Sashe 2
Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kallansa tai cikin tsananin tausayawa tace “ Hassan ka tausayamin ko dan halin da nake ciki.”
Kallanta yai yace “ Sau nawa zan ce miki ki cireni aranki Ummy? Dazu da safe nagama nazari ina tunanin abu biyu ko dai na bar kasar nan na koma egypt da zama ko kuma na bar gidan nan, ina tunanin wannan shine abinda ya cancanta na muku dake da Abba.”
Kallansa kawai takeyi cikin mamaki tace “ Kana tunanin in kabar kusa damu hankalinmu zai kwamta ne ko me?”
Kafafunsa ya sauko ya saukesu a kasa yace “ To ya kuke so nai? “
Tace “ ka zo muje gun likita ya sanar dakai hanyar da zakabi danyin yaki da matsalarka.”
Yace “ Ummy please ki fita.”
Mikewa tai dan tasan in bata fita bama ba wani abu dazai biyo baya, in har kaji yace mutum ya fita to tabbas karshen maganarsa tazo kenan, daga nan duk wani abu na duniya da zaka fada ko mai zafinsa bazai taba tanka wa ba.
Tana fita ta rufo kofar sannan ta sauka kasa, mai gidanta ta kalla jiki a sanyaye, yana ganin yanda tai yasan ba’a dace ba, kansa ga saukar kan dinning din sannan ya dago ya kalli yaransa biyu dababba mai bin Hassan sai kuma mai binsa mace, duk yaransu ukun sun girma, dan karamar mace wato Ameera a Ss2 take.
Sagir yana ganin yanda sukai duk jiki a sanyaye yai saurin mikewa sannan ya jawo Ummy ya zaunar da ita kan kujera yace “ Ummy kinsan jiya naje gidan Auty Nana?”
Ta kalleshi tace “Da yaushe?”
Yace “ bayan mun tashi a makaranta, Aina tace ai zata zo mana hutu karshen satin nan.””
Ameera da sauri tace “Ya Sagir da gaske?”
Abba yai murmushi yace “Auta da alama kawa ta kusa zuwa.”
Dukansu ne sukai murmushin.
Suna cikin cin abinci ya fito rike da makulin mota, ko kallan inda suke baiyi ba yai waje, sam basu kula da wucewarsa ba dan falan babba ne sannan dining area din na bangaren kitchen.
Mota kawai ya fada yai waje............
*Wattpad Ayushermohd* ( _please vote and Comment_😍)
#Oneluv
[08/10, 19:18] +234 816 365 0557: 🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *AyusherMohd*
*No 2*
Gudu yai ta shararawa a mota sai dayaga har ya fita daga cikin gari sannan yaja motar ya tsaya sannan ya gangara gefen titi ya kashe motar, gani nai ya fito daga mazaunin driver ya koma baya ya kwanta tare da lumshe idanunsa.
Bai dade da fara bacci ba yai wani irin zabura, a tsorace ya farka jikinsa ya fara karkarwa, jiyai numfashinsa na mai wahalar ja, jijiyoyin wuyansa ne suka firfito kamar wanda aka rikema hancinsa da bakinsa, zufa ce ta shiga keto masa da kyar ya jawo numfashi sannan ya mike ya zauna tare da hade kafafunsa, nan da nan idanunwansa suka canza.
Wayarsa ce datai kara tasa ya dawo hankalinsa, kallan wayar yai sunan mahaifinsa ne a jiki, idanunsa ya runtse yana takaicin wannan rayuwar tasa, shi kadai ya hana iyalan gidansu samun farin cikin rayuwa.
Lalai yana tunanin dolene ya bar kasar nan yaje inda ba wanda ya sanshi in ma rayuwar tasa a iya nan ta tsaya to shikam zai iya cewa Alhamdulila.
Bai dau wayar ba har sai da ta katse.
Fitowa yai daga motar ya hau samanta yana kallan bishiyoyi da sararin samaniya.
Ya dade a haka sosai yana tunani kafin ya sauko ya
••••••••••
A bangaren Jalila kuwa tana shiga ta tadda mahaifiyarta a zaune tana hada mafici, Goggo tana ganinta tace Jalila an dawo?
Jalila ta shigo fuska a hade tace “Goggo yunwa.”
Goggo tace “Yi maza ki cire kaya kici abinci kafin a kiraki daga cikin gida, ni kaina a zaune kawai nake anan amma hankalina na kanki.”
