Sashe 3
Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Suna zaune ita da Zarah, duk wata hira da zata fito daga bakin Zarah na Saurayinta Nasir ne, Jalila ta juyo tace “Nikam Zarah anya Nasir na sanki kamar yanda kike sansa?”
Fuska ta canza tace “ wacce irin tambaya ce wannan?”
Jalila xatai magana Uncle Sagir ya shigo, da sauri suka mike suka gaida shi.
Idanunsa akanta ya fara sauka, a hankali wani murmushi ya banyana a fuskarsa.
Sannan ya basu damar zama.
“Mathematics” abinda ya rubuta kenan a blackboard sannan ya ruba “Quadratics Equation”
Sannan ya juyo da hankalinsa kan d’alibai, Jalila ta dago suka hada ido da sauri ta sunkuyar da kanta tana wata da yatsun hannunta, haka ya shiga yi musu examples.
Jefi jefi yana sauke idanunsa akanta haka itama, har ya gama period dinsa sannan ya ce a hada masa assignment din da ya bada.
Nan monitor ta mike ta hada, kallan Jalila yai yace “Habiba inasan ganinki biyoni da books din nan.”
Kallansa tai sannan tai saurin cewa “Yes Sir”
Tare da fitowa ta amshi littatafan.
Yana gaba tana dan binsa a baya sai jitaj yace “ yau saboda in kama wata nazo da wuri sai tai sa’a bata makara ba.”
Tace “wata? Ni?”
Ta fada tana kallansa,bai juyo ba sannan bai daina tafiya ba yace “ da yau na kamata lalai da shikenan na daina amsa ko gaisuwarta.”
Tace “ Na daina zuwa late insha Allah, sannan jiya ma tsautsayine.”
Yace “ a tare zamu gama, kuna gama exams ni ma ina kammala aikina.”
Murmushi tai batace komai ba.
Yace “ me kikeyi tsayawa yi in an tashi daga school kullum?”
Tace “ Kanena nake jira a tashesu sannan a daukosu sai su biyo ta nan mu tafi.”
Yace “Kannenki?”
Ita kanta taji abin ban barakwai sai dai ko ma menene ai kannenta ne, tace “eh”
Juyowa yai yace “ a wani school suke?”
Tace “Crescent International School”
Kallan mamaki ya mata sai dai bai kara cewa komai ba sai juyawa dayai, yana tafiya yana mamaki, kannenta na Crescent ita kuma tana makarantar Government?
Sai data ajiye mai books din sannan ta fito, tana tafe tana mamakin tambayoyin da Uncle Sagir ya mata.
Ana tashi sun fito ita da Zarah, Zarah na ce mata ni dazu me kike nufi? Ban samu munyi magana ba........
Nasir da ta gani a tsaye ne yasa ta dakama Jalila duka a kafada tace “ Jalila kinga!”
Jalila ta juya ta kalli yaran dake tsaye daga gefensu tace “ yayanki ne?”
Yace “My Nasir ne, da alama ya gaji da missing dina ne.”
Jalila ta kalli Nasir din sannan ta kalli Zarah wata dariya ta kirkiro wanda kana gani kasan ta dole ce tace “ Ohh shine Ur Nasir?”
Zarah ta hade rai tace “Meye hakan?”
Jalila ta girgiza kai tace “Kije naga ya kura miki ido kamar zai daukeki.”
Murmushi tai sannan tace “ Kawata kalleni fuskata batai komai ba?”
Kamar zatai kuka ta daga kai tace “Eh”
Zarah ta fara tafiya cikin canza salo, Jalila kallansu kawai take cikin mamaki, wannan ai da alama makaranta ya samu da wuri amma ta tabbatar baiba Zarah shekara biyu bama, dan ma tace a level 3 yake ne amma lalai da tace sa’ansu ne,lalai ansha yarinta shiyasa.
Tab itakam gaskiya bataji zata iya soyaya da sa’anta, ita tafisan saurayi kamar Uncle Sagir, da sauri ta girgiza kai tace “What am I thinking? Ahhhhh lalai banida kai.”
#OneLuv💕
🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *AyusherMohd*
*No 3*
Tana kallansu suna tafe suna rangaji irin na masoya, murmushi tai sannan ta koma gefe ta tsaya.
