← Book details Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 45 OF 53

Sashe 45

Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Inna tana zaune tananin mafita Mumy ta banko kofa da sauri, Inna ta kalleta tace "naga sanda hankali zai ratsaki ki daina buga kofa haka, yarki ta kai a mata aure amma haryanzu inkina wani abu kamar karamar yarinya."

Mumy ta zauna da sauri tace "ni Inna ki bar fadanki zuwa anjima yanzu akwai matsala."
Gaban Inna ne ya fadi ta kalleta tace "Abakar ya dawone?"

"Ya dawo sai dai yaran ya dauke Goggo"
Inna tai shiru hankalinta ya tashi, ta kalli Mumy tace "yanzu kenan da alama sunsan komai ko?"

Mumy tace "me zai hana? Shiyasa Inna ni dama na kasa gane dalilinki na......."
Wani kallo data mata ne yasata yin shiru, Inna tace "kinsan menene yake bakantamin rai?" Bata jira amsartaba tace " rashin wayau da auna tunaninki, daga ni har mahaifinki munada saurin tunani da kwakwalwa amma ke ni bansan ina kika dauko ba, da farko kince yaran ubanki zaki aura yaran da ko A bai sani ba lokacin, dole da ganin bamuda wani da bayan ke yasa muka jure, sannan kikasan wannan yaran ya munafirceki ashe har aure gareshi, amma tsabar rashin kwakwalwa kika dage ke sai shi, sannan abin bakin ciki duk yanda nai dake akan kiyi aiki a company din da muka gina nida mahaifinki amma kinki, kin dage sai dai mijinki yai, sannan yanzu kice me?"

Mumy tai kasa dakai sannan tace "Inna wai dan Allah sai yaushe ne zaki amince da Abakar daro bisa dari? Mutumin nan na miki ladabi wanda ko ni bana miki, sannan ya a sona san da ba wanda yakemin irinshi..."

Inna tai tsaki tace "ni tashi ki bani guri nasan mafitar data dace damu dan zamanki anan bakomai yake karamin ba sai bakin ciki."

Mumy ta mike tai waje rai a bace....

Inna tai shiru tana tunani kafin ta dau waya ta kira Abakar.
Yana zaune a falo Mumy na gefensa itada Yasmeen, Sultan na daki yana ganin kiranta gabansa ya fadi ya kalli Mumy yace da alama Inna tagama shawara.

Mumy tace "muje tare."
Yace "karki damu ki zauna bari naje."
Nan ya mike yai sama.........

**********

Inna ta tashi tayi wanka, Ummy ta kawo mata kayanta tace ta saka, dan itakam ta kula kayan dake jikinta da wanda aka dauko a leda san ba magana, itada Jalila ne sukaje BQ dan ganin yanayin gun.

Jalila ta kalli Ummy tace "Ummy kije ciki zan gyara."

Ummy tai murmushi tace "Jalila ko dai ince masu aiki gidannan sundinga kwana ne?"

Jalila tace "saboda me?"
Tace "da alama aikin gidan ya karu, sannan zai yi yawa, tunda akwai bangarensu ina tunani gwara mu tambayesu, in zasu dinga kwana to, in kuma bazasuyi ba kinga sai mu samo wasu."

Jalila tai shiru can tace " Ummy gani, ga Lantana ina tunanin ba wani abu."

Ummy tai murmushi tace "baki fahimceni ba kenan."
Jalila ta mata kallo mai alamar tambaya tace "ban....."

Ummy tai dan dariya tace "so nake kibama Hassan kulawa 80% dan na kula ina hanaki kula dashi."
Jalila da sauri ta juya tana tattare kaya dan kunya, Ummy ta sake dariya tace "ko nayi sankai?"

Jalila tace "a'a kawai ta cigaba da aikinta.

Ummy ta kalleta tana murmushi, Lantana ta kira suka gyara gun, Ummy tace "gobe sai a siyo gado da kayan bukata a sa a ciki, wai gadan ciki ya tsufa, da Jalila zatai magana Ummy ta harareta wanda yasata yin shiru.

