← Book details Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 46 OF 53

Sashe 46

Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ummy tace "duk wani abunda kika sani muke sanji, wannan shikadai ne abinda zaisa musan abinda ya dace muyi, kada ki munafurcemu, kada ki munafirci mahaifiyarki."

Jalila ta kalli Goggo.

Turo kofar da akai ne yasa suka kalli kofar, Hassan ne ya shigo.

Kallan Jalila yai wacce itama kallansa takeyi, a hankali wani murmushi ya bayyana a fuskarta wanda yana ganin haka ya dauke kansa daga kallanta sannan ya nufi can gefe ya zauna akan kujera shi kadai.

Goggonta kalleshi, wannan shine na dazu......

********

Inna ce ta kalli Dady tace "take all the blame."

Kallanta yai cikin mamaki yace "ban gane ba?"
Tace "kace kaine kai komai, dama matarka ce da yarka, kaga kome kai dama kaine me hakki akansu, wannan shikadaine hanyar dazamu kwaci company dinmu."

  Dady yace "ni na kasa fahimta, kenan nine na shirya duk abinda ke faruwa?"
Tace "eh ko dama nice na shirya? Ina naga matsayi? Matar data tsufa????

Dady yamata wani kallan tsantsan mamaki........

#OneLuv💕

🗯 *JALILAH* 🗯

Written By : *AYUSHER MUHD*
✔ote me on Wattpad : *Ayusher Mohd*

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)

*44*

  Jalila tai ajiyar zuciya sannan ta kalli Goggo tace "sanda na sameki a bangaren su Dady akwance ba lafiya........................."
Haka ta kwashe komai ta sanar dasu, gaba daya falon yayi tsiy saboda tsananin tausayin abinda kunnuwansu yakeji, Hassan na zaune ya kwantar da kansa a saman kujera, idanuwansa na lumshe kai kafe bai san me ake cewa a falon ba, sai dai gaba daya zuciyarsa a karye take da abinda kunnuwansa keji, wannan wace irin rayuwa yarinyar nan tai? Wani irin rashin imani ne hakan? Hannunsa ya matse guri guda cikin tsananin takaici.

  Jalila ta karashe maganar tana kuka tace Goggo banasan wani abu ya sameki shiyasa na kasa fadamiki, sannan suma sunce min karna sanar dake.....

Goggo tana kallanta idanuwanta na zubar da kwalla ta jawota jikinta ta rungume Jalila ta saki wani kuka mai ban tausayi, Goggo tana hawaye tana shafa bayanta tana cewa "kiyi hakuri Jalila duk nice na ja miki abinda suka miki."

Ummy ma gaba daya hankalinta ya tashi, tausayin su ya kamata.

Sageer kam ba'a magana dan baima san hawaye yana gangaromai ba, sai dayaji ruwa a kuncinsa, ya goge da sauri yana kallanta.

  Ummy ta kalli Abba wanda yai shiru yana nazarin abinda ke faruwa, kenan bayan yaga Jalila yace yanaso su bawa dansa a matsayin matar Hassan shine sukai bincike akan Hassan, da sukaji bashida lafiya shine suka hadashi da ita, to ina asalin yar tasu? Dan ya fahimci akwai wata.

Kallan Jalila yai yace "ya isa haka Jalila, su ne suke tunanin sun cutar dake suna ganin sun yaudare mu, amma ni da matata basu yaidaremu ba ko kadan dan ni dama ke nagani sannan ke kika kwantamin a rai, haka itama ke ta gani sannan ke kika kwanta mata a rai, anci mutuncin mahaifiyarki a matsayinta na wacce ta haifeki ta shayar dake sannan ta reni bai kamata ko menene ba a aura da 'ya bada sanin mahaifiyarta ba."

Ummy cikin zafin rai tace "ai muma sun ci mutuncinmu taya zasu nuna mana sune suka haifeta bayan mahaifiyarta daban, tayana dan rashin imani zasu aurar da yarinya mahaifiyarta na kwance ba lafiya? Sannan suyi amfani da rashin lafiyarta gun sata tayi abinda sukeso?"

