← Book details Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 4 OF 53

Sashe 4

Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Tana isa ta tadda Safeena a falo tana kallo, wata banzar harara ta maka mata sannan tace " da kuka taho kuka barni sai kuma gashi mai rai da lafiya yayo gida da kansa."
Safeena tace " au da gaske kina can dama? Ni danaga ana zabga ruwa sai naga ina mai hankali zai tsaya a cikin ruwan nan?"
Jalila tace " mai hankali kikace ai ni kuwa ina na ganshi?"
Ta karasa maganar tana harararta, jitai ance " Uban wa ya baki damar cimata mutunci?"
Gabanta ne yai wani irin faduwa, duk gidan ba wanda take tsananin tsoron ya mata fada irin Inna, a tsorace ta kalleta idanunta sun firfito, bakinta ne ya shiga rawa tace "In nn nna......"
Kallanta tai sannan ta kalli Safeena tace " ke kuma Jalila matsayinku daya da zaki dinga zama tana fada miki kalamai irin haka?"
Jalila ta hadiyi wani miyau me daci tace " in na bahaka bane......."
"Dake nake magana?"
Jalila gabanta sai faduwa yakeyi.
Sultan ne ya fito daga kitchen rike da jarkar ruwa na faro yace " Inna ita Safeenar itace da laifi bai kamata ku dinga yanke hukunci ba tare da bincike ba."

Kallansa tai tace " Sultan shiga daki"
Baice komai ba ya wuce ciki, Jalila kuwa kamar wacce aka tsunduma a wani ruwan haka takeji, muryar Dady ne ya ratsa falon wanda maganganu Inna ne suka sa shi fitowa, da sauri yace "Hajiya ki mata afuwa ni zan hukuntata da kaina."
Kallansa tai a wulakance tace " kai har wani hukunci zaka iya? Ka saisaita yarinyarka in ba haka ba daga ita har uwarta zasu bar gidan nan, karka kuskura ka manta gida da dukiyar wanene kake mora daga kai har su."
Mumy ce ta rike hannunta tace " Kiyi hakuri ki bari dan Allah."
Ta fada tare da jan hannun ta zuwa dakinta.
Suna shiga tace "Inna sai yaushene zaki daina disga Abakar cikin yaransa? Karfa ki manta 'ya'yansa sunanan kuma suna jin zafin abin."
Kallanta tai tace " ke meyasa bakida hankaline? Kin nace sai kin aureshi dake da mahaifinki, bakya tunanin wannan cin mutuncin da nakemai shine dalilin da yasa yake nuna miki kulawa haka?"

  Tace " Wlh Inna ke kike ganin haka Abbakar na sona kamar yanda nake sansa, dan Allah ki daina wulakantashi."
Ta karasa maganar cikin lalashi.

A falo kuwa Dady a zuciye ya sa hannu ya fizgo Jalila ya kaita kitchen, cikin fada yace " sai yaushe ne zakiyi hankali kisan darajarsu Safeenan kikeci ke da uwarki?"
Kallansa tai cikin rawar baki tace " Dady itace........"
Cikin tsawa yace " so kike in fasa miki baki? Ko me ta miki bazaki hakura ba? Shashashar banza to wlh ki bala'in shiga hankalinki in har kinaso mahaifiyarki dake ku zauna a gidan nan."
Yana gama magana yai falo, yana shigowa Safeena taje da gudu da rungumeshi.

**************

   Yana shigowa cikin gidan ya tadda mahaifinsa a zaune a falo, karasawa yai ya gaidashi sannan ya fara kokarin mikewa.