Kayanta ta cire ta zura doguwar riga ta mikoma Goggo naira Goma sannan ta jawo kwanan abincin ta fara ci, Goggo tausayinta ne ya kamata dan dama tasan bazata taba kashe ashirin din nan ba, inda sabo ta saba wahala da rike yunwa.
Batai nisa da fara cin abincin ba Safeena ta shigo bako sallama tace “Ke kizo inji Mumy”
Bata kula taba sai cigaba da cin abincinta da tai, Safeena tace “ Malama ba magana nake miki ba?”
Jalila tace “Malama taje koyo sallama.”
Safeena tai kwafa tace “ Mumyn kike fadama haka?”
Jalila ta tsame hannunta dan duk ma abincin ya fita akanta ta mike ta wuce ta gabanta, Safeena ta juya a kule tai hanyar cikin gida.
Jalila ta tura kofar a hankali, Dady ta gani zaune da Yasmin a falo, suna kallo suna shan ice cream, sallamarta ya amsa yana kallanta, motsin Mumy da yaji ne yasa ya dauke idanunsa daga kanta.
Mumy tana gaba Safeena na bayanta, bata kalli inda Jalila take ba sai zama datai kusa da Dady tare da kwantar da kanta akan kafadarda tace “ Abban Yasmeen kafadata duk ciwo take min.”
Kallan ta yai tare da nuna tsantsar kulawa yace “ lafiya? Ko muje asibiti? Garin ya ya? Faduwa kikai?”
Kallan Jalila tai hakan yasa ya fahimci mai take nufi, mikewa naga yayi cikin mamaki naga ya yi ma Jalila alama da hannu, takawa tai zuwa inda yake tana neman bada hakuri, wani wawan mari naga an sakar mata wanda ni kam tsananin mamaki sai da yasa na yarda pen dina, ya dora da cewa “ menene aikinki a gidan nan?”
Idanunta ne suka fara zubar da kwalla dan tabbas taji marin har ranta tace “ duk wani aiki da akeyi a cikin gida.” Ta fada cikin kuka
Yace “ akan me tunda kika dawo baki shigo kin fara aikinki ba har dai da kikasa ta yin aikin wahala?
Da sauri tace “ Kiyi hakuri Mumy.”
Mumy ta mike tare da kallansa tace “” Abban Yasmeen abin ai bai kai da duka ba, in ka mata fada ma ai ya isa.”
Ya kalli Jalila a zafafe yace “ kece kikace kin daukema Mahaifiyarki aiki ko ba kece ba?”
Tace “nice”
Yace “ da haka kike tunanin zaku zauna a gidan da yake nata kuci kusha da kudin ta ba tare da kunyi aikin biya ba?”
Hawayenta ta share tace “ kayi hakuri.”
Mumy ta dan canza fuska tace “ sai yaushe ne zaka daina cewa gidana da kudina? Abu na ba naka bane?”
Yace “ na sani, sai dai agun wannan yarinyar da uwarta dole ne adinga tuna musu.”
Tace ka bari please matarkace dai
Kallan Jalila yai yace “Mata? Matar da bance inasoba aka likamin? Ko kuwa yar da batajin magana?”
Jalila kam hawaye kawai takeyi, Yasmeen ce tasa kuka da sauri suka juya kanta.
Dady yace “Auta menene?”
Ice cream dinta ta nuna wanda ya fadi a kasa, Jalila da sauri ta nufi kitchen ba ta dade ba ta dawo da kayan gyara gun, Nan ta gyara gun tas sannan tace “Yasmeen kin sanma yan kasa?”
Tace” ni kad’an zan san musu”
Tace “ ki bar musu tunda sun shanye wannan nan gaba karki basu kinji?”
Kai ta daga tare da yin murmushi.
Jalila wacce tana gyara gun Mumy da Dady suka shiga ciki ta goge hawayen da suka bata mata fuska sannan ta kalli Safeena wacce ke bakin kofa tana murmushin mugunta.
Bata bi ta kanta ba tai kitchen, Safeena ce ta biyota tace “Mumy tace kiyi fried cus cus da miyar vegetables”
Tace to
Nan ta shiga aiki tana yi hawaye na zubo mata, a duk sanda aka cima Mahaifiyarta mutunci wuni take tana kuka, sai dai abin bakin cikin ba kowa bane mai cima mahaifiyar tata mutunci ba sai Mahaifinta da zuri’ar sa dan kuwa zuri’arsa zatace, a iya sanin rayuwarta bata taba ganin mahaifinta ya shiga bangaren Mahaifiyarta ba balle mu’amala ta aure ta hadasu ba, in ta tuno irin kuncin da mahaifiyarta ta shiga a dalilin rashin so ba shakka sai taji nata ba mai zafi bane, gwara ita mahaifinta ne.