A hankali duk aka yoye tana tsaye, ganin rana ta fara dishashewa ne yasa ta daga kai ta kalli sama, hadari taga yana haduwa abinka da damina kan kace me gari yayi daki, da sauri ta juya ciki ganin iska mai kura tana tasowa.
Ji tai ta bugi abu, da sauri ta dago ta kalleshi.
Idanunsa na kanta, ta matsa baya da sauri cikin jin kunya, sannan tace "Sorry Sir"
Yace "anya yau sorry din nan zai karbu kuwa agurina? Da alama sai na hukunta mai laifin nan."
Kallansa tai sannan tace " Wlh ban ku........"
Yanda yake kallanta ne yasa ta kasa karasa maganar dake bakinta sannan tai saurin juyawa, dan ji take gabanta na faduwa.
Murmushi yai sannan yace "muje in kaiki gida."
Tace " Naam"
Yace "Baki ji bane ko bakya so ne? Hadari ne a garin in aka fara ruwa kina tunanin yanda zakiyi kije gida? Ko su Kannen naki ne bakyasan ki tafi ki barsu?"
Shiru tai tana dan nazari kafin tace " Nagode da kulawa Uncle Sagir sai dai in na tafi ba tare dasu ba fada za'amin."
Kamar zai sake magana sai kuma taga ya juya ya koma ciki, tana tsaye ya fito da lema ya mika mata bai jira tace komai ba ya hau mota yai gaba.
Da kallo ta bishi yau da mota yazo? Hmm ita kadai tasan cin zarafin da za'ama mahaifiyarta in har ta tafi.
Tana tsaye aka fara yayyafi da sauri ta bude lemarta ta shiga, kan kace me ruwa ya tsuge, ruwa ake mai karfin gaske wanda tana cikin lemar ma amma ba tsira tai ba, komawa gefe tai ta rakube.
Kamar motar zata tsaya sai taga ta yi gaba da gudu, cikin tsananin tsoro ta kalli motar tare da kwalla kara da karfi tace "Safeen ina nan fa......"
A cikin motar kuwa wanda Safeena tacema Malam Auwal da alama ta tafi ganin hadari, wanda akasan ranta ta tabbatar bata tafi ba, tsabar mugunta ce.
Haka ta rakube dan tsoro takeji ta koma cikin makarantar ita kadai, ganin a tsayen ma tsoro ya kamata kawai ta fara tafiya tana tafe tana kuka mai sauti, sai dai kasancewar karar ruwa bai sa tasan da karfi take kukan ba.
Yana zaune a cikin motarsa daga gefen titi wanda shi dama yafisan gurin shiru inda ba mutane, shiyasa mafi akasari zaka sameshi ne a zaune a cikin motarsa ya zuge glass kawai ya kwanta.
Jikin motar ta tsaya da taga ruwan ya dan yi sauki duk jikinta ya jike jagaf, ga lemarma sai lankwashewa takeyi saboda iska.
Juyawa tai ta kalli glass din motar, da yake motar mai tints ce sai ta shiga kallan kanta tana kara wani kukan,sam tunaninta bai kawo mata da wani a cikin motar ba.
Kallanta kawai yakeyi sai sharar kuka take wiwi.
Komawa yai ya maida kansa ya rufe idanunsa kamar mai bacci.
Kara juyowa yai ya kalleta, kuka take sosai, kamar dama neman kukan takeyi, haushi duk ya isheshi kamar a kansa take kukan, kofar mazauninsa ya bude, a tsorace ta kalli motar, kallansa tai a tsorace, sannan ta kalli motar .
Kallan tsoro tamai tace "Hmm hmm."
Hannunsa ya dago ya mata alama da ta matsa daga gun, tace "Ban gane me kace ba."
Alama ya sake mata da hannunsa akan tai gaba, sannan ya maida kofarsa ya rufe, da harara tabi kofar motar sannan tace " wannan kuma wani kwarantancen dan duniyar ne? Maganarce yafi karfin yimin ko kuwa tsabar rashin mutumci ne?"
Harara ta sake yi sannan ta juya, kallan motar ta sakeyi sannan tace "irin motar jiya"
Taja tsaki tace " da alama duk masu hawa irin motar nan basuda mutunci."