Mahaifinsa yace "Hassan!"
Komawa yai ya zauna tare da kallansa, Abba yai ajiyar zuciya sannan yace " Baka manta badai karshen satin nan zamu koma asibiti ko?"
Hassan ya kalleshi yace "Abba please ka hakura
Abba cikin kulawa yace " Ka taba ganin inda uba ya hakura da dansa? Karka damu insha Allah da yardar Allah wannan matsala taka zata warware sannan zaka samu sauki cikin yardar Allah."
Kallan mahaifinsa kawai yake shidai sun kasa fahimtarsa, mikewa yai baice komai ba zaiyi gaba.
Kaninsa ne ya dafashi yace " Yaya kace Ameen mana ko hankalin Abban zai kwanta?"
Ummy ya kalla wacce ke tsaye ita da Ameerah yai shiru sannan a hankali yadan motsa baki yace Ameeen.
Murmushi sukai dukansu m, Sagir ya dafashi yace " Ko kai fa Yaya."
Hannunsa yasa ya ture nashi daga kafadarsa yai wuce, Ummy tabi bayansa da kallo sannan ta kalli Ameera.
Kai Ameera ta daga sannan tai kitchen.
Faten dankali wanda Ummy ta masa ta zubo a plate sannan ta dau spoon ta fito, sama ta hau sannan ta shiga dakinsa.
Yana zaune a kasa kan carpet ta shiga.
Gabansa ta ajiye abincin sannan ta ce "Yaya abinci."
Kallanta yai yace " BAna......"
Tace " Na sani yaya baka jin yunwa dama ko da yaushe zancen kenan, sai dai Yaya ka ci ko dan Ummy ta samu sukuni a ranta."
  Yace "Naji zanci, ke kuma fita."
Ta mike tace " to"
Waje tai sannan ta turomai kofar.

#OneLuv💕

🗯 *JALILAH* 🗯

Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *AyusherMohd*

_Gaisuwa mai yawa tare da fatan alkairi a koda yaushe gareki Aunty na ta kaina.....Aunty Goggo Allah ya kareki ya ja da ranki😍 much luv Sister_

           *No 4*

   Da kyar ya tura abincin sannan ya mike ya shiga bandaki, wanka yai tare da dauro alwala.
Jalabiya ya zura ya tada sallah, ya dade sosai akan sallayar yana mika rokonsa gurin Allah sannan ya kwanta a kasa, a takure ya kwanta , sam baisan sanda bacci yai gaba dashi ba.
Ummy ce ta leko ta ganshi yana bacci, kusa dashi taje ta zauna tana kallansa cikin tsantsar so da kulawa da kuma tausayi, jan numfashi tai sannan ta mike ta dau tiren abincin da yaci tai waje.

  Gab da magrib yana bacci yaji kamar ana shakemai wuya, wani irin mumunan mafarki yakeyi wanda ya shiga sandarewa yana kankake jikinsa, idanunsa a runtse sai wani irin zufa da yake kwaranya daga jikinsa, numfashinsa ne ya shiga hawa da sauka, shure shure ya shiga yi saboda tsananin azabar da yake fuskanta.

  Har zai shiga dakinsa yaji alamar motsin Hassan, da sauri Sagir ya tura kofar, ganin Hassan a kankame yasa yai saurin shiga dakin, tabashi yai yana cewa Hassan! Yaya!
  A firgice ya bude idanunsa tare da jan wani irin numfashi, Sagir ya dagashi zaune yace "in kawo ma ruwa?"

  Hassan ya daga kai, da sauri ya mike ya dauko mai ruwa,  amsa yai ya lafa bakinsa, sai dayasha sosai sannan ya kalli Sagir ya mikamai jarkar.
Sagir ya amsa sannan yace "akwai abinda kake bukata?"
Kai ya girgiza alamar a'a.
Cikin tausayawa Sagir ya kalleshi sannan ya mike yace "Yaya kazo dan Allah ko waje ka fita kaji iskar duniya."
Bai kalleshi ba haka kuma bashi da niyyar amsamai, Sagir ganin haka yasa ya fita tare da ja mai kofar.

  Sagir yabi bayan kofar da kallo sannan yace "Allah ya yaye maka ya baka lafiya."

  Dakinsa Sagir ya shiga kallan kayan da ya cire dazu yai sannan yai murmushi ko a ya ta koma gida? Cikin nuna halin damuwa yace " ba ta dai jike ba ko?"
Kai ya girgiza yace " ya za'ai ta jike ga lemar da ya bata sannan ya tabbatar tace ai zuwa za'ai a daukesu."
Murmushi yai sannan ya dau wayarsa dayazo dayka ya sauka kasa.

