannan muryar ba daya zo mata da ita a can baya shekaru masu yawa, a lokacin kalmar nan sai data sata kuka mai yawa, yanzun ma hannunta tasa akan nashi sannan ta zauna a gefensa tace “ In kanasan ta ka aureta, in dai shine matsalar, ni zanma Hassan magana, sai dai kafi kowa sanin baka isa ka zaunar da ita a gidan nan ba, in har baso kake danka ya mata illa ba.”
Kallanta yai cikin rauni yace “ba santa ne matsala ba, ni gaba daya abinda ke damuna ne matsala, n rasa a yaushe na fara santa, a yaushe naji in banganta ba bazan iya rayuwa ba, na rasa a yaushene na fara amsa mata akan duk abinda tazomin dashi.”
Ummy ta kalleshi cikin mamaki tace “me kake mufi?”
Ya kalleta yace “kizo mu kwanta, banajin dadin abinda mukeyi, me kike tunanin zai faru in Hassan ya ganki anan? D’a nane sai dai duk duniya nafi shakkarsa akan kowa, sannan shikuma indai akanki ne ba abinda bazai yi ba.”
Ummy bata musa ba ta mike sukai daki, kwanciya sukai, tace “baka fadamin matsalar ba.”
Yace “gobe zan gaya miki mike faruwa wanda na kasa ganeshi.”
Ummy tace “Allah yaa kaimu.”
Nan sukai bacci............
Sageer kam gaba daya ya kasa bacci, daga bayama mikewa yai ya zauna akan gado ya kunna fitila yana tunani, anya bashine sillar komai ba?
Gaba daya tausayin Jalila ya hanashi rintsawa......
******
A can gidan Inna kuwa, Inna sai kiran wayar Dady take bai dauka ba, yana kallan kiranta yaki dauka, sai data kira sau hudu sannan ya daga yace “gashinan zuwa.”
Ajiye wayar yai ya koma mota, dan ya gama tunanin mafitarsa, yasan kuma yanda zai buloma abinda ke faruwa dashi..........
#OneLuv💕
🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
✔ote me on Wattpad : *Ayusher Mohd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
*40*
Washegari......
Jujuya cokali kawai takeyi a cikin cup din tea din, jefi jefi tana kallansa ta kasan ido tanasan mai magana, shikuma yana zaune a kasan yanacin abincinsa kamar ba wani abu dake damunsa.
Can dai ta tattaro dauriyarta tace "hmm yaya nace......"
Kallan daya mata ne yasa ta maida bakinta ta rufe tare da kallan cup din ta cigaba da juya cokalin.
Yana gama ci ya mike ya shiga toilet, wanka yai sannan ya fito.
Kallansa tai ta ganshi daga shi sai towel dake daure a kasa, da sauri ta juya baya tare da rufe fuskarta da tafin hannunta bai bi ta kanta ba harya saka kayansa, sannan ya dawo gaban madubi yana shafa mai, yana gamawa ya fefesa turare.
Jalila ta juyo ta kalleshi, matsowa kusa dashi ta danyi kadan tace "Yaya bakacemin komai ba."
Bai tanka mata ba ya dau wayarsa da makullin mota ya fita, tana tsaye ya rufo kofar.
Kallan kofar tai cikin mamaki a fili tace "mekenan?"
Takaici ne ya kamata ta zauna a bakin gadon dabas tama rasa me zata ce.
Jalila cikin tsoro ta kalleshi, hannunya daga a zuciye zai kai mata mari.
Jiyai ance " da alama sararka kenan?"
Juyowa tai da sauri ya kalli mai maganar, Jalila ma kallansa tai kawai sai ji tai hawaye sun zubo mata.
Karasowa yai cikin tafiyarsa ta isa sannan ya kalleta yace " tashi."
Mikewa tai tana kallansa, yace "bakiji me nacemiki ba ne da zaki zo?"
Tace "me kace?"
Yace “sau nawa zan ce miki ki canza tone in zakiyi magana? Meyasa bakyayi da confidence?”
Kallan juna sukai, hawaye ya gangaro mata, juyawa yai ya kalli Dady wanda yai tsuru tsuru.
Hassan ya kalleshi yace “ gobe zanzo muje dakai asibiti inda aka kwantar da mahaifiyarta, a gabanka zakasa hannun sallama mu amsheta.”
Dady yace “me kake nufi?”
Yace “abinda zuciyarka ta baka, u don’t deserve to be a father nor a husband.”
Kallan Jalila yai yace “wuce mu tafi.”
Kallan Dady tai gabanta na ci gaba da faduwa, Hassan ya kalleta ya mata alama data fara fita, nan ta fita tana waiyaye.
Tana fitowa daga bangaren falon taga Sageer a tsaye a jikin bango.
Yana ganin ta fito ya matso da sauri yace “ Jalila”
Hawayenta ta share sannan ta kalleshi, yace “menene?”