A haka har ta gama girkin, tana girkin tana gyara gidan inda ya baci, sai da ta juye musu nasu sannan ta dauko tasu samirar ta dan zuba kamar yanda aka kiyaste mata sannan ta gyara kitchen din.
Daukar na Mamar Mumy tai ta nufi sama inda take, Sallama tai sannan ta tura kofar bayan an bata izini, a zaune take sanye da glass tana karanta wata takarda, kana shiga dakin wani sanyin dadi da kamshi ne zai ratsaka, inda ake ajiye mata abinci ta ajiye sannan ta tsugunna tace “Inna barka da gida.”
Bata tankata ba, inda sabo ta saba mikewa tai sannan ta nufi hanyar waje.
Muryar inna taji cikin tsantsar isarta tace “ na dauka jiya ma sanar dake in kin dawo yau daga makaranta zaki kwashi wankina ki sauka dashi kasa?
Da sauri ta juyo tace “ yahkuri Inna wlh na manta.”
Bata kara tanka mata ba nan ta nufi inda kayan suke ta hadasu ta fito dasu.
Sauko wa tai tana kallan su Safeena da Sultan rike da littafan karatu da shigar uniform na islamiya zasu tafi.
Abinda take tsananin buri kenan a rayuwarta taga an sata a islamiyya.
Haka ta sauko ta kai wankin Inna gun Auwal dan ya kai mata sannan ta mikama Goggo abincinsu ta dawo dan gyara dakin Safeena da Sultan, tana gamawa ta koma kitchen dan daura abincin dare.
Haka rayuwar Jalila take, daga aiki sai aiki, makarantar boko kadai aka barta sai dare bayan magrib take samun zama da mahaifiyarta.
**************
_Washe gari_
Yau kam tayi sa’a ba’a sata yin breakfast mai wuya ba, ta samu ta biyosu Safeena, a mota dama Yasmeen ce kawai mai magana ta kula Safeena ta kula Jalila dan ita yarinya ba ruwanta.
Shi kuwa Sultan kamar baya cikin motar haka yake, earphone kawai yake sawa a kunnensa ya kwantar da kansa akan kujera har su isa.
Kallanta yai yace “ Sau nawa zan ce miki ki cireni aranki Ummy? Dazu da safe nagama nazari ina tunanin abu biyu ko dai na bar kasar nan na koma egypt da zama ko kuma na bar gidan nan, ina tunanin wannan shine abinda ya cancanta na muku dake da Abba.”
Kallansa kawai takeyi cikin mamaki tace “ Kana tunanin in kabar kusa damu hankalinmu zai kwamta ne ko me?”
Kafafunsa ya sauko ya saukesu a kasa yace “ To ya kuke so nai? “
Tace “ ka zo muje gun likita ya sanar dakai hanyar da zakabi danyin yaki da matsalarka.”
Yace “ Ummy please ki fita.”
Mikewa tai dan tasan in bata fita bama ba wani abu dazai biyo baya, in har kaji yace mutum ya fita to tabbas karshen maganarsa tazo kenan, daga nan duk wani abu na duniya da zaka fada ko mai zafinsa bazai taba tanka wa ba.
Tana fita ta rufo kofar sannan ta sauka kasa, mai gidanta ta kalla jiki a sanyaye, yana ganin yanda tai yasan ba’a dace ba, kansa ga saukar kan dinning din sannan ya dago ya kalli yaransa biyu dababba mai bin Hassan sai kuma mai binsa mace, duk yaransu ukun sun girma, dan karamar mace wato Ameera a Ss2 take.
Sagir yana ganin yanda sukai duk jiki a sanyaye yai saurin mikewa sannan ya jawo Ummy ya zaunar da ita kan kujera yace “ Ummy kinsan jiya naje gidan Auty Nana?”
Ta kalleshi tace “Da yaushe?”
Yace “ bayan mun tashi a makaranta, Aina tace ai zata zo mana hutu karshen satin nan.””
Ameera da sauri tace “Ya Sagir da gaske?”
Abba yai murmushi yace “Auta da alama kawa ta kusa zuwa.”
Dukansu ne sukai murmushin.
Suna cikin cin abinci ya fito rike da makulin mota, ko kallan inda suke baiyi ba yai waje, sam basu kula da wucewarsa ba dan falan babba ne sannan dining area din na bangaren kitchen.