Goggo ta share hawayenta tace " duk nice suka raina, nice suka maida abin zuba shara, nice basa ganin mutunci, nagode sosai da kaunar da kuka nuna ma yarinyar nan, ko ba'a fada ba na san akwai kulawa mai karfi datake samu a gidannan fiye da gidan da za'a kirashi da sunan gidan mahaifinta."

  Abba yai ajiyar zuciya yace "yanzu tunda nasan meke faruwa bazan barsu haka ba."

Ummy ta kalleshi da sauri tace "me zakayi?"
Ya mike cikin takaici yace "don't u understand what's happening? Sun daukemu a matsayin joke ne, kenan sun maidamu fools, duk abinda suka tsara shi muke bi."

Ummy ta kalli Hassan wanda kamar ma baisan abinda ake a falon ba, sannan ta kalli Abba tace " ni kuma ina ganin ka kyalesu kawai."

Abba yace " In mun kyalesu kina tunanin zasuyi dana sani?"

Goggo ta kallesu tace "amma dan Allah inada tambaya, me ka musu ne da harsuke tunanin ko za'a mutu sai sun kawo Jalila cikin gidan nan?"

Sageer ya kalli Abba yace "Abba ni kaina ina wannan tunanin."

Abba ya kalli Ummy yace " kasuwanci......."

Ummy tamai alama dayai shiru, yace " yanzu ke Jalila kiyi hakuri, nasan an shiga hakkinki, sannan an shiga hakkin mahaifiyar data haifeki, kuyi hakuri wannan harda laifin mu."

  Goggo da sauri tace "ba laifinku bane, masu laifin daban, zan iya yafe duk wani abu da za'amin ko na wulakanci ko na tozarci amma bazan yafemusu ba akan abinda sukama Jalila, tayaya zasuyi amfani dani wajen ganin sun sata abinda sukeso? Yanzu da ace mugun hannu ta fada fa???? Ta fada cikin raunaniyar murya.

  Hassan ya bude idanunsa ya kalli Jalila wacce ke kuka tana zaune kusa da Goggonta.

  A hankali ya mike kawai yabi ta bayan kujera yai hanyar waje.

  Jalila ta kalleshi, shima kallanta yai sannan ya dauke idanunsa da sauri.

  Ummy ta mike tace "Hassan ya akai?"

Yace "bakomai...."
Kawai yai kofa, kallan Abba tai cikin wani yanayi, hannunta ya yadan dafa alamar ba komai.
Sannan ya kalli Goggo wacce gaba daya ita da Jalila tausayi suke bashi, yace "Sageer kai dasu Jalila ku shiga ciki, ni zanyi magana da mahaifiyar Jalila."

Sageer ya mike ya fita, Jalila ta mike ta fito.

Abba ya kalli Goggo yace " garin yaya kika bari aka maidake kamar baiwa? Ko bakida yan uwa ne?"

  Tace "inadasu sai dai a matsayin babu suke."
Ummy tace "kamar ya?"

Tace "bayan anmin auren dole da Abakar aka umarceni da karna kara tako garin sai dashi tin daga lokacin ban sake zuwa ba, dan banida darajar da zai kaini."

Ummy tace "kamar ya? Baki sake neman mahaifiyarki da yan uwanki ba?"

Tace "ina zan nemisu bayan umarni mahaifina ya bani....."
Abba yace "wani umarni ne hakan?"

Ummy tai saurin cewa "Auranki fa?" Dan ta fahimci rashin ilimin addini ne ya sa ta dauka biyayya takeyi.

Goggo tace "ban sani ba nima dan rabona dashi tun ranar da aka kaini, lokacin Allah yai dabon Jalila."

  A tare sukace "me?"
Goggo tai kasa dakai tana murmushin takaici.

Ummy tace "Goggo muje kici abinci ki kwanta."

Abba ya kalleta cikin mamaki dan akwai tambayoyin da yake san jin amsarsu.

********

Jalila na fitowa ta nufi hanyar sama, Sageer da sauri yace "Jalila!"

Tsayawa tai bata juyo ba tana share kwallarta, Sageer ya matso ya mika mata handkerchief kallansa tai kamar zata karba sai kuma naga ta fasa, kamar bazata amsa ba sai kuma ta amsa  tace "nagode." Kawai tace ta juya ta hau saman.

