← Book details Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 52 OF 53

Sashe 52

Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read

  Shiru tai tana tunani, ta kalli kayan data cire wanda tasa a ciki basket din laundry.

  Ganin ba yanda zatai ne yasa tadan bude kofar kadan ta leko kanta.

Shikuma yana jin alamun bude kofarta ya kalli gun.
Suna hada ido ta komar da kanta.

Mikewa yai dan ya fahimceta.

Agoggo ya kalla, yaga azahar tayi ya mike ya tada sallah.

Ita kuma tana komawa ciki ta jingina da kofar toilet din, massage din daya mata dazu ta tuno, da sauri ta girgiza kai.

Sake lekowa tai taga yana sallah, a hankali ta fito tazo jikin wardrobe ta bude ta zura hijab.

  A cikin hijab din tasa bra sannan ta zura skirt ta sa riga sannan ta cire hijab din ta matso jikin madubi ta  shafa mai sannan ta fesa body spray da turare.

  Kallansa tai yana zaune akan sallaya ta lalaba tai waje.
Tana sauka ta hada tea kamar yanda ya sata tasha, sannan ta koma kitchen ta bude fridge ta dauko nama zata sa tafashe.

Bayan ta fita ne yai tunanin yanzufa sai ta tafi sa abinci ko?
Mikewa yai ya sauko kasa, kitchen ya nufa, ya taka ciki ya shiga.
Raban da Hassan ya shiga cikin kitchen shikansa ya manta, ko magana zaiyi sai dai ya tsaya daga falo, ko kofa.

  Juyowa tai jin motsin shigowa, kallansa tai cikin mamaki tace "yaya!"

Me zance? Abinda zuciyarsa ta tambayeshi kenan.
Hade rai yai yace "ruwa zaki bani."
Tace "ruwan sama har ya kare?"
Yace "a'a ba sanyi ne."
Cikin mamaki ta mikomai robar ruwa tana cewa ko na kashe fridge din?

Mikamai ruwan tai yasa hannu zai amsa, kan hannunta hannayensa suka taba, kallansa tai shima ya kalleta.

A hankali ta zare hannunta ta dan juya.
Ya amshi ruwan kafin yace "me kike? Ke da ba lafiya ba?"
Tace "abinci zanyi kaga ba kowa a gidan."

Yace "dan ba kowa sai akace mara lafiya yai abinci?"

Ta juyo tace "ba haka nake nufi ba, kaga sanda zasu dawo ne a gajiye zasu dawo."
Yace "in ance bakya kula da lafiyar ki kice ba haka ba, to Ummy ce tace karkiyi."
Ya juya ya bar kitchen din.

Da kallo ta bishi, tadan yi ajiyar zuciya tace "oh ni, yanzu ma laifi na sakeyi?"

Maida namantai cikin fridge din sannan ta fito.
A falo ta sameshi tace "Yaya!"

Ya kalleta yace " kin warke ko na kaiki asibiti?"

Tace "Allah na warke har mamaki nakeyi."

Ya juya ya hau sama.

Shiru tai tare da binsa da kallo.

*******

Ummy kuwa tana kashe waya ta saki wani murmushi, Sageer ya kalleta yace "Ummy wani abun ne?"
Tace "a'a bakomai, kawai dai abin ne kemin dadi, dan na tabbatar yanzu Hassan ya fara san matarsa."

Sageer ya kalleta wani abu ya ratsomai, ya daure yai murmushi yace "ai Ummy ki daina damuwa na tabbatar Yaya zaiso Jalila yanda bakya zato, tanada halayen da zaija ra'ayinsa."

Ummy ta jinjina kai cikin jin dadi tace "sosai ma, na yarda dakai Sageer."

A tare sukai murmushi Ummy tace "ya kukai da Goggo dazu?"

Sageer yace "ai bakiga kukan datake ba nidai har na taho tana kuka akan itakam da munbarta ta koma kauye ina ita ina wannan gida haka?"

Ummy tai murmushi tace "Sageer in na tuno abinda mutanen nan sukayima Jalila da mahaifiyarta sai naji kamar bai kamata mu kyalesu ba."

Yace "hakane Ummy koni abin na damuwa, bansan haka tai rayuwa ba."
Ummy tace "nikaina, sai dai mu barma Allah komai."

A ransa yace "bansani ba Jalila, bansan haka kikasha wahala a rayuwa ba, i am really sorry......."

*******

Suna saukowa Dady ha kalli Mumy yace "mumyn Yasmeen me kikeyi hakan?"

Rungumeshi tai tace "ba sai ka shiga maganar nan ba, wannan shikadai ne hanyar da zaisa Inna tadinga ganin girmanka."

Dady ya dago ya kalli sama, inna ya gani a tsaye tana kallansu, murmushi ya mata sannan ya kankame Mumy tare da sa kansa a wuyanta.

Inna ta dunkule hannunta sannan ta juya, snake yanzu kake nunamin abinda ke boye a kasan zuciyarka, u really try na yanda ka boye fuskarka a cikin mask ba wanda ya fahimci abinda ke tattare da ita.

Tace sai dai ka makaro dan kana tafin hannuna wlh.

(Nace damuwarki😏)

#OneLuv💕
Chapter 52 · 0% Book details