Mota kawai ya fada yai waje............
*Wattpad Ayushermohd* ( _please vote and Comment_😍)
#Oneluv
[08/10, 19:18] +234 816 365 0557: 🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *AyusherMohd*
*No 2*
Gudu yai ta shararawa a mota sai dayaga har ya fita daga cikin gari sannan yaja motar ya tsaya sannan ya gangara gefen titi ya kashe motar, gani nai ya fito daga mazaunin driver ya koma baya ya kwanta tare da lumshe idanunsa.
Bai dade da fara bacci ba yai wani irin zabura, a tsorace ya farka jikinsa ya fara karkarwa, jiyai numfashinsa na mai wahalar ja, jijiyoyin wuyansa ne suka firfito kamar wanda aka rikema hancinsa da bakinsa, zufa ce ta shiga keto masa da kyar ya jawo numfashi sannan ya mike ya zauna tare da hade kafafunsa, nan da nan idanunwansa suka canza.
Wayarsa ce datai kara tasa ya dawo hankalinsa, kallan wayar yai sunan mahaifinsa ne a jiki, idanunsa ya runtse yana takaicin wannan rayuwar tasa, shi kadai ya hana iyalan gidansu samun farin cikin rayuwa.
Lalai yana tunanin dolene ya bar kasar nan yaje inda ba wanda ya sanshi in ma rayuwar tasa a iya nan ta tsaya to shikam zai iya cewa Alhamdulila.
Bai dau wayar ba har sai da ta katse.
Fitowa yai daga motar ya hau samanta yana kallan bishiyoyi da sararin samaniya.
Ya dade a haka sosai yana tunani kafin ya sauko ya
••••••••••
A bangaren Jalila kuwa tana shiga ta tadda mahaifiyarta a zaune tana hada mafici, Goggo tana ganinta tace Jalila an dawo?
Jalila ta shigo fuska a hade tace “Goggo yunwa.”
Goggo tace “Yi maza ki cire kaya kici abinci kafin a kiraki daga cikin gida, ni kaina a zaune kawai nake anan amma hankalina na kanki.”
Kayanta ta cire ta zura doguwar riga ta mikoma Goggo naira Goma sannan ta jawo kwanan abincin ta fara ci, Goggo tausayinta ne ya kamata dan dama tasan bazata taba kashe ashirin din nan ba, inda sabo ta saba wahala da rike yunwa.
Batai nisa da fara cin abincin ba Safeena ta shigo bako sallama tace “Ke kizo inji Mumy”
Bata kula taba sai cigaba da cin abincinta da tai, Safeena tace “ Malama ba magana nake miki ba?”
Jalila tace “Malama taje koyo sallama.”
Safeena tai kwafa tace “ Mumyn kike fadama haka?”
Jalila ta tsame hannunta dan duk ma abincin ya fita akanta ta mike ta wuce ta gabanta, Safeena ta juya a kule tai hanyar cikin gida.
Jalila ta tura kofar a hankali, Dady ta gani zaune da Yasmin a falo, suna kallo suna shan ice cream, sallamarta ya amsa yana kallanta, motsin Mumy da yaji ne yasa ya dauke idanunsa daga kanta.
Mumy tana gaba Safeena na bayanta, bata kalli inda Jalila take ba sai zama datai kusa da Dady tare da kwantar da kanta akan kafadarda tace “ Abban Yasmeen kafadata duk ciwo take min.”
Kallan ta yai tare da nuna tsantsar kulawa yace “ lafiya? Ko muje asibiti? Garin ya ya? Faduwa kikai?”
Kallan Jalila tai hakan yasa ya fahimci mai take nufi, mikewa naga yayi cikin mamaki naga ya yi ma Jalila alama da hannu, takawa tai zuwa inda yake tana neman bada hakuri, wani wawan mari naga an sakar mata wanda ni kam tsananin mamaki sai da yasa na yarda pen dina, ya dora da cewa “ menene aikinki a gidan nan?”
Idanunta ne suka fara zubar da kwalla dan tabbas taji marin har ranta tace “ duk wani aiki da akeyi a cikin gida.” Ta fada cikin kuka
Yace “ akan me tunda kika dawo baki shigo kin fara aikinki ba har dai da kikasa ta yin aikin wahala?
Da sauri tace “ Kiyi hakuri Mumy.”
Mumy ta mike tare da kallansa tace “” Abban Yasmeen abin ai bai kai da duka ba, in ka mata fada ma ai ya isa.”