Sam ta manta da kukan da takeyi saboda masifa, tana tafe yayafi na digar mata tana yan mitocinta, sai da ta gama gajiya ligif sannan ta isa gida.
Goggo kuwa duk ta kasa zama saboda tsoro ganin yanda ake ruwa ga har yanzu bata dawo ba.
Tana shiga Goggo ta kalleta cikin tsananin tausayawa.
Jalila fadawa tai jikinta duk da jikarta ta sa kuka, idanun Goggo suka ciciko sai kanta kawai da take shafawa.
Jalila ta dago tana kuka tace ""Goggo Allah nasan da sanin Safeena, ai tasan ban taba tahowa ba."
Goggo tace "Kiyi hakuri"
Jalila tace "Goggo sai yaushe ne zaki daina cewa inyi hakuri? Gaba daya rayuwarmu ni dake a hakuri ta kare, nikam ina takaicin cewa ma Dadyne mahaifi......."
Marin da Goggo ta mata ne yasata yin shiru, kallan Goggo tai kuncinta a rike,Goggo ta kalli hannunta cikin dana sani sannan tace " taya zaki dinga kushe abinda Allah ya hada?"
Jalila tace "kiyi hakuri Goggo bazan kara ba"
Hannunta ta kamo tace " na sani, na sani sosai abinda ke ranki Jalila sai dai bayanda zamuyi da hukuncin Allah, sannan komai zaiyi ko kowa zai zageshi to lalai banda ke, domin shine silar zuwanki duniya."
Tace "Na daina Goggo kiyi hakuri."
Goggo tai murmushi tace " yi maza ki cire kayanki."
Mikewa tai ta shiga dan dakinsu.
Tana cire kaya tai sallah sannan ta mike tace "Goggo bari naje"
Goggo tace abinci fa? Naga da safe ma a tsatsaye kikaci, shiyasa kullum gakinan kamar a hure.
Tace " Goggo in na dawo naci" tace ban yarda ba sai dai ki tafi dashi can kici, ina zaki jira sai wajen magrib kici abinci?
Jalila tai murmushi sannan tace " to in na gama ma rana zam deba inci a namu."
Goggo tace "kin tabbatar?"
Tace eh karki damu Goggo na
Fuska ta canza tace “ wacce irin tambaya ce wannan?”
Jalila xatai magana Uncle Sagir ya shigo, da sauri suka mike suka gaida shi.
Idanunsa akanta ya fara sauka, a hankali wani murmushi ya banyana a fuskarsa.
Sannan ya basu damar zama.
“Mathematics” abinda ya rubuta kenan a blackboard sannan ya ruba “Quadratics Equation”
Sannan ya juyo da hankalinsa kan d’alibai, Jalila ta dago suka hada ido da sauri ta sunkuyar da kanta tana wata da yatsun hannunta, haka ya shiga yi musu examples.
Jefi jefi yana sauke idanunsa akanta haka itama, har ya gama period dinsa sannan ya ce a hada masa assignment din da ya bada.
Nan monitor ta mike ta hada, kallan Jalila yai yace “Habiba inasan ganinki biyoni da books din nan.”
Kallansa tai sannan tai saurin cewa “Yes Sir”
Tare da fitowa ta amshi littatafan.
Yana gaba tana dan binsa a baya sai jitaj yace “ yau saboda in kama wata nazo da wuri sai tai sa’a bata makara ba.”
Tace “wata? Ni?”
Ta fada tana kallansa,bai juyo ba sannan bai daina tafiya ba yace “ da yau na kamata lalai da shikenan na daina amsa ko gaisuwarta.”
Tace “ Na daina zuwa late insha Allah, sannan jiya ma tsautsayine.”
Yace “ a tare zamu gama, kuna gama exams ni ma ina kammala aikina.”
Murmushi tai batace komai ba.
Yace “ me kikeyi tsayawa yi in an tashi daga school kullum?”
Tace “ Kanena nake jira a tashesu sannan a daukosu sai su biyo ta nan mu tafi.”
Yace “Kannenki?”
Ita kanta taji abin ban barakwai sai dai ko ma menene ai kannenta ne, tace “eh”
Juyowa yai yace “ a wani school suke?”