  **************

    Jalila ce zaune tanacin abincin dare ita da Goggo, tunanin abinda ya faru dazu takeyi.
Jitai Goggo ta tabata tace " Jalila wani abun ya faru ne dazu?"
Jalila ta kalleta tace "Bakomai kawai dai ni akwai abinda na dade ina san tambayarki ne Goggo."

Goggo ta kalleta tana neman karin bayani, Jalila tace " Bawai da wani abin bafa nake san ji Goggo, kawai dai tambaya ce."
Goggo tace "Ina jinki."
Jalila tace " Ni Goggo baki da kowa ne sai Dady?"
Murmushi tai tace"Ban gane banida kowa ba sai shi? Kin tabaganin wanda bashida kowa a duniya?"
Jalila tace " To ni Goggo na kasa fahimtarki ne sam, na rasa takamaimai ke mukeyi a cikin gidan nan."
Goggo ta tsame hannunta sannan tace " Lalai Jalila, muhallin Mahaifin naki kike fadama haka?"
"Muhalli? Ai kowa yasan gidan Mumy ne ba nashi ba, sannan ni waye ma yasan ni 'yarsa  ce, ko suna a makaranta ni ansa nayi amfani da Auwal wato kakan Dady, dan kawai karma asan ni yar sace."

Goggo tace" ya isa to, ke dai ba ruwanki da wannan, mahaifinki da mahaifinki ne, sannan banaji yana da laifi a harkar nan, laifin na iyayenmu ne."
Jalila tace "Goggo dama tun can baya sanki"
Harararta tai tace"Wai yau me kikesan ji ne haka?"
Tace"ni dan Allah ki fadamin tarihinki Goggo."

Hannunta ta wanke a robar ruwan da Jalila ta kawo ta dan matsa kadan tace " sai randa hankali yazo miki."
Jalila ta dan turo baki tace "ni yau meyasa ake tacemin banda hankali?"
Goggo tace " Ce miki akai mara hankali a cikin gida?"
Tace "Safeena ce."
Goggo tace "Fada kukai kenan?"
Jalila ta hade rai tace " ni ai....."
Goggo tace "sai yaushe ne zaki dinga hakuri Jalila? Na dauka na rokeki akan kai zuciya nesa?"
Jalila ta kalleta tace "Yanzu duk hakurin da nakeyi bakya gani? Wlh a yanda nake ji da wata rana sai na fasama 'yar nan baki, kawai hakuri nake sawa a zuciyata."

Goggo tausayinta ya kamata tace"kiyi hakuri, duk tsanani yana tare da sauki, shiyasa a koda yaushe nake miki fatan miji na gari, wanda ke sanki ina tunanin hakan ne kadai zai kawo salama a zuciyata da taki."
Jalila tace "ni duk wanda zan aura sai dai in zai iya rikemin ke, dan bazan iya aure na barki ba."
Dariya Goggo tai tace "Lalai yarinta na damunki Jalila."
Haka sukai ta hira har suka kwanta.............

  *********

  Washegari.........

  Yau tana gama aiki ta shirya ta fito dan jiransu, dadi takeji yau ta rigasu shiryawa, yanda taga Dady ya fito da sauri ko gaisuwarta bai tsaya amsawa ba tasan lalai da matsala, mota taga ya shiga da sauri, sai ga Mumy ta taho da gudu tare da shiga gefensa itama, nan taga sun fita a guje.
Baki ta tabe tace "ko ina zasu haka oho"

  Su Safeena ne suka fito,Yasmeen na ganinta ta isa gunta da gudu tana nuna mata sabon school bag din da Dadynta ya siyo mata.
Jalila tace "inyee lalai tayi kyau."
Tafada tana kallan wata yagwalgwalaliyar jakar dake bayanta.
Mota suka shiga, Safeena ta kalli Sultan tace "Sultan kamar akwai matsala a company dinsu Dady ko?"
Sultan ya kalleta yace" ina na sani, in so kike kiji me yasa baki tambayeshi ba da zai fita?"
Haushi ne ya kamata tace " Wai kai meyasa mutum bai isa yai maganar mutunci dakai ba?"
Chapter 4 · 0% Book details