Tsayawa yai yana kallanta cikin tsananin tausayi, har saida tai kwana sannan ya juya zuwa dakinsa, yana shiga ya zauna a bakin gado yana tunani, haka rayuwarta take? Shiyasa ashe ake barinta a makaranta ita kadai? Shiyasa sukasata a government?

*******
Ummy ta taso tazo kusa da ita, suka fita tare, ina saurayin Jalila? Ta tabbatar Jalila.......... tunowa datai a inda tasan Sageer ne yasa ta kalli Ummy da sauri tace "ya sunan mijin Jalila?"

Ummy tace "Hassan!"

Goggo tace "wanda na gani dazu fa?"
Ummy tace "Sageer? Kaninsa ne."
Goggo tace "kaninsa?"

Ummy ta daga kai alamar eh, Goggo a ranta tace "to ko ba shi bane?"

Dakin Ameera ta kaita sannan tace "kici abinci ki kwanta, dan Allah karkiyi tunanin komai, Jalila yanzu 'yatace bazan kara bari wani abu ya sameta ba, sannan mu zamu san abinyi, ke dai ki kwantar da hankalinki ko dan lalurarki."

Goggo ta riko hannun Ummy tace "Nagode, nagode har bansan iya godiyar daya kamata nai miki ba."

Ummy tai murmushi tace "muma mungode, da kika fahimcemu, yanzu sai kisama auransu albarka."

Tace "insha Allah."

Nan ta shiga ciki.....

Ummy ta bita da kallan tausayi.

Jalila kam kamar zata shiga ciki sai kuma ta fasa, zama tai a falo kawai tana kuka ko kwanwutar bata kunna ba.

  Shima zama yai a kasa ya kwanatar da kansa akan kujerar dakin, wace irin rayuwa yarinyar nan tai? Amma duk da haka akwai laifinsa a ciki, ya tabbatar dabadan shi ba da baza'a mata auran dole haka ba, wadan nan tunani sune suke tayimai zirya a ransa, tarinta yaji hakan yasa ya kalli kofar falon.

  Mikewa naga yayi ya jingina kansa da jikin kofar, sheshekar kukanta yaji wanda yasashi rufe ido cikin tausayawa.

Jin kukan yake har zuciyarsa, a hankali ya bude kofar.

  Dayake makunin fitilar falon a kusa da kofar take kawai sai ya kunna ta.

Haske ne ya baibaye falon, da sauri ta dago.

  Jingina kansa yai da jikin kkatangar falon yana kallanta tare da sa hannunsa na hagu cikin aljihunsa.

  Kallansa itama takeyi, sun dade a haka kafin ta sauke idanunta kasa.

Yace " yau ma hobby din naki ya motsa ne?"

Ta kalleshi da idanunta da suka sha kuka, yace "a rana kuka nawa kikeyi?"

  Baki tadan motsa tanasan magana, yace " in zakiyi kuka kiyi a gurin daba kowa, dan ni ba hobby dina bane sauraransa."

  Ya juya bai rufe kofar ba ya zauna akan kujera, me yasa yace haka? Shi dayaje dan ya lalasheta?

  Mikewa yai yai sallar Isha'i, ganin batada niyyar shigowa yasa yaki mikewa daga kan sallayar, yana jiranta.

  Kofar yake lekawa, yaga ba alama.

  Pillow ya janyo yasa kansa akai yana kallan kofar.

  Abincin su ya kalla, bataci abinci ba, shiru yai yana tunanin shigowarta.

  Yana nan a kwance har karfe 10, baisan sanda bacci yai gaba dashi ba.

Jalila kam bayan ya juya kawai ta kwanta akan kujerar tana yan mitoci, kasan baka damu da hawayena ba me yasa dazu kazo? Nikam Yaya me yasa baya magana mai sanyi? Tadan turo baki ta kwanta tana tunanin rayuwarsu.

  Batasan bacci ya dauketa ba, sai karfe 11 ta farka, batai isha'i ba ya akai bacci ya dauketa?

Da sauri ta sauko daga kan kujera ta nufi dakin, a kwance ta ganshi a kasa, batai mamaki ba dan taga yanayi, kawai ta wuce toilet.
Chapter 46 · 0% Book details