Sageer kuwa a daki hankalinsa duk ya tashi tabbas Goggonta ganshi a lokacin dan har gaisheta yayi, to amma tagane tsakaninsu? Malam Sagir ashe da raban zan ganka.

Kalaman Goggo ne suka dawo mai, ajiyar zuciya yai cikin tashin hankali yace " ba zama bane ya dace dani."

Mikewa yai ta budo kofar dakinsa a hankali ha sako kai, yana leke.

Bakowa a falon, komawa yai ciki ya zauna yana tunanin abinyi, can ya daure ya fito a hankali yai falo, Ummy na zaune rike da littafin addu'oi ya shigo.

Ta kalleshi tace "Sageer fitowarka kenan, tun rana sai yamma?"

Yace "Ummy ina matar Yaya?"

Tace "Jalila? Tana BQ suna aiki, ta dage sai na taho, ya akai? Nemanta kake?"

Yai murmushin dole sannan yace "eh, bari naje can."
Ummy tace "to, amma Sagir karka tambayeta maganar mahaifiyarta, da magrib in anyi sallah za'a zauna a falon Abbanka."

Yace "to Ummy sannan yai waje.

Tana kwashe shara ya tsaya a bakin kofar yana kallanta.

Kallansa tai sannan ta matso inda yake jiki a sanyaye.

Kallan dakin yai, ya kalli Kofar Toilet inda Lantana ke wankewa.

Yace "Jalila!"

Yace "Uhmm"
Shiru suka danyi dan they are uncomfortable in suna tare ba kamar da ba.
Can ya daure yace "Goggonki, sanda mukaje asibiti....."

Sai a lokacin itama abin yazo mata, ta kalleshi da sauri tace "Ta ganka ko?"
Yace "kin manta har gaisawa munyi?"

Tai shiru tana kallansa, yace "Jalila, zaki iya mata magana? Dan banasan kowa yasan abinda ya faru a baya."

Jalila ta kalleshi tace "ince me? Ince Goggo yayan Uncle nake aure? Ko ince Goggo karki fadama kowa irin san da nakema Kanin mijina? Ko ince Goggo da naso Uncle ashe kanin mijinane?"

Yace "Jalila ya kikesan juya maganar da na fada ne? Me yasa bakya yima kalamai na kyakyasar fahimta?"

Idanunta ne suka ciciko tace "Uncle ni to ya zanyi? Me zance? Kamar yanda kake tsoron matsala ta afko a dalilinka, matsalar da zata sa hankalin iyayenka su tashi ni kaina a yanzu bana san ace nice silar wargaza farinciki Ummy da Abba, dakai kanka da yayanka, Uncle bansan....."

Kasa karasawa tai saboda kuka dake neman zuwa mata dan muryarta ta fara rawa.

Sageer yai shiru yana kallanta cikin tausayawa yace "Nafahimceki Jalila, na kuma gode da kaunar da kikema Family na, Please ko Goggonta tambayeki kawai kice mata sunane yazo daya, mu barshi kawai a haka."

Ta daga kai, kawai dan batasan itakam me zata kuma cewa ba...

Bayan sun gama aiki tai wanka a toilet din ta maida kayan jikinta ta hau sama.

Yana kwance yana bacci ta shiga a hankali ta dau kaya ta saka, sannan ta matso kusa dashi ta sa hannunta akansa, jin ba zafi yasa tai murmushi.

Da alama yau ma ciwon nasa da sauki, dan bacci yake hankalinsa a kwance.

*********
  Bayan magrib kuwa Ummy ta kalli Jalila bayan sun gama girki tace "Jalila inkin kaima Goggon ki ajiye sannan ki kaita falon Abba zamuyi magana."
Tace to, sannan ta dauki Abincin Goggo, tana shiga dakin ta zauna kusa da Goggo tare da kwanciya a kafadar ta tace "Goggona!"

Goggo ta kalleta tace " kin gama gudun?"

Jalila tace "gudun me?"
Goggo ta tureta daga kafadarta tace "kindauka bansan guduna kike ba? Kar na miki tambayoyi? Shiyasa tunda kika fita kikaki shigowa?"