Ya kalli Jalila a zafafe yace “ kece kikace kin daukema Mahaifiyarki aiki ko ba kece ba?”
Tace “nice”
Yace “ da haka kike tunanin zaku zauna a gidan da yake nata kuci kusha da kudin ta ba tare da kunyi aikin biya ba?”
Hawayenta ta share tace “ kayi hakuri.”
Mumy ta dan canza fuska tace “ sai yaushe ne zaka daina cewa gidana da kudina? Abu na ba naka bane?”
Yace “ na sani, sai dai agun wannan yarinyar da uwarta dole ne adinga tuna musu.”
Tace ka bari please matarkace dai
Kallan Jalila yai yace “Mata? Matar da bance inasoba aka likamin? Ko kuwa yar da batajin magana?”
Jalila kam hawaye kawai takeyi, Yasmeen ce tasa kuka da sauri suka juya kanta.
Dady yace “Auta menene?”
Ice cream dinta ta nuna wanda ya fadi a kasa, Jalila da sauri ta nufi kitchen ba ta dade ba ta dawo da kayan gyara gun, Nan ta gyara gun tas sannan tace “Yasmeen kin sanma yan kasa?”
Tace” ni kad’an zan san musu”
Tace “ ki bar musu tunda sun shanye wannan nan gaba karki basu kinji?”
Kai ta daga tare da yin murmushi.
Jalila wacce tana gyara gun Mumy da Dady suka shiga ciki ta goge hawayen da suka bata mata fuska sannan ta kalli Safeena wacce ke bakin kofa tana murmushin mugunta.
Bata bi ta kanta ba tai kitchen, Safeena ce ta biyota tace “Mumy tace kiyi fried cus cus da miyar vegetables”
Tace to
Nan ta shiga aiki tana yi hawaye na zubo mata, a duk sanda aka cima Mahaifiyarta mutunci wuni take tana kuka, sai dai abin bakin cikin ba kowa bane mai cima mahaifiyar tata mutunci ba sai Mahaifinta da zuri’ar sa dan kuwa zuri’arsa zatace, a iya sanin rayuwarta bata taba ganin mahaifinta ya shiga bangaren Mahaifiyarta ba balle mu’amala ta aure ta hadasu ba, in ta tuno irin kuncin da mahaifiyarta ta shiga a dalilin rashin so ba shakka sai taji nata ba mai zafi bane, gwara ita mahaifinta ne.
A haka har ta gama girkin, tana girkin tana gyara gidan inda ya baci, sai da ta juye musu nasu sannan ta dauko tasu samirar ta dan zuba kamar yanda aka kiyaste mata sannan ta gyara kitchen din.
Daukar na Mamar Mumy tai ta nufi sama inda take, Sallama tai sannan ta tura kofar bayan an bata izini, a zaune take sanye da glass tana karanta wata takarda, kana shiga dakin wani sanyin dadi da kamshi ne zai ratsaka, inda ake ajiye mata abinci ta ajiye sannan ta tsugunna tace “Inna barka da gida.”
Bata tankata ba, inda sabo ta saba mikewa tai sannan ta nufi hanyar waje.
Muryar inna taji cikin tsantsar isarta tace “ na dauka jiya ma sanar dake in kin dawo yau daga makaranta zaki kwashi wankina ki sauka dashi kasa?
Da sauri ta juyo tace “ yahkuri Inna wlh na manta.”
Bata kara tanka mata ba nan ta nufi inda kayan suke ta hadasu ta fito dasu.
Sauko wa tai tana kallan su Safeena da Sultan rike da littafan karatu da shigar uniform na islamiya zasu tafi.
Abinda take tsananin buri kenan a rayuwarta taga an sata a islamiyya.
Haka ta sauko ta kai wankin Inna gun Auwal dan ya kai mata sannan ta mikama Goggo abincinsu ta dawo dan gyara dakin Safeena da Sultan, tana gamawa ta koma kitchen dan daura abincin dare.
Haka rayuwar Jalila take, daga aiki sai aiki, makarantar boko kadai aka barta sai dare bayan magrib take samun zama da mahaifiyarta.
**************
_Washe gari_
Yau kam tayi sa’a ba’a sata yin breakfast mai wuya ba, ta samu ta biyosu Safeena, a mota dama Yasmeen ce kawai mai magana ta kula Safeena ta kula Jalila dan ita yarinya ba ruwanta.
Shi kuwa Sultan kamar baya cikin motar haka yake, earphone kawai yake sawa a kunnensa ya kwantar da kansa akan kujera har su isa.