Kallansa tai kamar zatai magana sai kuma ta fasa ta juya tai gaba, Sageer yace “Akwai abinda ya faru ko? Naga yaya ya shiga kuma shi bai fito ba.”
Juyowa tai ta kalleshi sannan ta juya kawai ta hau sama da gudu.
A falo kuwa
Hassan ya kalli Dady yace “me ka samu, na saida yarka dakai?”
Dady yace “me kake nufi?”
Hassan yace “yanda kai da manyanka iyayen gidannka kuke nunawa, kunayi ne kamar kun samu wani abu sosai wanda yasa kuka bada yarku.”
Dady ya kalleshi yace “Hassan ta ya zaka ce haka? Kana so kace rashin so ne yasa muka aurar da ita?”
Yace “sosai, inba rashin so ba kun taba tambayar ya mijin nata yake? Wasu halaye gareshi? Me nene aikinsa? Ya mu’amalarsa da jama’a take? Duk kunyi wannan tambayar? A matsayinka na uban yarinya?”
Dady ya kalleshi yace “Inna tayi bincike ita ce tasan mahai.......”
Ya katseshi rai a bace “wacece ita? Menene matsayinta agun Jalila?”
Dady yace “bangane ba?”
Hassan yamai wani kallo yace “ karka manta gobe zanzo in banzo ba jibi zanzo, in kuma har kukai tunanin yin abinda bai kamata ba, zan baku mamaki.”
Ya juya bai jira mai zai ce ba ya fita.
Dady haka ya fito gaba daya kansa yayi nauyi, Sageer ne kawai a falon yamai sallama ya fita, yana cemai ya gaida Taura.
Mota ya shiga yai gaba.
Sai daya je kofar gida sannan yai parking a gefen mota ya kashe motar ya fito yana tunanin abinda zai fi mai mahimmanci, danshi rayuwarsa itace gaba da komai, mai zaiyi dan cigaban sa?
Hassan kam yana haura beni kansa na wani juyawa da kyar ya kai kansa daki yana shiga ya kwanta.
Jalila na falo tana ganinsa ta taso dan dama ta kasa ko zama ne.
Yana shiga a shiga dakin itama, akwance ta ganshi akan gado, taje kusa dashi tana san mai magana sai dai ganin idanunsa a rufe tasan bayasan magana, balle ya juya mata baya.
Ta dan dade a tsaye kafin ta fito.
Karfe tara tai shimfida ta kwanta, shikam tunda yai sallah ya sake kwanciya bai sake ko motsawa ba balle ta samu damar magana.
Shikam takaicin abinda ke faruwa a gidansu ne yake damunshi, meke damun Abba? Meyasa ita wannan rayuwarta take a cude? Meyasa abubuwa ke faruwa haka? Yau ce rana ta farko dayai fada da magana mai tsayi haka, gaba daya kansa wani irin sarawa hakeyi, ya dade sosai kafin bacci ya daukeshi.
Jalila kam ta dade a kwance kamar tana bacci, me suka fada da bata nan? Taya uba wanda ya haifeta zai dinga mata haka? Hawayenta ta share data tuno rayuwar da mahaifiyarta tai, lalai bazata bari Goggo ta cigaba da zama dasu ba.
Juyawa tai saitin da Hassan yake, ta haska wayarta, ganinsa tai a dukunkune ta mike ta dan rage A.C din dakin sannan ta matso inda yake, kansa baya kan pillow din, in dagashi? Ganin yanda ya kwanta a takure.
Hannu tasa a hankali ta daga kansa ta daura akan pillow din sannan ta juya ta kwanta.
Shikam tana tabashi yaji ta, har sai data kwanta idanunsa na bude juyawa yai shima saitin da take kwance, duk da ta kashe hasken dakin ba ganinta yakeyi ba, sai dai ya samu kansa da tsurawa gun ido kafin ya maida idanunsa ya rufe.
*************
A kasa kuwa, Ummy ce tasa kayan baccinta ta sa hijab tana neman fita daga dakin.
Abba ya kalleta yace “ina zaki?”
Tace “Dakin Ameera, ni kam kamar munyi kuskure da mun sani dakin can mun gyarashi.”
Kallanta yai yanda take mai magana kamar bawani abu na sabani a tsakaninsu.
Abba ya kalleta zaiyi magana wayarsa tai kara.
Kallansa tai tace anama waya, ta juya ta fita.
Zaliha ce, kashe wayar yai gaba daya sannan ya mike ya fito daga dakin.
Dakin Ameera ya shiga, Ummy tana kade gadon ya bude kofar, kallansa tai tace “ya akai? Ko akwai abinda kakeso?”
Abba ya kalleta sannan ya shigo ciki ya zauna akan gadon yace “ Kinsan gwara kiyi fada?”
Tace “fada kamar yaya?”
Yace “wannan abinda kikeyi it really scared me, gwara ki nunamin ranki ya baci in ma hakuri ne na baki.”
Tace “ munyi fada dakai ne?”