Tace “Crescent International School”
Kallan mamaki ya mata sai dai bai kara cewa komai ba sai juyawa dayai, yana tafiya yana mamaki, kannenta na Crescent ita kuma tana makarantar Government?
Sai data ajiye mai books din sannan ta fito, tana tafe tana mamakin tambayoyin da Uncle Sagir ya mata.
Ana tashi sun fito ita da Zarah, Zarah na ce mata ni dazu me kike nufi? Ban samu munyi magana ba........
Nasir da ta gani a tsaye ne yasa ta dakama Jalila duka a kafada tace “ Jalila kinga!”
Jalila ta juya ta kalli yaran dake tsaye daga gefensu tace “ yayanki ne?”
Yace “My Nasir ne, da alama ya gaji da missing dina ne.”
Jalila ta kalli Nasir din sannan ta kalli Zarah wata dariya ta kirkiro wanda kana gani kasan ta dole ce tace “ Ohh shine Ur Nasir?”
Zarah ta hade rai tace “Meye hakan?”
Jalila ta girgiza kai tace “Kije naga ya kura miki ido kamar zai daukeki.”
Murmushi tai sannan tace “ Kawata kalleni fuskata batai komai ba?”
Kamar zatai kuka ta daga kai tace “Eh”
Zarah ta fara tafiya cikin canza salo, Jalila kallansu kawai take cikin mamaki, wannan ai da alama makaranta ya samu da wuri amma ta tabbatar baiba Zarah shekara biyu bama, dan ma tace a level 3 yake ne amma lalai da tace sa’ansu ne,lalai ansha yarinta shiyasa.
Tab itakam gaskiya bataji zata iya soyaya da sa’anta, ita tafisan saurayi kamar Uncle Sagir, da sauri ta girgiza kai tace “What am I thinking? Ahhhhh lalai banida kai.”
#OneLuv💕
🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *AyusherMohd*
*No 3*
Tana kallansu suna tafe suna rangaji irin na masoya, murmushi tai sannan ta koma gefe ta tsaya.
A hankali duk aka yoye tana tsaye, ganin rana ta fara dishashewa ne yasa ta daga kai ta kalli sama, hadari taga yana haduwa abinka da damina kan kace me gari yayi daki, da sauri ta juya ciki ganin iska mai kura tana tasowa.
Ji tai ta bugi abu, da sauri ta dago ta kalleshi.
Idanunsa na kanta, ta matsa baya da sauri cikin jin kunya, sannan tace "Sorry Sir"
Yace "anya yau sorry din nan zai karbu kuwa agurina? Da alama sai na hukunta mai laifin nan."
Kallansa tai sannan tace " Wlh ban ku........"
Yanda yake kallanta ne yasa ta kasa karasa maganar dake bakinta sannan tai saurin juyawa, dan ji take gabanta na faduwa.
Murmushi yai sannan yace "muje in kaiki gida."
Tace " Naam"
Yace "Baki ji bane ko bakya so ne? Hadari ne a garin in aka fara ruwa kina tunanin yanda zakiyi kije gida? Ko su Kannen naki ne bakyasan ki tafi ki barsu?"
Shiru tai tana dan nazari kafin tace " Nagode da kulawa Uncle Sagir sai dai in na tafi ba tare dasu ba fada za'amin."
Kamar zai sake magana sai kuma taga ya juya ya koma ciki, tana tsaye ya fito da lema ya mika mata bai jira tace komai ba ya hau mota yai gaba.
Da kallo ta bishi yau da mota yazo? Hmm ita kadai tasan cin zarafin da za'ama mahaifiyarta in har ta tafi.
Tana tsaye aka fara yayyafi da sauri ta bude lemarta ta shiga, kan kace me ruwa ya tsuge, ruwa ake mai karfin gaske wanda tana cikin lemar ma amma ba tsira tai ba, komawa gefe tai ta rakube.
Kamar motar zata tsaya sai taga ta yi gaba da gudu, cikin tsananin tsoro ta kalli motar tare da kwalla kara da karfi tace "Safeen ina nan fa......"
A cikin motar kuwa wanda Safeena tacema Malam Auwal da alama ta tafi ganin hadari, wanda akasan ranta ta tabbatar bata tafi ba, tsabar mugunta ce.