Jalila ta tuntsire da dariya tace "ni? Wlh ba haka bane aiki mukeyi ne bakiga Lantana ma batanan ba?"

Goggo tace "ba wani."
Jalila fa kara kwanciya a kafadarta tace " Ummy tace inkaiki falon Abba, anan zakiji komai."

Tace "kaini dan ni kaina so nake naji."

  Nan suka fita tare, sai data kusa kaita falon, suna tafe tare sai ga Ummy tace " Jalila barta zamu shiga tare."
Ta matso kusa da kunnenta tace "ki je ki lalabo mijinki."

Jalila ta kalleta, Ummy tai murmushi sannan ta nuna mata sama da kanta.

Jalila ta kalli saman sannan ta nufi matatakalar, anya zai fito kuwa? Gashi bashida lafiya.

Kofar dakin ta tura ta shiga, yana kan sallaya yana karatun kur'ani.

Zama tai a bakin gado tana jiransa, bai dade ba yakai ayar karshe ta cikin suratul maryam, yana neman dauko wata surar ne dan izu daya yake yi a duk tsakanin sallar magrib da isha'i tai saurin cewa "Yaya!"

Tsayawa yai bai fara wata surarba sannan bai juyo ya kalleta ba, tace "Yaya za'ayi maganar."

Ya juyo yace "magana?"
Ta kalleshi tace "maganar nan.... ba Abba yace sai anjima ba?"
Yace "and so?"

Tace "shine za'ayi yanzu ka sauko."

Yace "in me?"
Tace "ka sauko, muje tare."

Yace "kinsan me kike cewa? Nine zan sauko inje inda kowa zai zauna ayi magana?"

Kallansa tai tai raurau da ido, yace "ki tashi kije, ni ba nayi nawa part din ba? Saurab ya rage naki."

  Haryanzu kallansa take da idanun kafin tace "Yaya Please"

Juyawa yai ya bude kur'ani zai dora daga inda ya tsaya.

Da sauri ta sauko ta bayansa ta rike gefen rigarsa ta kafadarsa.

Juyowa yai yace "wai........"

Bata jira me zaice ba tace " yaya dan Allah ka taimaken, ba wai wani abu zakace ba, inka zauna agun ma ya isa."

Yace "in zauna?"

Tsugunawa tai ta gefensa tace "Dan Allah yaya."

Hade rai yai ya juya, tace "kan ne?" Ya mata shiru, tace "yahkuri yaya, na sani ina takura maka, sannan ina takura maka da neman yin depending akanka akan komai na rayuwata, kayi hakuri nasan bana kyautawa."

Ta mike tai waje, a falo ta tsaya tai ajiyar zuciya sannan tace " who do u think u are?"

A hankali ta fara sauka daga matatakar, jiki a sanyaye.

  A falo kuwa Abba da Ummy na zaune daga bangare daya, Goggo na dayan bangaren Jalila ta shigo.

Tana shigowa Sageer ya shigo, tunda ya shigo Goggo ke kallansa, inata san fuskar nan? Abba ne ya katseta da cewa "yaki saukowa?"

Ta daga kai alamar eh.
Jiki a sanyaye ta zauna a kasa kusa da Goggo.

Sageer ya zauna a kasa kusa da Abba.

Falon ya dan yi shiru kafin Abba yai gyaran murya yace "Sannu da zuwa mahaifiyar Jalila, muna baki hakuri akan abinda ya faru wanda mu kanmu bamusan takamaimai abinda ke faruwa ba, sai dai ina neman sanin dalilin dayasa ba wanda yasan da zamanki a gidan, sannan dalilin dayasa aka munafircemu mu dake akan auran nan, Jalila yar muce a yanzu shiyasa nake san sanin menene ke faruwa takamaimai."

Goggo tace "nagode da karamawa, sai dai a yanda nasan mutanen nan ba damuwa sukai damu ba ina mamakin yanda akai suka kawo Jalila cikin gidan karamci irin wannan."

Abba yai murmushi yace "mun gode da karamawa, Jalila inaso ki sanar damu abinda ke faruwa."

Jalila ta kalli Abba, ta kalli Ummy sannan ta kalli Sageer.
Chapter 45 · 0% Book details