Kallanta yai, tace “ kai da Hassan ne kukai fada akai na wanda ni banaso, sai dai ya zanyi? Banaso naga kuna irin wannan akaina, tunda nake dakai na taba hanaka aure?”
Yace “ kece kuwa kike da yanda zakiyi tunda akanki akeyi, ke kadaice kike da dama hana fadan, sannan maganar aure nasan tunda nake dake ban taba sha’awar kawo wata mace gidana ba, yanzun ma ni kaina bansan meke damuna ba.”
Ummy ta kalleshi tace “ saboda kanasan ta shine ka hauni da fada waccan zuwa akan zaka koma Abuja, sannan yanzu kace bakasan meke damunka ba? Ni mubar wannan maganar, ni matsalata da damuwa ta akan Hassan ne, dan Allah ka daina barin yana sanin abinda ke faruwa a tsakaninmu, kafi kowa sanin halinsa in har yasan ina cikin damuwa, banaso Sageer ko Ameera ma susan wannan maganar, na rokeka da Allah, in aure zakayi kayi, wannan ra’ayinka ne sannan rayuwarka ce amma Please karka bari yarana su shiga wani hali a dalilin abinda kakeso.”
Abba ya runtse idanu cikin takaicin abinda ya dade yana ginawa, wato farin cikin gidansa na neman wargajewa a dalilinsa.
Ummy ya kalla cikin wani yanayi na tausayawa sannan yace “Maimuna ina cikin wani hali........”
Yanda yai maganar ne yasa ta tsaya tana kallansa sai dai tausayinsa ne ya kamata, dan bazata taba manta irin wannan muryar ba daya zo mata da ita a can baya shekaru masu yawa, a lokacin kalmar nan sai data sata kuka mai yawa, yanzun ma hannunta tasa akan nashi sannan ta zauna a gefensa tace “ In kanasan ta ka aureta, in dai shine matsalar, ni zanma Hassan magana, sai dai kafi kowa sanin baka isa ka zaunar da ita a gidan nan ba, in har baso kake danka ya mata illa ba.”
Kallanta yai cikin rauni yace “ba santa ne matsala ba, ni gaba daya abinda ke damuna ne matsala, n rasa a yaushe na fara santa, a yaushe naji in banganta ba bazan iya rayuwa ba, na rasa a yaushene na fara amsa mata akan duk abinda tazomin dashi.”
Ummy ta kalleshi cikin mamaki tace “me kake mufi?”
Ya kalleta yace “kizo mu kwanta, banajin dadin abinda mukeyi, me kike tunanin zai faru in Hassan ya ganki anan? D’a nane sai dai duk duniya nafi shakkarsa akan kowa, sannan shikuma indai akanki ne ba abinda bazai yi ba.”
Ummy bata musa ba ta mike sukai daki, kwanciya sukai, tace “baka fadamin matsalar ba.”
Yace “gobe zan gaya miki mike faruwa wanda na kasa ganeshi.”
Ummy tace “Allah yaa kaimu.”
Nan sukai bacci............
Sageer kam gaba daya ya kasa bacci, daga bayama mikewa yai ya zauna akan gado ya kunna fitila yana tunani, anya bashine sillar komai ba?
Gaba daya tausayin Jalila ya hanashi rintsawa......
******
A can gidan Inna kuwa, Inna sai kiran wayar Dady take bai dauka ba, yana kallan kiranta yaki dauka, sai data kira sau hudu sannan ya daga yace “gashinan zuwa.”
Ajiye wayar yai ya koma mota, dan ya gama tunanin mafitarsa, yasan kuma yanda zai buloma abinda ke faruwa dashi..........
#OneLuv💕
🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
✔ote me on Wattpad : *Ayusher Mohd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
*40*
Washegari......
Jujuya cokali kawai takeyi a cikin cup din tea din, jefi jefi tana kallansa ta kasan ido tanasan mai magana, shikuma yana zaune a kasan yanacin abincinsa kamar ba wani abu dake damunsa.
Can dai ta tattaro dauriyarta tace "hmm yaya nace......"
Kallan daya mata ne yasa ta maida bakinta ta rufe tare da kallan cup din ta cigaba da juya cokalin.
Yana gama ci ya mike ya shiga toilet, wanka yai sannan ya fito.
Kallansa tai ta ganshi daga shi sai towel dake daure a kasa, da sauri ta juya baya tare da rufe fuskarta da tafin hannunta bai bi ta kanta ba harya saka kayansa, sannan ya dawo gaban madubi yana shafa mai, yana gamawa ya fefesa turare.
Jalila ta juyo ta kalleshi, matsowa kusa dashi ta danyi kadan tace "Yaya bakacemin komai ba."
Bai tanka mata ba ya dau wayarsa da makullin mota ya fita, tana tsaye ya rufo kofar.
Kallan kofar tai cikin mamaki a fili tace "mekenan?"
Takaici ne ya kamata ta zauna a bakin gadon dabas tama rasa me zata ce.