Haka ta rakube dan tsoro takeji ta koma cikin makarantar ita kadai, ganin a tsayen ma tsoro ya kamata kawai ta fara tafiya tana tafe tana kuka mai sauti, sai dai kasancewar karar ruwa bai sa tasan da karfi take kukan ba.
Yana zaune a cikin motarsa daga gefen titi wanda shi dama yafisan gurin shiru inda ba mutane, shiyasa mafi akasari zaka sameshi ne a zaune a cikin motarsa ya zuge glass kawai ya kwanta.
Jikin motar ta tsaya da taga ruwan ya dan yi sauki duk jikinta ya jike jagaf, ga lemarma sai lankwashewa takeyi saboda iska.
Juyawa tai ta kalli glass din motar, da yake motar mai tints ce sai ta shiga kallan kanta tana kara wani kukan,sam tunaninta bai kawo mata da wani a cikin motar ba.
Kallanta kawai yakeyi sai sharar kuka take wiwi.
Komawa yai ya maida kansa ya rufe idanunsa kamar mai bacci.
Kara juyowa yai ya kalleta, kuka take sosai, kamar dama neman kukan takeyi, haushi duk ya isheshi kamar a kansa take kukan, kofar mazauninsa ya bude, a tsorace ta kalli motar, kallansa tai a tsorace, sannan ta kalli motar .
Kallan tsoro tamai tace "Hmm hmm."
Hannunsa ya dago ya mata alama da ta matsa daga gun, tace "Ban gane me kace ba."
Alama ya sake mata da hannunsa akan tai gaba, sannan ya maida kofarsa ya rufe, da harara tabi kofar motar sannan tace " wannan kuma wani kwarantancen dan duniyar ne? Maganarce yafi karfin yimin ko kuwa tsabar rashin mutumci ne?"
Harara ta sake yi sannan ta juya, kallan motar ta sakeyi sannan tace "irin motar jiya"
Taja tsaki tace " da alama duk masu hawa irin motar nan basuda mutunci."
Sam ta manta da kukan da takeyi saboda masifa, tana tafe yayafi na digar mata tana yan mitocinta, sai da ta gama gajiya ligif sannan ta isa gida.
Goggo kuwa duk ta kasa zama saboda tsoro ganin yanda ake ruwa ga har yanzu bata dawo ba.
Tana shiga Goggo ta kalleta cikin tsananin tausayawa.
Jalila fadawa tai jikinta duk da jikarta ta sa kuka, idanun Goggo suka ciciko sai kanta kawai da take shafawa.
Jalila ta dago tana kuka tace ""Goggo Allah nasan da sanin Safeena, ai tasan ban taba tahowa ba."
Goggo tace "Kiyi hakuri"
Jalila tace "Goggo sai yaushe ne zaki daina cewa inyi hakuri? Gaba daya rayuwarmu ni dake a hakuri ta kare, nikam ina takaicin cewa ma Dadyne mahaifi......."
Marin da Goggo ta mata ne yasata yin shiru, kallan Goggo tai kuncinta a rike,Goggo ta kalli hannunta cikin dana sani sannan tace " taya zaki dinga kushe abinda Allah ya hada?"
Jalila tace "kiyi hakuri Goggo bazan kara ba"
Hannunta ta kamo tace " na sani, na sani sosai abinda ke ranki Jalila sai dai bayanda zamuyi da hukuncin Allah, sannan komai zaiyi ko kowa zai zageshi to lalai banda ke, domin shine silar zuwanki duniya."
Tace "Na daina Goggo kiyi hakuri."
Goggo tai murmushi tace " yi maza ki cire kayanki."
Mikewa tai ta shiga dan dakinsu.
Tana cire kaya tai sallah sannan ta mike tace "Goggo bari naje"
Goggo tace abinci fa? Naga da safe ma a tsatsaye kikaci, shiyasa kullum gakinan kamar a hure.
Tace " Goggo in na dawo naci" tace ban yarda ba sai dai ki tafi dashi can kici, ina zaki jira sai wajen magrib kici abinci?
Jalila tai murmushi sannan tace " to in na gama ma rana zam deba inci a namu."
Goggo tace "kin tabbatar?"
Tace eh karki damu Goggo na